< Fitowa 31 >

1 Sai Ubangiji ya ce wa Musa,
Yahweh [also] said to Moses/me, “Note that I have chosen Bezalel, the son of Uri and grandson of Hur, from the tribe of Judah, [for special tasks].
2 “Duba, na zaɓi Bezalel ɗan Uri, ɗan Hur, na kabilar Yahuda,
3 na kuma cika shi da Ruhun Allah, fasaha, azanci, da kuma sani cikin kowace irin sana’a,
I have caused him to be completely controlled/empowered by my Spirit, and I have given him special ability [to make things] and have enabled him to know how to do very skilled work.
4 don yin zāne-zāne na aikin zinariya, azurfa da tagulla,
He can engrave skillful designs in gold, silver, and bronze.
5 don yanka da shirya duwatsu, yin aikin katako, da kuma yin kowane irin aikin sana’ar hannu.
He can cut (jewels/valuable stones) and enclose them [in tiny gold settings/frames]. He can carve things from wood and do other skilled work.
6 Ban da haka, na zaɓi Oholiyab ɗan Ahisamak, na kabilar Dan, don yă taimake shi. Na kuma ba da fasaha ga dukan masu aikin sana’ar hannu, don yin duk abin da na umarce ka.
Note that I have also appointed Oholiab, the son of Ahisamach, from the tribe of Dan, to work with him. I have also given special ability to other men, in order that they can make all the things that I have commanded you [to be made].
7 Tentin Sujada, akwatin Alkawari tare da murfin kafara a bisansa, da dukan kayan aiki na tentin,
That includes the Sacred Tent, the sacred chest and its lid, all the other things that will be inside the Sacred Tent,
8 tebur da kayansa, wurin ajiye fitila na zinariya zalla, da dukan kayansa, bagaden ƙona turare,
the table and all the things that are used with it, the pure gold lampstand and all the things that are used to take care of it, the altar [for burning] incense,
9 bagaden hadaya ta ƙonawa da dukan kayansa, daro tare da mazauninsa,
the altar for offering sacrifices that will be burned and all the things that will be used with it, the washbasin and its base,
10 da kuma saƙaƙƙun riguna, tsarkakan riguna don Haruna firist da rigunan’ya’yansa maza, sa’ad da suke hidima a matsayin firistoci,
all the beautiful sacred clothes for Aaron and his sons to wear when they work as priests,
11 da man shafewa, da turare mai ƙanshi don Wuri Mai Tsarki. Za a yi su kamar yadda na umarce ka.”
the oil for anointing, and the sweet-smelling incense for the Holy Place. [The skilled workers] must make all these things exactly as I have told you to do.”
12 Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa,
Yahweh also said to Moses/me,
13 “Ka faɗa wa Isra’ilawa, ‘Dole ku kiyaye Asabbataina. Wannan zai zama alama tsakanina da ku daga tsara zuwa tsara, saboda ku sani ni ne Ubangiji, wanda ya mai da ku masu tsarki.
“Tell the Israeli people, ‘Obey my instructions regarding the (rest days/Sabbath days). Those days will remind you [and your descendants], throughout all future generations, that I, Yahweh, have (set you apart/chosen you) to be my people.
14 “‘Ku kiyaye Asabbaci, domin yă zama mai tsarki a gare ku. Duk wanda ya ƙazantar da shi, za a kashe shi; duk wanda ya yi wani aiki a ranar, za a ware shi daga mutane.
You must obey [my rules about] the Sabbath days because they are holy/sacred. Those who treat those days in an irreverent way by working on those days must be executed [to show that] I no longer consider them to belong to my people.
15 Kwana shida, za a yi aiki, amma a rana ta bakwai, Asabbaci ne na hutu, mai tsarki ga Ubangiji. Duk wanda ya yi wani aiki a Asabbaci, za a kashe shi.
You may work for six days [each week], but the seventh day [of each week] is a solemn day of rest, dedicated to me, Yahweh. Anyone who does any work on a day of rest is to be executed [because I no longer want them to be able to associate with my people].
16 Isra’ilawa za su kiyaye Asabbaci, suna bikinsa daga tsara zuwa tsara a matsayin madawwamin alkawari.
You Israeli people must respect the rest day, and you [and your descendants] must (celebrate it/keep it holy) throughout all future generations. [It will remind you] of the agreement that I have made with you that will last forever.
17 Zai zama alama tsakanina da Isra’ilawa har abada, gama cikin kwana shida Ubangiji ya yi sama da ƙasa, a rana ta bakwai kuma ya daina aiki, ya kuma huta.’”
It will remind you Israeli people and remind me [of that agreement] because I, Yahweh, created the heavens and the earth in six days, and on the seventh day I stopped doing that work and relaxed.’”
18 Sa’ad da Ubangiji ya gama yin wa Musa magana a kan Dutsen Sinai, sai ya ba shi alluna biyu na Alkawari, allunan duwatsu rubutattu da yatsan Allah.
When Yahweh finished talking with Moses/me on the top of Sinai Mountain, he gave him/me the two stone slabs on which he had engraved his commandments with his own fingers.

< Fitowa 31 >