< Fitowa 30 >
1 “Ka yi bagade da itacen ƙirya don ƙona turare.
And you shall make an altar to burn incense upon: of shittim wood shall you make it.
2 Zai zama murabba’i, tsawon zai zama kamu ɗaya, fāɗi kuma kamu ɗaya, amma tsayin yă zama kamu biyu, ƙahoninsa kuma su zama ɗaya da shi.
A cubit shall be the length thereof, and a cubit the breadth thereof; foursquare shall it be: and two cubits shall be the height thereof: the horns thereof shall be of the same.
3 Ka dalaye bisansa da kuma dukan gefe-gefensa da kuma ƙahoninsa da zinariya zalla, ka kuma yi zubi na zinariya kewaye da shi.
And you shall overlay it with pure gold, the top thereof, and the sides thereof round about, and the horns thereof; and you shall make unto it a crown of gold round about.
4 Ka yi zobai biyu na zinariya domin bagade a ƙarƙashin zubin, biyu a gefe da gefe su fuskanci juna, don su riƙe sandunan da ake amfani da su don ɗaukarsa.
And two golden rings shall you make to it under the crown of it, by the two corners thereof, upon the two sides of it shall you make it; and they shall be for places for the staves to bear it likewise.
5 Ka yi sandunan nan da itacen ƙirya, ka dalaye su da zinariya.
And you shall make the staves of shittim wood, and overlay them with gold.
6 Ka sa bagaden a gaban labulen da yake gaban akwatin alkawari, a gaba murfin kafara wanda yake bisa akwatin alkawari, inda zan sadu da kai.
And you shall put it before the vail that is by the ark of the testimony, before the mercy seat that is over the testimony, where I will meet with you.
7 “Haruna zai ƙone turare a bisa bagaden kowace safiya, sa’ad da yake shirya fitilu.
And Aaron shall burn thereon sweet incense every morning: when he dresses the lamps, he shall burn incense upon it.
8 Dole Haruna yă ƙone turare sa’ad da ya ƙuna fitilu da yamma, ta haka za a riƙa ƙona turare a gaban Ubangiji, daga tsara zuwa tsara.
And when Aaron lights the lamps at even, he shall burn incense upon it, a perpetual incense before the LORD throughout your generations.
9 Ba za a ƙona wani irin turare dabam a bisa wannan bagade ba, ba kuma za a miƙa hadaya ta ƙonawa, ko ta hatsi, ko ta sha a bisansa ba.
All of you shall offer no strange incense thereon, nor burnt sacrifice, nor food offering; neither shall all of you pour drink offering thereon.
10 Sau ɗaya a shekara, Haruna zai yi kafara a bisa ƙahoninsa. Dole a yi wannan kafara ta shekara-shekara da jinin kafara ta hadaya don zunubi daga tsara zuwa tsara. Gama bagaden mafi tsarki ne ga Ubangiji.”
And Aaron shall make an atonement upon the horns of it once in a year with the blood of the sin offering of atonements: once in the year shall he make atonement upon it throughout your generations: it is most holy unto the LORD.
11 Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa,
And the LORD spoke unto Moses, saying,
12 “Sa’ad da za ku ƙidaya Isra’ilawa, dole kowanne yă biya domin yă fanshe kansa ga Ubangiji a lokacin da aka ƙidaya shi. Ta haka babu wata annobar da za tă buge su sa’ad da kuke ƙidaya su.
When you take the sum of the children of Israel after their number, then shall they give every man a ransom for his soul unto the LORD, when you number them; that there be no plague among them, when you number them.
13 Kowannen da ya ƙetare zuwa wurin waɗanda aka riga aka ƙidaya, dole yă ba da rabin shekel, bisa ga ma’aunin shekel na tsattsarkan wuri, wanda nauyinsa garwa ashirin ne. Wannan rabin shekel hadaya ce ga Ubangiji.
This they shall give, every one that passes among them that are numbered, half a shekel after the shekel of the sanctuary: (a shekel is twenty gerahs: ) an half shekel shall be the offering of the LORD.
14 Duk waɗanda suka ƙetare, waɗanda shekarunsu ya kai ashirin ko fiye, za su ba da hadaya ga Ubangiji.
Every one that passes among them that are numbered, from twenty years old and above, shall give an offering unto the LORD.
15 Masu arziki ba za su bayar fiye da rabin shekel ba, talakawa kuma ba za su bayar ƙasa da haka ba, sa’ad da za ku yi hadaya ga Ubangiji don kafara rayukanku.
The rich shall not give more, and the poor shall not give less than half a shekel, when they give an offering unto the LORD, to make an atonement for your souls.
16 Ku karɓi kuɗin kafara daga hannun Isra’ilawa, ku yi amfani da shi domin hidimar Tentin Sujada. Zai zama abin tunawa ga Isra’ilawa a gaban Ubangiji, don su yi kafarar rayukansu.”
And you shall take the atonement money of the children of Israel, and shall appoint it for the service of the tabernacle of the congregation; that it may be a memorial unto the children of Israel before the LORD, to make an atonement for your souls.
17 Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa,
And the LORD spoke unto Moses, saying,
18 “Ka yi daro na tagulla, ka yi masa ƙafafun da za a ajiye shi da tagulla don wanki. Ka ajiye shi tsakanin Tentin Sujada da bagade, ka zuba ruwa a ciki.
You shall also make a vessel that holds water of brass, and his foot also of brass, to wash likewise: and you shall put it between the tabernacle of the congregation and the altar, and you shall put water therein.
19 Haruna da’ya’yansa maza za su wanke hannuwansu da ƙafafunsu da ruwan da yake cikinsa.
For Aaron and his sons shall wash their hands and their feet thereat:
20 Duk lokacin da suka shiga Tentin Sujada, za su yi wanka, don kada su mutu. Duk lokacin da suka yi kusa da bagade don hidima ta miƙa hadayar da aka yi wa Ubangiji da wuta,
When they go into the tabernacle of the congregation, they shall wash with water, that they die not; or when they come near to the altar to minister, to burn offering made by fire unto the LORD:
21 za su wanke hannuwansu da ƙafafunsu, don kada su mutu. Wannan za tă zama dawwammamiyar farilla domin Haruna da zuriyarsa daga tsara zuwa tsara.”
So they shall wash their hands and their feet, that they die not: and it shall be a statute for ever to them, even to him and to his seed throughout their generations.
22 Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa,
Moreover the LORD spoke unto Moses, saying,
23 “Ka ɗauki waɗannan kayan yaji masu kyau, shekel 500 na ruwan mur, rabin turaren sinnamon mai daɗin ƙanshi shekel 250, shekel 250 na turaren wuta mai ƙanshi,
Take you also unto you principal spices, of pure myrrh five hundred shekels, and of sweet cinnamon half so much, even two hundred and fifty shekels, and of sweet calamus two hundred and fifty shekels,
24 shekel 500 na kashiya, duk bisa ga ma’aunin shekel na tsattsarkan wuri, da moɗa na man zaitun.
And of cassia five hundred shekels, after the shekel of the sanctuary, and of oil olive an hin:
25 Da waɗannan za ka yi man shafewa mai tsarki, yadda mai yin turare yake yi. Zai zama man shafewa mai tsarki.
And you shall make it an oil of holy ointment, an ointment compound after the are of the apothecary: it shall be an holy anointing oil.
26 Sa’an nan ka yi amfani da shi don shafa wa Tentin Sujada, da akwatin alkawari,
And you shall anoint the tabernacle of the congregation therewith, and the ark of the testimony,
27 da tebur da kuma dukan kayansa, da wurin ajiye fitila da dukan kayansa, da bagaden ƙona turare,
And the table and all his vessels, and the candlestick and his vessels, and the altar of incense,
28 bagaden hadaya ta ƙonawa da dukan kayansa, da daro da mazauninsa.
And the altar of burnt offering with all his vessels, and the vessel that holds water and his foot.
29 Za ka tsarkake su don su zama mafi tsarki, kuma duk abin da ya taɓa su, zai zama mai tsarki.
And you shall sanctify them, that they may be most holy: whatsoever touches them shall be holy.
30 “Ka shafe Haruna da’ya’yansa maza, ka kuma tsarkake su don su yi mini hidima a matsayin firistoci.
And you shall anoint Aaron and his sons, and consecrate them, that they may minister unto me in the priest's office.
31 Ka faɗa wa Isra’ilawa, ‘Wannan mai, zai zama mai tsarki ne a gare ni don shafewa, daga tsara zuwa tsara.
And you shall speak unto the children of Israel, saying, This shall be an holy anointing oil unto me throughout your generations.
32 Kada a zuba a jikunan mutane, kada kuma a yi wani mai irinsa. Wannan mai, mai tsarki ne, za ku kuma ɗauke shi a matsayi mai tsarki.
Upon man's flesh shall it not be poured, neither shall all of you make any other like it, after the composition of it: it is holy, and it shall be holy unto you.
33 Duk wanda ya yi irin wannan mai, duk wanda kuma ya shafa shi a kan wani wanda yake ba firist ba, za a ware shi daga mutanensa.’”
Whosoever compounds any like it, or whosoever puts any of it upon a stranger, shall even be cut off from his people.
34 Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka ɗauki kayan yaji mai ƙanshi, resin na gum, da onika, da galbanum, da kuma zallan lubban, duk nauyinsu yă zama daidai.
And the LORD said unto Moses, Take unto you sweet spices, stacte, and onycha, and galbanum; these sweet spices with pure frankincense: of each shall there be a like weight:
35 Ka yi turare mai ƙanshi yadda mai yin turare yake yi. A sa masa gishiri, yă zama tsabtatacce, tsarkakakke.
And you shall make it a perfume, a confection after the are of the apothecary, tempered together, pure and holy:
36 Ka ɗiba kaɗan daga ciki, ka niƙa, ka ajiye a gaban akwatin alkawari a cikin Tentin Sujada, inda zan sadu da kai. Zai zama mafi tsarki a gare ku.
And you shall beat some of it very small, and put of it before the testimony in the tabernacle of the congregation, where I will meet with you: it shall be unto you most holy.
37 Kada ku yi wani turare irinsa wa kanku; ku ɗauke shi a matsayi mai tsarki ga Ubangiji.
And as for the perfume which you shall make, all of you shall not make to yourselves according to the composition thereof: it shall be unto you holy for the LORD.
38 Duk wanda ya yi irinsa don jin daɗin ƙanshinsa, dole a ware shi daga mutanensa.”
Whosoever shall make like unto that, to smell thereto, shall even be cut off from his people.