< Fitowa 3 >
1 Ana nan wata rana Musa yana kiwon tumakin Yetro surukinsa, firist na Midiyan, sai ya bi da tumaki zuwa gefe mai nisa a cikin hamada, har ya zo Horeb, dutsen Allah.
Now Moses fed the sheep of Jethro his father in law, the priest of Madian: and he drove the flock to the inner parts of the desert, and came to the mountain of God, Horeb.
2 A can mala’ikan Ubangiji ya bayyana a gare shi cikin harshen wuta, a ƙaramin itace. Musa ya lura cewa ko da yake wuta na ci ƙaramin itacen, amma bai ƙone ba.
And the Lord appeared to him in a flame of fire out of the midst of a bush: and he saw that the bush was on fire and was not burnt.
3 Sai Musa ya ce, “Wannan abin mamaki ne, don me wannan itace bai ƙone ba? Bari in matso kusa in gani.”
And Moses said: I will go and see this great sight, why the bush is not burnt.
4 Da Ubangiji ya ga Musa ya matso don yă duba, sai Allah ya yi kira daga cikin ƙaramin itacen ya ce, “Musa! Musa!” Sai Musa ya amsa ya ce, “Ga ni.”
And when the Lord saw that he went forward to see, he called to him out of the midst of the bush, and said: Moses, Moses. And he answered: Here I am.
5 Allah ya ce, “Kada ka zo kusa, tuɓe takalmanka, gama inda kake tsaye, wuri ne mai tsarki.”
And he said: Come not nigh hither, put off the shoes from thy feet: for the place whereon thou standest is holy ground.
6 Sai Allah ya ce, “Ni ne Allah na kakanninka, Allah na Ibrahim, Allah na Ishaku da kuma Allah na Yaƙub.” Da jin wannan, sai Musa ya ɓoye fuskarsa, domin ya ji tsoro yă dubi Allah.
And he said: I am the God of thy father, the God of Abraham, the God of Isaac, and the God of Jacob. Moses hid his face: for he durst not look at God.
7 Ubangiji ya ce, “Tabbatacce na ga azabar mutanena a Masar. Na ji su suna kuka saboda matsin da shugabannin gandunsu suke musu, na kuma damu da wahalarsu.
And the Lord said to him: I have seen the affliction of my people in Egypt, and I have heard their cry because of the rigour of them that are over the works:
8 Saboda haka na sauko domin in cece su daga hannun Masarawa, in kuma fitar da su daga ƙasar Masar, in kai su ƙasa mai kyau mai fāɗi, ƙasa mai zub da madara da zuma, inda Kan’aniyawa, Hittiyawa, Amoriyawa, Ferizziyawa, Hiwiyawa da Yebusiyawa suke.
And knowing their sorrow, I am come down to deliver them out of the hands of the Egyptians, and to bring them out of that land into a good and spacious land, into a land that floweth with milk and honey, to the places of the Chanaanite, and Hethite, and Amorrhite, and Pherezite, and Hevite, and Jebusite.
9 Yanzu kukan Isra’ilawa ya kai gare ni, na kuma ga yadda Masarawa suke wulaƙanta su
For the cry of the children of Israel is come unto me: and I have seen their affliction, wherewith they are oppressed by the Egyptians.
10 To, fa, sai ka tafi. Ina aikan ka wurin Fir’auna don ka fitar da mutanena Isra’ilawa daga Masar.”
But come, and I will send thee to Pharao, that thou mayst bring forth my people, the children of Israel out of Egypt.
11 Amma Musa ya ce wa Allah, “Wane ni in tafi wurin Fir’auna, in kuma fitar da Isra’ilawa daga Masar?”
And Moses said to God: Who am I that I should go to Pharao, and should bring forth the children of Israel out of Egypt?
12 Sai Allah ya ce, “Zan kasance da tare kai. Wannan kuwa za tă zama alama a gare ka cewa Ni na aike ka. Bayan ka fitar da mutanen daga Masar, za ku yi sujada ga Allah a kan dutsen nan.”
And he said to him: I will be with thee: and this thou shalt have for a sign, that I have sent thee: When thou shalt have brought my people out of Egypt, thou shalt offer sacrifice to God upon this mountain.
13 Musa ya ce wa Allah, “A ce ma na tafi wurin Isra’ilawa na ce musu, ‘Allah na kakanninku ya aiko ni wurinku,’ in suka tambaye ni, ‘Mene ne sunansa?’ Me zan ce?”
Moses said to God: Lo, I shall go to the children of Israel, and say to them: The God of your fathers hath sent me to you. If they should say to me: What is his name? what shall I say to them?
14 Allah ya ce wa Musa, “NI NE wanda NINE. Abin da za ka faɗa wa Isra’ilawa ke nan cewa, ‘NI NE, ya aiko ni wurinku.’”
God said to Moses: I AM WHO AM. He said: Thus shalt thou say to the children of Israel: HE WHO IS, hath sent me to you.
15 Allah ya kuma ce wa Musa, “Ka faɗa wa Isra’ilawa, ‘Ubangiji, Allah na kakanninka, Allah na Ibrahim, Allah na Ishaku da kuma Allah na Yaƙub, ya aiko ni wurinku.’ Wannan shi ne sunana har abada, sunan da za a tuna da ni daga tsara zuwa tsara ke nan.
And God said again to Moses: Thus shalt thou say to the children of Israel: The Lord God of your fathers, the God of Abraham, the God of Isaac, and the God of Jacob, hath sent me to you: This is my name for ever, and this is my memorial unto all generations.
16 “Tafi ka tattara dattawan Isra’ila, ka ce musu, ‘Ubangiji, Allah na kakanninku, Allah na Ibrahim, Ishaku da Yaƙub, ya bayyana a gare ni ya ce, Na lura da ku, na kuma ga abubuwan da ake yi muku a Masar.
Go, gather together the ancients of Israel, and thou shalt say to them: The Lord God of your fathers, the God of Abraham, the God of Isaac, and the God of Jacob, hath appeared to me, saying: Visiting I have visited you: and I have seen all that hath befallen you in Egypt.
17 Na kuma yi alkawari, zan fitar da ku daga azabarku a Masar zuwa ƙasar Kan’aniyawa, Hittiyawa, Amoriyawa, Ferizziyawa, Hiwiyawa da Yebusiyawa, ƙasa mai zub da madara da zuma.’
And I have said the word to bring you forth out of the affliction of Egypt, into the land of the Chanaanite, the Hethite, and the Amorrhite, and Pherezite, and Hevite, and Jebusite, to a land that floweth with milk and honey.
18 “Dattawan Isra’ila za su saurare ka. Sa’an nan da kai da dattawan Isra’ila, za ku tafi wurin sarkin Masar, ku ce masa, ‘Ubangiji, Allah na Ibraniyawa, ya sadu da mu. Bari mu yi tafiyar kwana uku zuwa cikin hamada domin mu yi hadaya wa Ubangiji Allahnmu.’
And they shall hear thy voice: and thou shalt go in, thou and the ancients of Israel, to the king of Egypt, and thou shalt say to him: The Lord God of the Hebrews hath called us: we will go three days’ journey into the wilderness, to sacrifice unto the Lord our God.
19 Amma na san cewa sarkin Masar ba zai yarda ku tafi ba, sai hannu mai ƙarfi ya tilasta shi.
But I know that the king of Egypt will not let you go, but by a mighty hand.
20 Saboda haka zan miƙa hannuna in bugi Masarawa da duk al’ajaban da zan aikata a cikinsu. Bayan haka zai bar ku, ku tafi.
For I will stretch forth my hand and will strike Egypt with all my wonders which I will do in the midst of them: after these he will let you go.
21 “Zan kuma sa mutanen su sami tagomashi daga wurin Masarawa, saboda sa’ad da za ku fita, ba za ku fita hannu wofi ba.
And I will give favour to this people, in the sight of the Egyptians: and when you go forth, you shall not depart empty:
22 Kowace mace ta tambayi maƙwabciyarta, da kuma duk wata macen da take cikin gidanta, kayayyakin azurfa da na zinariya da kuma na riguna, waɗanda za ku sa wa’ya’yanku maza da mata. Ta haka nan za ku washe Masarawa.”
But every woman shall ask of her neighbour, and of her that is in her house, vessels of silver and of gold, and raiment: and you shall put them on your sons and daughters, and shall spoil Egypt.