< Fitowa 3 >

1 Ana nan wata rana Musa yana kiwon tumakin Yetro surukinsa, firist na Midiyan, sai ya bi da tumaki zuwa gefe mai nisa a cikin hamada, har ya zo Horeb, dutsen Allah.
Mosi ni Midian vaihma, a masei Jethro e tu hoi hmaenaw a khoum navah, thingyeiyawn e kanîloumlah a ceikhai teh, Horeb tie Cathut e mon koe a pha.
2 A can mala’ikan Ubangiji ya bayyana a gare shi cikin harshen wuta, a ƙaramin itace. Musa ya lura cewa ko da yake wuta na ci ƙaramin itacen, amma bai ƙone ba.
Hatnavah, BAWIPA e kalvantami teh buruk dawk hoi ka tâcawt e hmaito lahoi a kamnue. Mosi ni a khet navah, hmai a to ei, buruk teh a kak hoeh e hah a hmu navah,
3 Sai Musa ya ce, “Wannan abin mamaki ne, don me wannan itace bai ƙone ba? Bari in matso kusa in gani.”
Bangkongmaw buruk kang laipalah ao. Hete kângairu e hno heh ka cei vaiteh ka khet han telah ati.
4 Da Ubangiji ya ga Musa ya matso don yă duba, sai Allah ya yi kira daga cikin ƙaramin itacen ya ce, “Musa! Musa!” Sai Musa ya amsa ya ce, “Ga ni.”
Mosi ni a khet e BAWIPA ni a hmu navah, Mosi, Mosi telah buruk thung hoiyah a kaw. Mosi ni hai ka o telah atipouh.
5 Allah ya ce, “Kada ka zo kusa, tuɓe takalmanka, gama inda kake tsaye, wuri ne mai tsarki.”
Cathut ni hai hnai hanh. Na khokkhawm hah rading haw. Na kangduenae hmuen teh kathounge talai doeh.
6 Sai Allah ya ce, “Ni ne Allah na kakanninka, Allah na Ibrahim, Allah na Ishaku da kuma Allah na Yaƙub.” Da jin wannan, sai Musa ya ɓoye fuskarsa, domin ya ji tsoro yă dubi Allah.
Kai teh nange na pa e Cathut, Abraham e Cathut, Isak e Cathut, Jakop e Cathut, doeh telah atipouh. Mosi ni Cathut teh a khet ngam hoeh dawkvah a minhmai a ramuk.
7 Ubangiji ya ce, “Tabbatacce na ga azabar mutanena a Masar. Na ji su suna kuka saboda matsin da shugabannin gandunsu suke musu, na kuma damu da wahalarsu.
BAWIPA ni hai Izip ram kaawm e ka taminaw e a khang e rektapnae hah kai ni khei ka hmu toe. Ahnimouh thaw ka tawksak e bawinaw kecu dawk ahnimae hramnae lawk ka thai teh, reithai khangnae hai ka panue.
8 Saboda haka na sauko domin in cece su daga hannun Masarawa, in kuma fitar da su daga ƙasar Masar, in kai su ƙasa mai kyau mai fāɗi, ƙasa mai zub da madara da zuma, inda Kan’aniyawa, Hittiyawa, Amoriyawa, Ferizziyawa, Hiwiyawa da Yebusiyawa suke.
Ahnimouh teh Izip ram, Izip taminaw e kut dawk hoi ratang vaiteh, Kanaannaw, Hitnaw, Amornaw, Periznaw, Hivnaw hoi Jebusitnaw onae ram, sanutui hoi khoitui a lawngnae ram dawk hrawi hanlah kai ka kum.
9 Yanzu kukan Isra’ilawa ya kai gare ni, na kuma ga yadda Masarawa suke wulaƙanta su
Atu haiyah, Isarelnaw khuika lawk kai koe a pha teh, Izipnaw ni ahnimouh rektapnae hai ka hmu toe.
10 To, fa, sai ka tafi. Ina aikan ka wurin Fir’auna don ka fitar da mutanena Isra’ilawa daga Masar.”
Hatdawkvah, atu cet leih. Nang teh ka tami, Isarelnaw hah Izip ram hoi hrawi tâcokhai hanlah, nang teh Faro siangpahrang koe kai ni na patoun han telah atipouh.
11 Amma Musa ya ce wa Allah, “Wane ni in tafi wurin Fir’auna, in kuma fitar da Isra’ilawa daga Masar?”
Mosi nihai, kai teh bang patet e tami lah maw ka o teh, Faro siangpahrang koe ka cei vaiteh, Isarelnaw hah Izip ram hoi hrawi tâcokhai han telah Cathut koe atipouh navah,
12 Sai Allah ya ce, “Zan kasance da tare kai. Wannan kuwa za tă zama alama a gare ka cewa Ni na aike ka. Bayan ka fitar da mutanen daga Masar, za ku yi sujada ga Allah a kan dutsen nan.”
Cathut ni atangcalah kai teh nang koe lah ka o han. Kai ni nang na patounnae mitnoutnae teh, nang ni hote taminaw hah Izip ram hoi hrawi tâcokhai hnukkhu, hete mon dawk Cathut na bawk han telah atipouh.
13 Musa ya ce wa Allah, “A ce ma na tafi wurin Isra’ilawa na ce musu, ‘Allah na kakanninku ya aiko ni wurinku,’ in suka tambaye ni, ‘Mene ne sunansa?’ Me zan ce?”
Mosi nihai, kai ni Isarelnaw onae hmuen koe ka pha teh, nangmae mintoenaw e Cathut ni kai teh nangmouh koe na patoun toe telah kai ni ka dei pawiteh, ahnimouh ni hote Cathut e min teh apimaw telah kai bout na pacei awh navah, bangtelamaw bout ka dei pouh han telah Cathut koe a pacei.
14 Allah ya ce wa Musa, “NI NE wanda NINE. Abin da za ka faɗa wa Isra’ilawa ke nan cewa, ‘NI NE, ya aiko ni wurinku.’”
Cathut ni hai KAI teh KAI doeh. KAI ka tet e ni kai teh nangmouh na onae hmuen koe na patoun toe telah Isarelnaw koe bout dei pouh telah Mosi koe atipouh.
15 Allah ya kuma ce wa Musa, “Ka faɗa wa Isra’ilawa, ‘Ubangiji, Allah na kakanninka, Allah na Ibrahim, Allah na Ishaku da kuma Allah na Yaƙub, ya aiko ni wurinku.’ Wannan shi ne sunana har abada, sunan da za a tuna da ni daga tsara zuwa tsara ke nan.
Cathut ni Mosi koe bout a dei pouh e teh, nangmae mintoenaw e Cathut, Abraham e Cathut, Isak e Cathut, Jakop e Cathut lah kaawm e BAWIPA ni kai teh nangmouh koe na patoun toe, telah Isarelnaw koe na dei pouh han. Hote min teh a yungyoe e ka min lah ao teh catounnaw ni pahnim hoeh nahanelah ao.
16 “Tafi ka tattara dattawan Isra’ila, ka ce musu, ‘Ubangiji, Allah na kakanninku, Allah na Ibrahim, Ishaku da Yaƙub, ya bayyana a gare ni ya ce, Na lura da ku, na kuma ga abubuwan da ake yi muku a Masar.
Cet nateh Isarel kacuenaw hah pâkhueng nateh, nangmae mintoenaw e Cathut, Abraham e Cathut, Isak e Cathut, Jakop e Cathut lah kaawm e BAWIPA ni kai koe a kamnue teh, nangmouh na khet awh navah, Izip ram vah nangmouh lathueng bangmaw a sak awh tie kamcengcalah ka hmu awh toe.
17 Na kuma yi alkawari, zan fitar da ku daga azabarku a Masar zuwa ƙasar Kan’aniyawa, Hittiyawa, Amoriyawa, Ferizziyawa, Hiwiyawa da Yebusiyawa, ƙasa mai zub da madara da zuma.’
Izip ram vah na khang a e rucatnae dawk hoi nangmouh na ratang vaiteh, Kanaannaw, Hit naw, Amor naw, Periznaw, Hiv naw hoi Jebusitnaw ram, sanutui hoi khoitui a lawngnae ram dawk hrawi kâenkhai hanlah kai ni lawk ka kam telah ahnimouh koe dei pouh.
18 “Dattawan Isra’ila za su saurare ka. Sa’an nan da kai da dattawan Isra’ila, za ku tafi wurin sarkin Masar, ku ce masa, ‘Ubangiji, Allah na Ibraniyawa, ya sadu da mu. Bari mu yi tafiyar kwana uku zuwa cikin hamada domin mu yi hadaya wa Ubangiji Allahnmu.’
Ahnimouh ni nange lawk a ngâi awh vaiteh, nang ni Isarel kacuenaw hoi Izip siangpahrang koe na kâen vaiteh, Hebrunaw e BAWIPA Cathut teh kaimouh ni kâhmo awh toe. Ramke dawk hnin thum touh lam cei koe kamamae BAWIPA Cathut thuengnae sak thai hanelah, kâ na poe haw, telah na ti pouh han.
19 Amma na san cewa sarkin Masar ba zai yarda ku tafi ba, sai hannu mai ƙarfi ya tilasta shi.
Izip siangpahrang ni a thaonae kut laipalah teh, cei nahane kâ na poe awh mahoeh tie ka panue.
20 Saboda haka zan miƙa hannuna in bugi Masarawa da duk al’ajaban da zan aikata a cikinsu. Bayan haka zai bar ku, ku tafi.
Kai ni hai kut ka daw vaiteh, Izip ram dawk ka sak hane kaie kângairunae hoi hote ram teh runae ka poe han. Hathnukkhu, Izip siangpahrang ni nangmouh teh na tâco sak awh han.
21 “Zan kuma sa mutanen su sami tagomashi daga wurin Masarawa, saboda sa’ad da za ku fita, ba za ku fita hannu wofi ba.
Hote miphun teh Izipnaw koe minhmai kahawi a hmu sak vaiteh, nangmouh ni na tâco awh navah, kuthrawng hoi na tâcawt awh mahoeh.
22 Kowace mace ta tambayi maƙwabciyarta, da kuma duk wata macen da take cikin gidanta, kayayyakin azurfa da na zinariya da kuma na riguna, waɗanda za ku sa wa’ya’yanku maza da mata. Ta haka nan za ku washe Masarawa.”
Bangkongtetpawiteh, napui pueng ni imri, amamae im dawk kaawm e koe sui ngun hoi khohnanaw a hei awh vaiteh, nangmae na canaw hah a pathoup awh vaiteh, Izipnaw e hnopai hah na lawp awh han telah Mosi koe a dei pouh.

< Fitowa 3 >