< Fitowa 29 >

1 “Ga abin da za ka yi don ka keɓe su, don su yi mini hidima a matsayin firistoci. Ka ɗauki ɗan bijimi da raguna biyu marasa lahani.
And this is the thing that thou shalt do unto them to hallow them, to become priests unto me: Take one young bullock, and two rams without blemish,
2 Daga garin alkama mai laushi marar yisti kuwa, ka yi burodi, da wainan da aka kwaɓa da mai, da ƙosai waɗanda an barbaɗa mai a kai.
And unleavened bread, and unleavened cakes, mingled with oil, and unleavened wafers, anointed with oil; of fine wheaten flour shalt thou make them.
3 Ka sa waɗannan a cikin kwando. Sa’an nan ka miƙa su tare da ɗan bijimin da ragunan nan biyu.
And thou shalt put them into one basket, and bring them near in the basket, with the bullock and the two rams.
4 Bayan haka sai ka kawo Haruna da’ya’yansa a ƙofar Tentin Sujada ka yi musu wanka.
And Aaron and his sons shalt thou bring near unto the door of the tabernacle of the congregation, and shalt wash them with water.
5 Ka ɗauki rigar ka sa wa Haruna, ka sa masa doguwar rigar, da rigar efod, da efod kanta, da ƙyallen maƙalawa a ƙirji. Ka ɗaura masa efod da ɗamarar da aka yi mata ado.
And thou shalt take the garments, and clothe Aaron with the coat, and the robe of the ephod, and the ephod, and the breastplate, and gird him with the girdle of the ephod:
6 Ka naɗa masa rawani a kai, ka kuma sa kambi mai tsarki a bisa rawanin.
And thou shalt put the mitre upon his head, and thou shalt fasten the holy crown upon the mitre.
7 Ka ɗauki man shafewa ka shafe shi, ta wurin zuba man a kansa.
Then shalt thou take the anointing oil, and pour it upon his head, and anoint him.
8 Ka kawo’ya’yansa, ka sa musu taguwoyi,
And his sons shalt thou bring near, and clothe them with coats.
9 ka kuma sa musu huluna a kansu. Sa’an nan ka ɗaura wa Haruna da’ya’yansa abin ɗamara. Su kuwa da zuriyarsu, aikin firist kuwa zai zama nasu ta wurin dawwammamiyar farilla. “Ta haka za ka keɓe Haruna da’ya’yansa maza.
And thou shalt gird them with the girdles, Aaron and his sons, and bind the bonnets on them; and the priest's office shall be theirs for a perpetual statute: and thus shalt thou consecrate Aaron and his sons.
10 “Ka kuma kawo bijimin a gaban Tentin Sujada, sai Haruna da’ya’yansa su ɗora hannuwansu a kansa.
And thou shalt cause the bullock to be brought before the tabernacle of the congregation: and Aaron and his sons shall lay their hands upon the head of the bullock.
11 Ka yanka shi a gaban Ubangiji a ƙofar Tentin Sujada.
And thou shalt kill the bullock before the Lord, by the door of the tabernacle of the congregation.
12 Ka ɗibi jinin bijimin ka zuba a kan ƙahoni na bagade da yatsanka, sauran jinin kuwa ka zuba a gindin bagaden.
And thou shalt take of the blood of the bullock, and put it upon the horns of the altar with thy finger, and all the remaining blood shalt thou pour out beside the bottom of the altar.
13 Sa’an nan ka ɗauki dukan kitsen da ya rufe kayan ciki, da kitsen da yake manne da hanta, da ƙoda biyu da kuma kintsen da yake a kansu, ka ƙone su a kan bagade.
And thou shalt take all the fat that covereth the inwards, and the midriff above the liver, and the two kidneys, and the fat that is upon them, and burn them upon the altar.
14 Amma ka ƙone naman bijimin, da fatarsa, da kayan cikin, a bayan sansani. Hadaya ce ta zunubi.
But the flesh of the bullock, and his skin, and his dung, shalt thou burn with fire, without the camp: it is a sin-offering.
15 “Ka ɗauki ɗaya daga cikin ragunan, Haruna kuwa da’ya’yan maza za su ɗora hannuwansa a kansa.
And the one ram shalt thou take; and Aaron and his sons shall lay their hands upon the head of the ram.
16 Ka yanka ragon, ka ɗibi jinin, ka yayyafa shi kewaye da gefen bagaden.
And thou shalt slay the ram, and thou shalt take his blood, and sprinkle it upon the altar round about.
17 Ka yayyanka rago gunduwa-gunduwa, ka wanke kayan cikin, da ƙafafun, da kan, ka haɗa su da gunduwoyin.
And the ram shalt thou cut in pieces, and wash his inwards, and his legs, and put them with his pieces, and with his head.
18 Sa’an nan ka ƙone ragon ɗungum a kan bagade. Hadaya ta ƙonawa ce ga Ubangiji, mai daɗin ƙanshi, wato, hadaya ce da aka ƙone da wuta ga Ubangiji.
And thou shalt burn the whole ram upon the altar, it is a burnt-offering unto the Lord; it is a sweet savor, an offering made by fire unto the Lord.
19 “Ka ɗauki ɗayan ragon, sai Haruna da’ya’yansa maza su ɗora hannuwansu a kansa.
And thou shalt take the other ram; and Aaron and his sons shall lay their hands upon the head of the ram.
20 Ka yanka ragon, ka ɗibi jinin, ka shafa a bisa leɓen kunnen Haruna na dama, da bisa leɓen kunnuwan’ya’yansa maza na dama, da kan manyan yatsotsin hannuwansu na dama, da kuma a kan manyan yatsotsin ƙafafunsu na dama. Sauran jinin kuwa, sai ka yayyafa shi kewaye da gefen bagaden.
Then shalt thou kill the ram, and take of his blood, and put it upon the tip of Aaron's right ear, and upon the tip of the right ear of his sons, and upon the thumb of their right hand, and upon the great toe of their right foot, and sprinkle the blood upon the altar round about.
21 Ka ɗibi jinin da yake a kan bagade, da man shafewa, ka yafa a kan Haruna da rigunansa, da kuma a kan’ya’yansa maza da rigunansu. Sa’an nan shi da’ya’yansa maza da rigunansu za su tsarkake.
And thou shalt take of the blood that is upon the altar, and of the anointing oil, and sprinkle them upon Aaron, and upon his garments, and upon his sons, and upon the garments of his sons with him: and he shall be hallowed, together with his garments, and his sons, and the garments of his sons with him.
22 “Ka ɗebi kitse daga wannan rago, ka yanke wutsiyarsa mai kitse, ka kuma ɗebi kitsen da ya rufe kayan ciki, da kitsen da yake bisa hanta, da ƙoda biyu da kitsen da yake kansu, da cinyar dama. (Gama rago ne don naɗi.)
And thou shalt take from the ram the fat and the rump, and the fat that covereth the inwards, and the midriff above the liver, and the two kidneys, and the fat that is upon them, and the right shoulder; for it is a ram of consecration;
23 Daga kwandon burodi marar yisti, wanda yake gaban Ubangiji, ka ɗauki dunƙule ɗaya, da waina da aka yi da mai, da kuma ƙosai.
And one loaf of bread, and one cake of the oiled bread, and one wafer, out of the basket of the unleavened bread that is before the Lord.
24 Ka sa dukan waɗannan a hannun Haruna da’ya’yansa maza, su kaɗa su a gaban Ubangiji a matsayin hadaya ta kaɗawa.
And thou shalt put all this upon the hands of Aaron, and upon the hands of his sons; and thou shalt make with them a waving before the Lord.
25 Sa’an nan ka karɓe su daga hannuwansu, ka ƙone su a kan bagade tare da hadaya ta ƙonawa, domin ƙanshi mai daɗi ga Ubangiji, wato, hadaya ce da aka ƙone da wuta ga Ubangiji.
And thou shalt then take them from their hands, and burn them upon the altar upon the burnt-offering; for a sweet savor before the Lord, it is an offering made by fire unto the Lord.
26 Bayan haka, ka ɗauki ƙirjin ragon domin naɗin Haruna, ka kaɗa shi a gaban Ubangiji kamar hadaya ta kaɗawa. Wannan ƙirji zai zama rabonka.
And thou shalt take the breast of the ram of the consecration that belongeth to Aaron, and make therewith a waving before the Lord; and it shall belong to thee as thy portion.
27 “Ka tsarkake ƙirji na hadaya ta kaɗawa, da cinya ta hadaya ta ɗagawa, waɗanda za a kaɗa a kuma ɗaga na ragon naɗin, wanda yake na Haruna da kuma na’ya’yansa maza.
And thou shalt sanctify the breast which hath been waved, and the shoulder which hath been lifted up, which was waved, and which was heaved up, of the ram of the consecration, of that which belongeth to Aaron, and of that which belongeth to his sons:
28 Wannan zai zama rabon Haruna da’ya’yansa maza daga Isra’ilawa. Gama wannan hadaya ta ɗagawa ce daga cikin hadayu na salama da Isra’ilawa za su miƙa wa Ubangiji.
That they shall belong to Aaron and to his sons, as a statute forever, from the children of Israel; for it is a heave-offering; and a heave-offering it shall remain from the children of Israel, from the sacrifices of their peace-offerings, as their heave-offering unto the Lord.
29 “Keɓaɓɓun tufafin nan na Haruna za su zama na zuriyarsa bayan mutuwarsa. Da tufafin nan ne za a zuba musu mai, a keɓe su.
And the holy garments belonging to Aaron shall be for his sons after him, to anoint them therein, and to consecrate them therein.
30 Ɗan da ya gāje shi a matsayin firist, shi ne zai sa su har kwana bakwai, lokacin da ya shiga Tentin Sujada, don yă yi aiki a Wuri Mai Tsarki.
Seven days shall that one of his sons put them on who is to be priest in his place, who is to go into the tabernacle of the congregation to minister in the sanctuary.
31 “Ka ɗauki ragon naɗi, ka dafa naman a tsattsarkan wuri.
And the ram of the consecration shalt thou take, and seethe his flesh in a holy place.
32 A ƙofar Tentin Sujada, Haruna da’ya’yansa maza za su ci wannan rago da burodin da yake cikin kwandon.
And Aaron with his sons shall eat the flesh of the ram, and the bread that is in the basket, by the door of the tabernacle of the congregation.
33 Za su ci abubuwan nan da aka yi kafara da su a lokacin tsarkakewarsu da keɓewarsu. Ba wanda zai ci, sai su kaɗai, gama abubuwan nan tsarkaka ne.
And they shall eat those things wherewith the atonement was made, to consecrate them and to sanctify them; but a stranger shall not eat thereof, because they are holy.
34 In naman ragon naɗi ko wani burodin ya ragu har safiya, a ƙone shi, kada a ci gama tsarkake ne.
And if aught of the flesh of the consecration sacrifice, or of the bread, remain unto the morning, then shalt thou burn the remainder with fire; it shall not be eaten, because it is holy.
35 “Ka yi wa Haruna da’ya’yansa maza duk abin da na umarce ka, ka ɗauki kwana bakwai don naɗinsu.
And thou shalt do unto Aaron, and to his sons thus, all as I have commanded thee; seven days shalt thou consecrate them.
36 Ka miƙa bijimi ɗaya kowace rana domin hadaya don zunubi ta yin kafara. Ka tsarkake bagade ta wuri yin kafara dominsa, ka shafe shi da mai don ka tsarkake shi.
And a bullock shalt thou offer every day for a sin-offering as an atonement: and thou shalt cleanse the altar, in as much as thou makest an atonement upon it; and thou shalt anoint it, to sanctify it.
37 Kwana bakwai za ka yi kafara saboda bagaden, ka kuma tsarkake shi. Sa’an nan bagaden zai zama mafi tsarki, kuma duk abin da ya taɓa bagaden zai tsarkaka.
Seven days shalt thou make an atonement upon the altar and sanctify it; and the altar shall be most holy; whatsoever toucheth the altar shall be holy.
38 “Ga abin da za ka miƙa a bisa bagaden kowace rana.’Yan raguna biyu masu shekara ɗaya-ɗaya.
And this is what thou shalt offer upon the altar: Two sheep of the first year for every day, continually.
39 Ka miƙa ɗaya da safe, ɗaya kuma da yamma.
The one sheep shalt thou offer in the morning; and the other sheep shalt thou offer toward evening.
40 Haɗe da ɗan rago na farkon, ka miƙa mudun gari mai laushi wanda an gauraye da kwalaba ɗaya na tataccen mai zaitun, da kwalaba ɗaya na ruwan inabi don hadaya ta sha.
And a tenth part of fine flour mingled with the fourth part of a hin of beaten oil, and the fourth part of a hin of wine for a drink-offering, shall be for the one sheep.
41 Ka miƙa ɗaya ragon da yamma, tare da hadaya ta gari da hadaya ta sha kamar aka yi ta safe, mai daɗin ƙanshi, wato, hadaya ce da aka ƙone da wuta ga Ubangiji.
And the other sheep shalt thou offer toward evening; according to the meat-offering of the morning, and according to its drink-offering shalt thou do unto it, for a sweet savor, an offering made by fire unto the Lord.
42 “Wannan za tă zama hadaya ta ƙonawar da za a dinga yi kowace rana, daga tsara zuwa tsara. Za a yi ta miƙa hadayar a ƙofar Tentin Sujada a gaban Ubangiji. A can zan sadu da kai, in yi magana da kai;
A continual burnt-offering throughout your generations [shall this be] at the door of the tabernacle of the congregation before the Lord; where I will meet with you, to speak unto thee there.
43 a can kuma zan sadu da Isra’ilawa, in kuma tsarkake wurin da ɗaukakata.
And I will meet there with the children of Israel, and it shall be sanctified by my glory.
44 “Ta haka zan tsarkake Tentin Sujada da bagaden, in kuma tsarkake Haruna da’ya’yansa maza su yi mini hidima a matsayin firistoci.
And I will sanctify the tabernacle of the congregation, and the altar: and both Aaron and his sons will I sanctify, that they may he priests unto me.
45 Sa’an nan zan zauna a cikin Isra’ilawa, in kuma zama Allahnsu.
And I will dwell among the children of Israel, and I will be to them for a God.
46 Za su san cewa ni ne Ubangiji Allahnsu, wanda ya fitar da su daga Masar saboda in zauna a cikinsu. Ni ne Ubangiji Allahnsu.
And they shall know that I am the Eternal, their God, who brought them forth out of the land of Egypt, that I might dwell among them: I am the Lord their God.

< Fitowa 29 >