< Fitowa 24 >

1 Ana nan sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Ku hauro zuwa wurina, kai da Haruna, Nadab da Abihu, da kuma dattawa saba’in a cikin Isra’ila. Za ku yi sujada da ɗan nisa,
و به موسی گفت: «نزد خداوند بالابیا، تو و هارون و ناداب و ابیهو و هفتادنفر از مشایخ اسرائیل و از دور سجده کنید.۱
2 sai Musa kaɗai zai kusaci Ubangiji. Amma sauran kada su zo kusa, kada kuma jama’a su hau tare da shi.”
وموسی تنها نزدیک خداوند بیاید و ایشان نزدیک نیایند و قوم همراه او بالا نیایند.»۲
3 Sa’ad da Musa ya tafi ya faɗa wa mutanen duk kalmomin Ubangiji da dokokinsa, sai suka amsa da murya ɗaya suna cewa, “Duk abin da Ubangiji ya faɗa, za mu yi.”
پس موسی آمده، همه سخنان خداوند و همه این احکام را به قوم باز‌گفت و تمامی قوم به یک زبان در جواب گفتند: «همه سخنانی که خداوند گفته است، بجاخواهیم آورد.»۳
4 Sai Musa ya rubuta duk abin da Ubangiji ya faɗa. Ya tashi kashegari da sassafe ya gina bagade kusa da dutsen, ya aza al’amudai goma sha biyu bisa ga kabilu goma sha biyu na Isra’ila.
و موسی تمامی سخنان خداوند را نوشت و بامدادان برخاسته، مذبحی درپای کوه و دوازده ستون، موافق دوازده سبطاسرائیل بنا نهاد.۴
5 Sai ya aiki samarin Isra’ilawa, suka miƙa hadaya ta ƙonawa, suka kuma miƙa ƙananan bijimai don hadaya ta salama ga Ubangiji.
و بعضی از جوانان بنی‌اسرائیل را فرستاد و قربانی های سوختنی گذرانیدند وقربانی های سلامتی از گاوان برای خداوند ذبح کردند.۵
6 Musa ya ɗauki rabin jinin ya zuba a cikin kwanoni, rabin kuma ya yayyafa a kan bagaden.
و موسی نصف خون را گرفته، در لگنهاریخت و نصف خون را بر مذبح پاشید،۶
7 Sa’an nan ya ɗauki Littafin Alkawari ya karanta wa mutane. Suka amsa suka ce, “Za mu yi duk abin da Ubangiji ya faɗa; za mu yi biyayya.”
و کتاب عهد را گرفته، به سمع قوم خواند. پس گفتند: «هرآنچه خداوند گفته است، خواهیم کرد و گوش خواهیم گرفت.»۷
8 Musa ya kuma ɗauki jinin, ya yayyafa a kan mutanen ya ce, “Wannan shi ne jinin alkawarin da Ubangiji ya yi da ku, bisa ga dukan waɗannan kalmomi.”
و موسی خون را گرفت و بر قوم پاشیده، گفت: «اینک خون آن عهدی که خداوند بر جمیع این سخنان با شما بسته است.»۸
9 Musa da Haruna, Nadab da Abihu, da dattawa saba’in, Allah na Isra’ila suka haura
و موسی با هارون و ناداب و ابیهو و هفتاد نفراز مشایخ اسرائیل بالا رفت.۹
10 suka kuma ga Allah na Isra’ila. A ƙarƙashin ƙafafunsa akwai wani abu wanda aka yi da saffaya, mai haske kuma kamar sararin sama kansa.
و خدای اسرائیل را دیدند، و زیر پایهایش مثل صنعتی از یاقوت کبود شفاف و مانند ذات آسمان در صفا.۱۰
11 Amma Allah bai yi wa shugabannin Isra’ila wani abu ba; suka ga Allah, suka ci suka kuma sha.
و برسروران بنی‌اسرائیل دست خود را نگذارد، پس خدا را دیدند و خوردند و آشامیدند.۱۱
12 Ubangiji ya ce wa Musa, “Hauro wurina a kan dutse, ka tsaya a nan, zan ba ka allunan dutsen, da doka da umarnan da na rubuta don koyonsu.”
وخداوند به موسی گفت: «نزد من به کوه بالا بیا، وآنجا باش تا لوحهای سنگی و تورات و احکامی را که نوشته‌ام تا ایشان را تعلیم نمایی، به تو دهم.»۱۲
13 Sa’an nan Musa ya fita tare da Yoshuwa mataimakinsa, ya kuwa hau kan dutsen Allah.
پس موسی با خادم خود یوشع برخاست، وموسی به کوه خدا بالا آمد.۱۳
14 Ya ce wa dattawan, “Ku jira mu a nan, sai mun dawo wurinku. Haruna da Hur suna tare da ku, in wani yana da wata damuwa, sai yă je wurinsu.”
و به مشایخ گفت: «برای ما در اینجا توقف کنید، تا نزد شمابرگردیم، همانا هارون و حور با شما می‌باشند. پس هر‌که امری دارد، نزد ایشان برود.»۱۴
15 Da Musa ya hau dutsen, sai girgije ya rufe dutsen,
و چون موسی به فراز کوه برآمد، ابر کوه را فرو گرفت.۱۵
16 sai ɗaukakar Ubangiji ta sauka a kan Dutsen Sinai, kwana shida girgije ya rufe dutsen, a rana ta bakwai, sai Ubangiji ya kira Musa daga cikin girgijen.
و جلال خداوند بر کوه سینا قرار گرفت، وشش روز ابر آن را پوشانید، و روز هفتمین، موسی را از میان ابر ندا درداد.۱۶
17 Ga Isra’ilawa dai, ɗaukakar Ubangiji ta yi kamar wuta mai ci a kan dutse.
و منظر جلال خداوند، مثل آتش سوزنده در نظر بنی‌اسرائیل برقله کوه بود.۱۷
18 Sa’an nan Musa ya shiga girgijen ya hau kan dutsen. Ya zauna a kan dutsen yini arba’in da dare arba’in.
و موسی به میان ابر داخل شده، به فراز کوه برآمد، و موسی چهل روز و چهل شب در کوه ماند.۱۸

< Fitowa 24 >