< Fitowa 24 >
1 Ana nan sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Ku hauro zuwa wurina, kai da Haruna, Nadab da Abihu, da kuma dattawa saba’in a cikin Isra’ila. Za ku yi sujada da ɗan nisa,
Dieu dit à Moïse: « Monte vers Yahweh, toi et Aaron, Nadab et Abiu, et soixante-dix des anciens d’Israël, et prosternez-vous de loin.
2 sai Musa kaɗai zai kusaci Ubangiji. Amma sauran kada su zo kusa, kada kuma jama’a su hau tare da shi.”
Moïse s’approchera seul de Yahweh; les autres ne s’approcheront pas, et le peuple ne montera pas avec lui. »
3 Sa’ad da Musa ya tafi ya faɗa wa mutanen duk kalmomin Ubangiji da dokokinsa, sai suka amsa da murya ɗaya suna cewa, “Duk abin da Ubangiji ya faɗa, za mu yi.”
Moïse vint rapporter au peuple toutes les paroles de Yahweh et toutes les lois; et le peuple entier répondit d’une seule voix: « Toutes les paroles qu’a dites Yahweh, nous les accomplirons. »
4 Sai Musa ya rubuta duk abin da Ubangiji ya faɗa. Ya tashi kashegari da sassafe ya gina bagade kusa da dutsen, ya aza al’amudai goma sha biyu bisa ga kabilu goma sha biyu na Isra’ila.
Moïse écrivit toutes les paroles de Yahweh. Puis, s’étant levé de bon matin, il bâtit un autel au pied de la montagne, et dressa douze stèles pour les douze tribus d’Israël.
5 Sai ya aiki samarin Isra’ilawa, suka miƙa hadaya ta ƙonawa, suka kuma miƙa ƙananan bijimai don hadaya ta salama ga Ubangiji.
Il envoya des jeunes gens, enfants d’Israël, et ils offrirent à Yahweh des holocaustes et immolèrent des taureaux en sacrifices d’actions de grâces.
6 Musa ya ɗauki rabin jinin ya zuba a cikin kwanoni, rabin kuma ya yayyafa a kan bagaden.
Moïse prit la moitié du sang, qu’il mit dans des bassins, et il répandit l’autre moitié sur l’autel.
7 Sa’an nan ya ɗauki Littafin Alkawari ya karanta wa mutane. Suka amsa suka ce, “Za mu yi duk abin da Ubangiji ya faɗa; za mu yi biyayya.”
Ayant pris le livre de l’alliance, il le lut en présence du peuple, qui répondit: « Tout ce qu’a dit Yahweh, nous le ferons et nous y obéirons. »
8 Musa ya kuma ɗauki jinin, ya yayyafa a kan mutanen ya ce, “Wannan shi ne jinin alkawarin da Ubangiji ya yi da ku, bisa ga dukan waɗannan kalmomi.”
Moïse prit le sang et en aspergea le peuple, en disant: « Voici le sang de l’alliance que Yahweh a conclue avec vous sur toutes ces paroles. »
9 Musa da Haruna, Nadab da Abihu, da dattawa saba’in, Allah na Isra’ila suka haura
Moïse monta avec Aaron, Nadab et Abiu et soixante-dix des anciens d’Israël;
10 suka kuma ga Allah na Isra’ila. A ƙarƙashin ƙafafunsa akwai wani abu wanda aka yi da saffaya, mai haske kuma kamar sararin sama kansa.
et ils virent le Dieu d’Israël: sous ses pieds était comme un ouvrage de brillants saphirs, pur comme le ciel même.
11 Amma Allah bai yi wa shugabannin Isra’ila wani abu ba; suka ga Allah, suka ci suka kuma sha.
Et il n’étendit pas sa main sur les élus des enfants d’Israël: ils virent Dieu, et ils mangèrent et burent.
12 Ubangiji ya ce wa Musa, “Hauro wurina a kan dutse, ka tsaya a nan, zan ba ka allunan dutsen, da doka da umarnan da na rubuta don koyonsu.”
Yahweh dit à Moïse: « Monte vers moi sur la montagne, et restes-y; je te donnerai les tables de pierre, la loi et les préceptes que j’ai écrits pour leur instruction. »
13 Sa’an nan Musa ya fita tare da Yoshuwa mataimakinsa, ya kuwa hau kan dutsen Allah.
Moïse se leva, avec Josué, son serviteur, et Moïse monta vers la montagne de Dieu.
14 Ya ce wa dattawan, “Ku jira mu a nan, sai mun dawo wurinku. Haruna da Hur suna tare da ku, in wani yana da wata damuwa, sai yă je wurinsu.”
Il dit aux anciens: Attendez-nous ici, jusqu’à ce que nous revenions auprès de vous. Voici Aaron et Hur seront avec vous; si quelqu’un a un différend, qu’il s’adresse à eux. »
15 Da Musa ya hau dutsen, sai girgije ya rufe dutsen,
Moïse monta vers la montagne, et la nuée couvrit la montagne;
16 sai ɗaukakar Ubangiji ta sauka a kan Dutsen Sinai, kwana shida girgije ya rufe dutsen, a rana ta bakwai, sai Ubangiji ya kira Musa daga cikin girgijen.
la gloire de Yahweh reposa sur la montagne de Sinaï, et la nuée la couvrit pendant six jours. Le septième jour, Yahweh appela Moïse du milieu de la nuée.
17 Ga Isra’ilawa dai, ɗaukakar Ubangiji ta yi kamar wuta mai ci a kan dutse.
L’aspect de la gloire de Yahweh était, aux yeux des enfants d’Israël, comme un feu dévorant sur le sommet de la montagne.
18 Sa’an nan Musa ya shiga girgijen ya hau kan dutsen. Ya zauna a kan dutsen yini arba’in da dare arba’in.
Moïse entra au milieu de la nuée, et monta à la montagne; et Moïse demeura sur la montagne quarante jours et quarante nuits.