< Fitowa 24 >

1 Ana nan sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Ku hauro zuwa wurina, kai da Haruna, Nadab da Abihu, da kuma dattawa saba’in a cikin Isra’ila. Za ku yi sujada da ɗan nisa,
Og han sagde til Moses: »Stig op til HERREN, du og Aron, Nadab og Abihu og halvfjerdsindstyve af Israels Ældste, og tilbed i Frastand;
2 sai Musa kaɗai zai kusaci Ubangiji. Amma sauran kada su zo kusa, kada kuma jama’a su hau tare da shi.”
Moses alene skal træde hen til HERREN, de andre ikke, og det øvrige Folk maa ikke følge med ham derop.«
3 Sa’ad da Musa ya tafi ya faɗa wa mutanen duk kalmomin Ubangiji da dokokinsa, sai suka amsa da murya ɗaya suna cewa, “Duk abin da Ubangiji ya faɗa, za mu yi.”
Derpaa kom Moses og kundgjorde hele Folket alle HERRENS Ord og alle Lovbudene, og hele Folket svarede enstemmigt: »Alle de Ord, HERREN har talet, vil vi overholde.«
4 Sai Musa ya rubuta duk abin da Ubangiji ya faɗa. Ya tashi kashegari da sassafe ya gina bagade kusa da dutsen, ya aza al’amudai goma sha biyu bisa ga kabilu goma sha biyu na Isra’ila.
Da skrev Moses alle HERRENS Ord op; og tidligt næste Morgen rejste han ved Foden af Bjerget et Alter og tolv Stenstøtter svarende til Israels tolv Stammer.
5 Sai ya aiki samarin Isra’ilawa, suka miƙa hadaya ta ƙonawa, suka kuma miƙa ƙananan bijimai don hadaya ta salama ga Ubangiji.
Derefter sendte han de unge Mænd blandt Israeliterne hen for at bringe Brændofre og slagte unge Tyre som Takofre til HERREN.
6 Musa ya ɗauki rabin jinin ya zuba a cikin kwanoni, rabin kuma ya yayyafa a kan bagaden.
Og Moses tog den ene Halvdel af Blodet og gød det i Offerskaalene, men den anden Halvdel sprængte han paa Alteret.
7 Sa’an nan ya ɗauki Littafin Alkawari ya karanta wa mutane. Suka amsa suka ce, “Za mu yi duk abin da Ubangiji ya faɗa; za mu yi biyayya.”
Saa tog han Pagtsbogen og læste den op i Folkets Paahør, og de sagde: »Vi vil gøre alt, hvad HERREN har talet, og lyde ham!«
8 Musa ya kuma ɗauki jinin, ya yayyafa a kan mutanen ya ce, “Wannan shi ne jinin alkawarin da Ubangiji ya yi da ku, bisa ga dukan waɗannan kalmomi.”
Derpaa tog Moses Blodet og sprængte det paa Folket, idet han sagde: »Se, dette er Pagtens Blod, den Pagt, HERREN har sluttet med eder paa Grundlag af alle disse Ord.«
9 Musa da Haruna, Nadab da Abihu, da dattawa saba’in, Allah na Isra’ila suka haura
Og Moses, Aron, Nadab og Abihu og halvfjerdsindstyve af Israels Ældste steg op
10 suka kuma ga Allah na Isra’ila. A ƙarƙashin ƙafafunsa akwai wani abu wanda aka yi da saffaya, mai haske kuma kamar sararin sama kansa.
og skuede Israels Gud; under hans Fødder var der ligesom Safirfliser, som selve Himmelen i Straaleglans.
11 Amma Allah bai yi wa shugabannin Isra’ila wani abu ba; suka ga Allah, suka ci suka kuma sha.
Men han lagde ikke Haand paa Israeliternes ypperste Mænd. De skuede Gud, og de spiste og drak.
12 Ubangiji ya ce wa Musa, “Hauro wurina a kan dutse, ka tsaya a nan, zan ba ka allunan dutsen, da doka da umarnan da na rubuta don koyonsu.”
Og HERREN sagde til Moses: »Stig op til mig paa Bjerget og bliv der, saa vil jeg give dig Stentavlerne, Loven og Budet, som jeg har opskrevet til Vejledning for dem.«
13 Sa’an nan Musa ya fita tare da Yoshuwa mataimakinsa, ya kuwa hau kan dutsen Allah.
Da bød Moses og Josua, hans Medhjælper op, og Moses steg op paa Guds Bjerg;
14 Ya ce wa dattawan, “Ku jira mu a nan, sai mun dawo wurinku. Haruna da Hur suna tare da ku, in wani yana da wata damuwa, sai yă je wurinsu.”
men til de Ældste sagde han: »Vent paa os her, til vi kommer tilbage til eder. Se, Aron og Hur er hos eder; er der nogen, der har en Retstrætte, kan han henvende sig til dem!«
15 Da Musa ya hau dutsen, sai girgije ya rufe dutsen,
Derpaa steg Moses op paa Bjerget. Da indhyllede Skyen Bjerget,
16 sai ɗaukakar Ubangiji ta sauka a kan Dutsen Sinai, kwana shida girgije ya rufe dutsen, a rana ta bakwai, sai Ubangiji ya kira Musa daga cikin girgijen.
og HERRENS Herlighed nedlod sig paa Sinaj Bjerg. Og Skyen indhyllede Sinaj Bjerg i seks Dage, men den syvende Dag raabte HERREN ud fra Skyen til Moses;
17 Ga Isra’ilawa dai, ɗaukakar Ubangiji ta yi kamar wuta mai ci a kan dutse.
og medens HERRENS Herlighed viste sig for Israeliternes Øjne som en fortærende Ild paa Bjergets Top,
18 Sa’an nan Musa ya shiga girgijen ya hau kan dutsen. Ya zauna a kan dutsen yini arba’in da dare arba’in.
gik Moses ind i Skyen og steg op paa Bjerget. Og Moses blev paa Bjerget i fyrretyve Dage og fyrretyve Nætter.

< Fitowa 24 >