< Fitowa 23 >

1 “Kada ku baza rahoton ƙarya. Kada kuma ku haɗa baki da mugayen mutane har da ku zama munafukai ta wurin ba da shaidar ƙarya.
Thou shalt not raise a false report: put not thy hand with the wicked to be an unrighteous witness.
2 “Kada ku yi abin da ba daidai ba, don galibin mutane suna yin haka. Sa’ad da kuke ba da shaida a gaban shari’a, kada ku ba da shaidar ƙarya a kauce wa gaskiya don ku faranta wa taron jama’a rai.
Thou shalt not follow a multitude to [do] evil; neither shalt thou speak in a cause to decline after many to wrest [judgment]:
3 Kada ku yi wa matalauci sonkai a gaban shari’a.
Neither shalt thou countenance a poor man in his cause.
4 “In ka ga saniyar abokin gābanka, ko jakinsa ya ɓace, ka yi ƙoƙari ka mai da shi wurinsa.
If thou shalt meet thy enemy's ox or his ass going astray, thou shalt surely bring it back to him again.
5 In ka ga jakin wani maƙiyinka ya fāɗi a ƙarƙashin kayan da ya ɗauka, kada ka bar shi can, ka yi ƙoƙari ka taimake shi.
If thou shalt see the ass of him that hateth thee lying under his burden, and wouldest forbear to help him, thou shalt surely help with him.
6 “Kada ku kāsa yin adalci ga matalauci a wurin shari’a.
Thou shalt not wrest the judgment of thy poor in his cause.
7 Ku yi nesa da ƙage. Kada ku kashe marar laifi tare da mai adalci, gama ba zan bar mugun yă tafi haka kawai ba.
Keep thee far from a false matter; and the innocent and righteous slay thou not: for I will not justify the wicked.
8 “Kada ka karɓi cin hanci, gama cin hanci yakan makanta waɗanda suke gani, yakan kuma karkatar da maganar masu adalci.
And thou shalt take no gift: for the gift blindeth the wise, and perverteth the words of the righteous.
9 “Kada ka zalunci baƙo, ku kanku kun san halin baƙunci, gama dā ku baƙi ne a Masar.
Also thou shalt not oppress a stranger; for ye know the heart of a stranger, seeing ye were strangers in the land of Egypt.
10 “Shekara shida za ku nome gonakinku ku girbe amfanin gonar,
And six years thou shalt sow thy land, and shalt gather in the fruits thereof:
11 amma a shekara ta bakwai za ku bar ƙasa tă huta. Sa’an nan matalautan da suke cikinku za su sami abinci daga cikinta, namun jeji kuma za su ci abin da aka bari. Ku yi haka da gonakinku na inabi, da na itatuwan zaitun.
But the seventh [year] thou shalt let it rest and lie still; that the poor of thy people may eat: and what they leave, the beasts of the field shall eat. In like manner thou shalt deal with thy vineyard, [and] with thy olive-yard.
12 “Kwana shida za ku yi aikinku, amma a rana ta bakwai, kada ku yi aiki, saboda saniyarku da jakinku su huta, haka kuma bawan da aka haifa a gidanku, da kuma baƙon da yake a cikinku yă wartsake.
Six days thou shalt do thy work, and on the seventh day thou shalt rest: that thy ox and thy ass may rest, and the son of thy handmaid, and the stranger, may be refreshed.
13 “Ku mai da hankali, ku yi biyayya da duk abin da na faɗa muku. Kada ku kira sunaye waɗansu alloli; kada a ji su a bakinku.
And in all [things] that I have said to you be circumspect: and make no mention of the names of other gods, neither let it be heard from thy mouth.
14 “Sau uku a shekara za ku yi mini biki.
Three times thou shalt keep a feast to me in the year.
15 “Ku yi Bikin Burodi Marar Yisti, kwana bakwai za ku ci burodi marar yisti, kamar yadda na umarce ku. Ku yi wannan a lokacin da aka ayana a watan Abib, gama a watan ne kuka fito daga Masar. “Kada wani yă zo a gabana hannu wofi.
Thou shalt keep the feast of unleavened bread: (thou shalt eat unleavened bread seven days, as I commanded thee, in the time appointed of the month Abib; for in it thou camest out from Egypt: and none shall appear before me empty: )
16 “Ku yi Bikin Girbi da nunan fari na amfanin shuke-shuken gonarku. “Ku yi Bikin Tattarawa a ƙarshen shekara, sa’ad da kuka tattara amfani daga gonarku.
And the feast of harvest, the first-fruits of thy labors, which thou hast sown in the field: and the feast of in-gathering, [which] is in the end of the year, when thou hast gathered in thy labors out of the field.
17 “Sau uku a shekara, maza duka za su bayyana a gaban Ubangiji Mai Iko Duka.
Three times in the year all thy males shall appear before the LORD God.
18 “Kada ku miƙa mini hadayar jini tare da wani abu mai yisti. “Ba za a bar kitsen bikin hadayata yă kwana ba.
Thou shalt not offer the blood of my sacrifice with leavened bread; neither shall the fat of my sacrifice remain until the morning.
19 “Dole ne ku kawo mafi kyau daga nunan fari na gonakinku a gidan Ubangiji Allahnku. “Kada ku dafa ɗan akuya a cikin madarar mahaifiyarsa.
The first of the first-fruits of thy land thou shalt bring into the house of the LORD thy God. Thou shalt not seethe a kid in his mother's milk.
20 “Ga shi, zan aika mala’ika a gabanku, yă tsare ku a tafiyarku, yă kuma kawo ku wurin da na shirya.
Behold, I send an Angel before thee, to keep thee in the way, and to bring thee into the place which I have prepared.
21 Ku saurare shi, ku kuma kasa kunne ga abin da yake faɗa. Kada ku yi masa tawaye; ba zai gafarta tawayenku ba, gama shi wakilina ne.
Beware of him, and obey his voice, provoke him not; for he will not pardon your transgressions: for my name [is] in him.
22 In kun kasa kunne sosai ga abin da yake faɗi, kuka kuma yi abin da na faɗa, zan zama magabci ga abokan gābanku, zan kuma yi hamayya da abokan hamayyanku.
But if thou shalt indeed obey his voice, and do all that I speak; then I will be an enemy to thy enemies, and an adversary to thy adversaries.
23 Mala’ikana zai sha gabanku, yă kawo ku cikin ƙasar Amoriyawa, da Hittiyawa, da Ferizziyawa, da Kan’aniyawa, da Hiwiyawa, da kuma Yebusiyawa, zan kuma kawar da su.
For my Angel shall go before thee, and bring thee in to the Amorites, and the Hittites, and the Perizzites, and the Canaanites, [and] the Hivites, and the Jebusites; and I will cut them off.
24 Kada ku durƙusa wa allolinsu, ko ku yi musu sujada, ko kuma ku bi al’adunsu. Za ku hallaka dukan allolinsu, ku kuma farfasa keɓaɓɓun duwatsunsu.
Thou shalt not bow down to their gods, nor serve them, nor do after their works: but thou shalt utterly overthrow them, and quite break down their images.
25 Ku bauta wa Ubangiji Allahnku, albarkansa kuwa za tă kasance a kan abincinku da ruwan shanku. Zan ɗauke cuta daga cikinku.
And ye shall serve the LORD your God, and he will bless thy bread, and thy water; and I will take sickness away from the midst of thee.
26 A ƙasarku, mace ba za tă yi ɓari ba, ba kuma za a sami marar haihuwa ba. Zan ba ku tsawon rai.
There shall nothing cast their young, nor be barren, in thy land: I will complete the number of thy days.
27 “Zan aiki razanata a gabanku, in kuma sa ruɗami a cikin kowace al’ummar da za ku sadu da ita. Zan sa duk abokan gābanku su juye da baya, su gudu.
I will send my fear before thee, and will destroy all the people to whom thou shalt come, and I will make all thy enemies turn their backs to thee.
28 Zan aiki rina a gabanku, su kori Hiwiyawa, Kan’aniyawa da kuma Hittiyawa.
And I will send hornets before thee, which shall drive out the Hivite, the Canaanite, and the Hittite from before thee.
29 Amma ba a shekara guda zan kore muku su ba, don kada ƙasar tă zama kufai har namun jeji su fi ƙarfinku.
I will not drive them out from before thee in one year; lest the land should become desolate, and the beast of the field should multiply against thee.
30 Da kaɗan da kaɗan zan kore muku su, har yawanku yă kai yadda za ku mallaki ƙasar.
By little and little I will drive them out from before thee, until thou shalt be increased and inherit the land.
31 “Zan kafa iyakokinku daga Jan Teku zuwa Bahar Rum, daga hamada kuma zuwa Kogi. Zan ba da mazaunan ƙasar a hannunku, za ku kuwa kore su daga gabanku.
And I will set thy bounds from the Red sea even to the sea of the Philistines, and from the desert to the river: for I will deliver the inhabitants of the land into your hand; and thou shalt drive them out before thee.
32 Kada ku ƙulla yarjejjeniya da su, ko da allolinsu.
Thou shalt make no covenant with them, nor with their gods.
33 Kada ku bari su zauna a cikin ƙasarku, in har kuka bar su, za su ɓata ku da zunubinsu na bautar allolinsu, har zai yă zama muku tarko.”
They shall not dwell in thy land, lest they make thee to sin against me: for if thou shalt serve their gods, it will surely be a snare to thee.

< Fitowa 23 >