< Fitowa 23 >

1 “Kada ku baza rahoton ƙarya. Kada kuma ku haɗa baki da mugayen mutane har da ku zama munafukai ta wurin ba da shaidar ƙarya.
“Do not tell to others (false rumors/untrue reports) about other people. Do not help someone who is guilty by (testifying falsely/lying) [about what happened].
2 “Kada ku yi abin da ba daidai ba, don galibin mutane suna yin haka. Sa’ad da kuke ba da shaida a gaban shari’a, kada ku ba da shaidar ƙarya a kauce wa gaskiya don ku faranta wa taron jama’a rai.
Do not join a group of people who are planning to do something evil. Do not testify the way the [crowd wants you to], if that will prevent [the judge from deciding the case] justly/fairly.
3 Kada ku yi wa matalauci sonkai a gaban shari’a.
When a poor person is on trial, do not [testify in] his favor [just] because he is poor [and you feel sorry for him].
4 “In ka ga saniyar abokin gābanka, ko jakinsa ya ɓace, ka yi ƙoƙari ka mai da shi wurinsa.
If you see someone’s bull or donkey when it is wandering away [loose], take it back to [its owner, even if the owner] is your enemy.
5 In ka ga jakin wani maƙiyinka ya fāɗi a ƙarƙashin kayan da ya ɗauka, kada ka bar shi can, ka yi ƙoƙari ka taimake shi.
If you see someone’s donkey that has fallen down [because of its heavy load], help the owner to get the donkey up again, [even if] he is someone who hates you. Do not just walk away [without helping him].
6 “Kada ku kāsa yin adalci ga matalauci a wurin shari’a.
Decide the cases of poor people who are on trial [as] fairly [as you decide the cases of other people].
7 Ku yi nesa da ƙage. Kada ku kashe marar laifi tare da mai adalci, gama ba zan bar mugun yă tafi haka kawai ba.
Do not accuse people falsely. Do not decide that innocent and righteous [DOU] people should be executed, because I will (punish/not forgive) people who do such an evil thing.
8 “Kada ka karɓi cin hanci, gama cin hanci yakan makanta waɗanda suke gani, yakan kuma karkatar da maganar masu adalci.
Do not accept money that is a bribe, because officials who accept bribes are not able to [MTY] decide what is right to do, and they do not allow innocent people to be treated fairly.
9 “Kada ka zalunci baƙo, ku kanku kun san halin baƙunci, gama dā ku baƙi ne a Masar.
Do not mistreat foreigners [who live among you]. You know [how people often treat] foreigners, because the Egyptians [did not treat you well when] you were foreigners there.
10 “Shekara shida za ku nome gonakinku ku girbe amfanin gonar,
Plant [seeds] in your ground and gather the harvest for six years.
11 amma a shekara ta bakwai za ku bar ƙasa tă huta. Sa’an nan matalautan da suke cikinku za su sami abinci daga cikinta, namun jeji kuma za su ci abin da aka bari. Ku yi haka da gonakinku na inabi, da na itatuwan zaitun.
But during the seventh year you must not plant anything. [If things grow without your planting seeds], allow poor people [to harvest and] eat the crops. If there are still crops (left over/that they do not harvest), allow wild animals to eat them. Do the same thing with your grapevines/vineyards and your olive trees.
12 “Kwana shida za ku yi aikinku, amma a rana ta bakwai, kada ku yi aiki, saboda saniyarku da jakinku su huta, haka kuma bawan da aka haifa a gidanku, da kuma baƙon da yake a cikinku yă wartsake.
[You may] work for six days [each week], but on the seventh day you must rest [and not work]. And on the seventh day you must allow your work animals and your slaves and the foreigners [who live among you] also [to rest and] be refreshed.
13 “Ku mai da hankali, ku yi biyayya da duk abin da na faɗa muku. Kada ku kira sunaye waɗansu alloli; kada a ji su a bakinku.
Make certain that you obey everything that I have commanded [you to do]. Do not pray to [MTY] other gods. Do not even mention their names.”
14 “Sau uku a shekara za ku yi mini biki.
“Every year you must celebrate three festivals to [honor] me.
15 “Ku yi Bikin Burodi Marar Yisti, kwana bakwai za ku ci burodi marar yisti, kamar yadda na umarce ku. Ku yi wannan a lokacin da aka ayana a watan Abib, gama a watan ne kuka fito daga Masar. “Kada wani yă zo a gabana hannu wofi.
[The first one] is the Festival of Bread That Has No Yeast. Celebrate it in the month [that is named] Abib. That is the month in which you left Egypt. Celebrate it in the way that I commanded you. And always bring [LIT] an offering when you come to worship me.
16 “Ku yi Bikin Girbi da nunan fari na amfanin shuke-shuken gonarku. “Ku yi Bikin Tattarawa a ƙarshen shekara, sa’ad da kuka tattara amfani daga gonarku.
The second one is the Festival of Harvesting. During that festival you must offer to me the first parts/harvest of your crops that grow from the seeds that you planted. The third one is the Festival of Living in Temporary Shelters. That will be after you finish harvesting your grain and grapes and fruit.
17 “Sau uku a shekara, maza duka za su bayyana a gaban Ubangiji Mai Iko Duka.
Every year, at each of these times, all the men must gather together to worship me, Yahweh God.
18 “Kada ku miƙa mini hadayar jini tare da wani abu mai yisti. “Ba za a bar kitsen bikin hadayata yă kwana ba.
When you sacrifice an animal [and offer it] to me, you must not offer bread that has been baked with yeast. [When you] offer sacrifices, [burn] the fat [from the animals on that same day]. Do not allow any fat to remain until the next morning.
19 “Dole ne ku kawo mafi kyau daga nunan fari na gonakinku a gidan Ubangiji Allahnku. “Kada ku dafa ɗan akuya a cikin madarar mahaifiyarsa.
Each year, when you harvest your crops, bring to the place where you worship me, Yahweh God, the first part of what you harvest. When you kill a (young animal/kid [or lamb or calf)], do not [prepare to eat it by] boiling it in its mother’s milk.”
20 “Ga shi, zan aika mala’ika a gabanku, yă tsare ku a tafiyarku, yă kuma kawo ku wurin da na shirya.
“Note this: I am going to send an angel ahead of you, to guard you as you travel and to bring you safely to the place that I have prepared [for you]. Pay attention to what he says and obey him. Do not rebel against him, because he will have my authority [MTY] and he will (punish/not forgive) [LIT] you if you rebel against him.
21 Ku saurare shi, ku kuma kasa kunne ga abin da yake faɗa. Kada ku yi masa tawaye; ba zai gafarta tawayenku ba, gama shi wakilina ne.
22 In kun kasa kunne sosai ga abin da yake faɗi, kuka kuma yi abin da na faɗa, zan zama magabci ga abokan gābanku, zan kuma yi hamayya da abokan hamayyanku.
But if you pay attention to what he says and if you do all that I tell you [to do], I will fight strongly [DOU] against all of your enemies.
23 Mala’ikana zai sha gabanku, yă kawo ku cikin ƙasar Amoriyawa, da Hittiyawa, da Ferizziyawa, da Kan’aniyawa, da Hiwiyawa, da kuma Yebusiyawa, zan kuma kawar da su.
My angel will go ahead of you, and will take you to where the Amor and Heth and Periz and Canaan and Hiv and Jebus people-groups live, and I will completely get rid of them.
24 Kada ku durƙusa wa allolinsu, ko ku yi musu sujada, ko kuma ku bi al’adunsu. Za ku hallaka dukan allolinsu, ku kuma farfasa keɓaɓɓun duwatsunsu.
Do not bow down before their gods/idols or worship them. And do not do the things [that they think that their gods want] them to do. Completely destroy their gods/idols, and smash to pieces their sacred stones.
25 Ku bauta wa Ubangiji Allahnku, albarkansa kuwa za tă kasance a kan abincinku da ruwan shanku. Zan ɗauke cuta daga cikinku.
You must worship me, Yahweh God. [If you do that], I will bless your (OR, bless [you by giving you]) food and water, and I will protect you from becoming sick.
26 A ƙasarku, mace ba za tă yi ɓari ba, ba kuma za a sami marar haihuwa ba. Zan ba ku tsawon rai.
No women in your land will have (miscarriages/babies that will die after being born prematurely), and no women will be unable to become pregnant. And I will enable you to live a long time.
27 “Zan aiki razanata a gabanku, in kuma sa ruɗami a cikin kowace al’ummar da za ku sadu da ita. Zan sa duk abokan gābanku su juye da baya, su gudu.
I will cause the people who oppose you to become very afraid of me. I will cause the people whom you fight against to become very confused. And then I will cause them to turn around and run away from you.
28 Zan aiki rina a gabanku, su kori Hiwiyawa, Kan’aniyawa da kuma Hittiyawa.
I will cause your enemies to become terrified. And I will expel the Hiv, Canaan, and Heth people-groups from your land.
29 Amma ba a shekara guda zan kore muku su ba, don kada ƙasar tă zama kufai har namun jeji su fi ƙarfinku.
I will not expel [all of] them in less than one year. If I did that, your land would become deserted, and there would be very many wild animals ([that would attack you/you would not be able to control]).
30 Da kaɗan da kaɗan zan kore muku su, har yawanku yă kai yadda za ku mallaki ƙasar.
I will expel those people-groups slowly, a few at a time, until the number of your people increases and you are able to live everywhere in the land.
31 “Zan kafa iyakokinku daga Jan Teku zuwa Bahar Rum, daga hamada kuma zuwa Kogi. Zan ba da mazaunan ƙasar a hannunku, za ku kuwa kore su daga gabanku.
I will cause the borders of your land to extend from the (Red Sea/Gulf of Aqaba) [in the southeast] to the Mediterranean Sea [in the northwest], and from the [Sinai] Desert [in the southwest] to the [Euphrates] River [in the northeast of the country]. I will enable you [MTY] to expel the people who live there, so that you will expel them as you occupy more of the country.
32 Kada ku ƙulla yarjejjeniya da su, ko da allolinsu.
You must not make any agreement/treaty with those people or with their gods.
33 Kada ku bari su zauna a cikin ƙasarku, in har kuka bar su, za su ɓata ku da zunubinsu na bautar allolinsu, har zai yă zama muku tarko.”
Do not allow [those people] to live in your land, in order that they do not cause you to sin against me. If you worship their gods, [you will not be able to escape from worshiping them and sinning against me, just like someone caught] in a trap [is unable to escape] [MET].”

< Fitowa 23 >