< Fitowa 22 >

1 “In mutum ya saci saniya ko tunkiya ya yanka, ko ya sayar, zai biya shanu biyar, a maimakon saniyar da ya sata, ko kuma tumaki huɗu, maimakon tunkiyar da ya sata.
“Se um homem rouba um boi ou uma ovelha, e a mata ou vende, pagará cinco bois por um boi, e quatro ovelhas por uma ovelha.
2 “In aka iske ɓarawo yana cikin ƙoƙarin shiga yă yi sata, aka buge shi har ya mutu, to, ba za a nemi alhakin jininsa daga wurin kowa ba;
Se o ladrão for encontrado arrombando e for atingido para que morra, não haverá culpa de derramamento de sangue por ele.
3 amma in ya faru bayan wayewar gari, to, za a nemi alhakin jinin ɓarawon a hannun wanda ya bugi ɓarawon. “Ɓarawon da aka kama da abin da ya sata, dole yă yi cikakkiyar ramuwa, amma in ba shi da kome, dole a sayar da shi a biya abin da ya sata.
Se o sol se levantou sobre ele, ele é culpado de derramamento de sangue. Ele deverá fazer a restituição. Se ele não tiver nada, então será vendido por seu roubo.
4 In an sami dabbar, ko saniya, ko jaki, ko tunkiya da ya sata da rai a hannunsa, dole ɓarawon yă biya taran da za a ci shi, sau biyu na kowane ɗaya.
Se o bem roubado for encontrado vivo na mão dele, seja boi, burro ou ovelha, ele pagará o dobro.
5 “In mutum ya sa dabbobinsa su yi kiwo a fili ko a gonar inabi, ya kuma bar dabbobinsa suka yi ɓarna a cikin gonar wani, sai a sa mai dabbar yă biya tara daga amfanin gonarsa mafi kyau duka.
“Se um homem faz com que um campo ou vinhedo seja comido deixando seu animal solto, e ele pasta no campo de outro homem, ele fará a restituição do melhor de seu próprio campo, e do melhor de seu próprio vinhedo.
6 “In gobara ta tashi, ta kuma bazu cikin ƙayayyuwa, har ta cinye tarin hatsi, ko hatsin da ke tsaye, ko dukan gonar, dole wanda ya sa wutar, yă biya taran da aka yanka masa saboda ɓarnan da wutar ta yi.
“Se o fogo irromper, e pegar em espinhos para que os choques do grão, ou o grão em pé, ou o campo sejam consumidos; aquele que ateou o fogo certamente fará a restituição.
7 “In mutum ya ba maƙwabcinsa azurfa, ko kaya ajiya, aka kuma sace su daga gidan maƙwabcin, in an kama ɓarawon, sai ɓarawon yă biya abin da ya sata har sau biyu.
“Se um homem entregar ao seu vizinho dinheiro ou coisas para guardar, e for roubado da casa do homem, se o ladrão for encontrado, ele pagará o dobro.
8 Amma in ba a sami ɓarawon ba, sai wanda aka yi ajiyar a gidansa, yă bayyana a gaban alƙalai a bincika ko yana da hannu a kan kayan maƙwabcinsa.
Se o ladrão não for encontrado, então o dono da casa se aproximará de Deus, para saber se ele pôs ou não a mão nos bens de seu próximo.
9 A kowane rikicin cin amana da zai shiga tsakanin mutum biyu, ko a kan bijimi, ko jaki, ko tunkiya, ko riga, kai, ko a kan kowane irin abin da ya ɓata, da ma abin da aka samu a hannun wani, in akwai jayayya, za a kawo mutumin a gaban alƙalai. Wanda alƙali ya ce shi ne mai laifi, sai yă biya ɗayan taran da za a yanka, har sau biyu.
Para cada questão de transgressão, seja por boi, por burro, por ovelha, por roupa, ou por qualquer tipo de coisa perdida, sobre a qual se diz: “Isto é meu”, a causa de ambas as partes virá perante Deus. Aquele que Deus condena pagará o dobro a seu próximo.
10 “In mutum ya ba da jaki, ko saniya, ko tunkiya, ko kowace dabba wa maƙwabcinsa ajiya, sai abin ya mutu, ko ya ji rauni, ko an ɗauke shi, in ba shaida,
“Se um homem entregar ao seu próximo um burro, um boi, uma ovelha ou qualquer animal para guardar, e ele morrer ou for ferido, ou expulso, nenhum homem o verá;
11 rantsuwa ce za tă raba tsakaninsu a gaban Ubangiji cewa babu hannunsa a dukiyar maƙwabcinsa. Mai dukiyar kuwa zai yarda da rantsuwar, ba za a bukaci wanda aka bai wa amanar yă biya ba.
o juramento de Javé estará entre ambos, ele não terá colocado sua mão sobre os bens de seu próximo; e seu dono o aceitará, e ele não fará restituição.
12 Amma idan satan dabbar ce aka yi, dole wanda aka bai wa ajiyar yă biya mai dabbar taran da aka ci masa.
Mas se lhe for roubado, aquele que o roubou fará a restituição ao seu proprietário.
13 In naman jeji ne ya kashe ta, zai nuna gawar don shaida, ba za a kuwa sa maƙwabcin yă biya abin da naman jeji ya kashe ba.
Se for despedaçada, deixe-o trazê-la como prova. Ele não deverá reparar o que foi rasgado.
14 “In mutum ya yi aron dabba daga wurin maƙwabcinsa, sai dabbar ta ji rauni ko ta mutu, yayinda mai shi ba ya nan, dole wanda ya yi aron dabbar yă biya.
“Se um homem tomar emprestado algo de seu vizinho, e ele for ferido, ou morrer, seu dono não estiver com ele, ele certamente fará a restituição.
15 Amma idan mai dabbar yana a wurin, wanda ya karɓa aron, ba zai biya kome ba. In an yi hayar dabbar ce, to, kuɗin da aka biya na hayar zai zama a madadin rashin.
Se seu proprietário estiver com ele, ele não o fará bem. Se for uma coisa alugada, ela veio para seu arrendamento.
16 “Idan mutum ya ruɗe budurwa, wadda ba wanda yake nemanta, ya kuma kwanta da ita, dole yă biya kuɗin aurenta, za tă kuma zama matarsa.
“Se um homem atrai uma virgem que não se compromete a se casar e se deita com ela, certamente pagará um dote para que ela seja sua esposa.
17 In mahaifinta ya ƙi yă ba da ita ga mutumin, dole mutumin yă biya dukiya daidai da abin da akan biya domin budurwai.
If seu pai se recusa totalmente a dá-la a ele, ele pagará dinheiro de acordo com o dote de virgens.
18 “Kada ku bar maiya da rai.
“Você não deve permitir que uma feiticeira viva.
19 “Duk mutumin da ya yi jima’i da dabba dole a kashe shi.
“Quem fizer sexo com um animal certamente será condenado à morte.
20 “Duk wanda ya yi hadaya ga wani allah ban da Ubangiji, dole a hallaka shi.
“Aquele que se sacrifica a qualquer deus, exceto a Iavé somente, será totalmente destruído.
21 “Kada a wulaƙanta, ko a zalunci baƙo, domin dā ku baƙi ne a ƙasar Masar.
“Você não deve enganar um estrangeiro ou oprimi-lo, pois você foi um estrangeiro na terra do Egito.
22 “Kada ku ci zalin gwauruwa, ko maraya.
“Você não deve tirar proveito de nenhuma viúva ou criança sem pai.
23 In kuka yi haka, idan kuma suka yi kuka gare ni, zan ji kukansu.
Se você se aproveitar deles, e eles chorarem para mim, certamente ouvirei seu grito;
24 Zan husata, in kuma kashe ku da takobi; matanku kuma, su ma su zama gwauraye,’ya’yanku kuwa su zama marayu.
e minha ira se acenderá, e eu vos matarei com a espada; e vossas mulheres serão viúvas, e vossos filhos órfãos de pai.
25 “In kun ba wa jama’ata matalauta da suke tsakaninku bashin kuɗi, kada ku zama kamar masu ba da rance; kada ku sa yă biya da ruwa.
“Se você emprestar dinheiro a qualquer um de meu povo com você que é pobre, você não será para ele como credor. Você não lhe cobrará juros.
26 In kun ɗauki mayafi maƙwabcinku a matsayin jingina, ku mayar masa kafin fāɗuwar rana,
Se você levar a roupa de seu vizinho como garantia, você a devolverá a ele antes do sol se pôr,
27 domin mayafin ne abin da yake da shi na rufe jikinsa. To, da me zai rufu yă yi barci? Sa’ad da ya yi mini kuka, zan ji, gama ni mai tausayi ne.
pois essa é sua única cobertura, é sua roupa para sua pele. Em que ele dormiria? Acontecerá, quando ele chorar para mim, que eu ouvirei, pois sou gracioso.
28 “Kada ku yi maganar saɓo ga Allah, ko ku la’anta mai mulkin mutanenku.
“Você não blasfemará contra Deus, nem amaldiçoará um governante de seu povo.
29 “Kada ku jinkirta fitar da zakarku daga rumbunanku, ko harajin kayan da kuka saya. “Dole ku ba ni’ya’yan farinku maza.
“Você não deve demorar a oferecer a partir de sua colheita e da saída de suas prensas. “Você me dará o primogênito de seus filhos”.
30 Ku yi haka da shanunku da tumakinku. Bari su kasance da iyayensu mata, har kwana bakwai, amma ku ba ni su a rana ta takwas.
Você fará o mesmo com seu gado e com suas ovelhas”. Estará com sua mãe sete dias, depois no oitavo dia mo darás”.
31 “Za ku kasance mutanena masu tsarki. Saboda kada ku ci naman da namun jeji suka kashe; ku jefa wa karnuka.
“Vocês serão homens santos para mim, portanto não comerão nenhuma carne que seja rasgada por animais no campo. Vocês a jogarão para os cães.

< Fitowa 22 >