< Fitowa 22 >

1 “In mutum ya saci saniya ko tunkiya ya yanka, ko ya sayar, zai biya shanu biyar, a maimakon saniyar da ya sata, ko kuma tumaki huɗu, maimakon tunkiyar da ya sata.
Jeźliby kto ukradł wołu albo owcę, i zabiłby je, albo je sprzedał, pięć wołów wróci za jednego wołu, a cztery owce za jedną owcę,
2 “In aka iske ɓarawo yana cikin ƙoƙarin shiga yă yi sata, aka buge shi har ya mutu, to, ba za a nemi alhakin jininsa daga wurin kowa ba;
Jeźliby przy podkopywaniu zastany był złodziej, a ubity będąc umarłby, kto zabił, nie będzie winien krwi;
3 amma in ya faru bayan wayewar gari, to, za a nemi alhakin jinin ɓarawon a hannun wanda ya bugi ɓarawon. “Ɓarawon da aka kama da abin da ya sata, dole yă yi cikakkiyar ramuwa, amma in ba shi da kome, dole a sayar da shi a biya abin da ya sata.
Jeźliby to po wejściu słońca uczynił, krwi winien będzie, koniecznie wróci; a jeźli nie ma, sprzedany będzie za złodziejstwo swoje.
4 In an sami dabbar, ko saniya, ko jaki, ko tunkiya da ya sata da rai a hannunsa, dole ɓarawon yă biya taran da za a ci shi, sau biyu na kowane ɗaya.
Jeźli znaleziona będzie w ręku jego rzecz kradziona, bądź wół, bądź osieł, bądź owca, jeszcze żywe, we dwójnasób wróci.
5 “In mutum ya sa dabbobinsa su yi kiwo a fili ko a gonar inabi, ya kuma bar dabbobinsa suka yi ɓarna a cikin gonar wani, sai a sa mai dabbar yă biya tara daga amfanin gonarsa mafi kyau duka.
Gdyby wypasł kto pole, albo winnicę, i puściłby bydlę swoje, aby się pasło na polu cudzem: z najlepszego urodzaju pola swego, i z najlepszego urodzaju winnicy swej nagrodzi.
6 “In gobara ta tashi, ta kuma bazu cikin ƙayayyuwa, har ta cinye tarin hatsi, ko hatsin da ke tsaye, ko dukan gonar, dole wanda ya sa wutar, yă biya taran da aka yanka masa saboda ɓarnan da wutar ta yi.
Jeźliby wyszedł ogień, a trafiłby na ciernie, i spaliłby stóg, albo stojące zboże, albo pole samo, koniecznie nagrodzi ten, co zapalił, co zgorzało.
7 “In mutum ya ba maƙwabcinsa azurfa, ko kaya ajiya, aka kuma sace su daga gidan maƙwabcin, in an kama ɓarawon, sai ɓarawon yă biya abin da ya sata har sau biyu.
Gdyby kto dał bliźniemu swemu srebro, albo naczynie do schowania, a to by ukradziono było z domu onego człowieka: jeźliby znaleziony był złodziej, wróci dwojako.
8 Amma in ba a sami ɓarawon ba, sai wanda aka yi ajiyar a gidansa, yă bayyana a gaban alƙalai a bincika ko yana da hannu a kan kayan maƙwabcinsa.
Jeźliby nie był znaleziony złodziej, stawi się pan domu onego przed sędziów, i przysięże, że nie ściągnął ręki swojej na rzecz bliźniego swego.
9 A kowane rikicin cin amana da zai shiga tsakanin mutum biyu, ko a kan bijimi, ko jaki, ko tunkiya, ko riga, kai, ko a kan kowane irin abin da ya ɓata, da ma abin da aka samu a hannun wani, in akwai jayayya, za a kawo mutumin a gaban alƙalai. Wanda alƙali ya ce shi ne mai laifi, sai yă biya ɗayan taran da za a yanka, har sau biyu.
O każdą rzecz, o którą by był spór, o wołu, o osła, o owcę, o szatę, o każdą, rzecz zgubioną, gdyby kto rzekł, że to jest moje, przed sędziów przyjdzie sprawa obydwu; kogo winnym znajdą sędziowie, nagrodzi w dwójnasób bliźniemu swemu.
10 “In mutum ya ba da jaki, ko saniya, ko tunkiya, ko kowace dabba wa maƙwabcinsa ajiya, sai abin ya mutu, ko ya ji rauni, ko an ɗauke shi, in ba shaida,
Jeźliby kto dał bliźniemu swemu osła, albo wołu, albo owcę, albo inne bydlę na chowanie, a zdechłoby albo okaleczało, albo gwałtem zajęte było, gdzie by nikt nie widział:
11 rantsuwa ce za tă raba tsakaninsu a gaban Ubangiji cewa babu hannunsa a dukiyar maƙwabcinsa. Mai dukiyar kuwa zai yarda da rantsuwar, ba za a bukaci wanda aka bai wa amanar yă biya ba.
Przysięga Pańska będzie między obiema, że nie ściągnął ręki swej na rzecz bliźniego swego: i przyjmie pan onej rzeczy przysięgę, a on nie będzie nagradzał.
12 Amma idan satan dabbar ce aka yi, dole wanda aka bai wa ajiyar yă biya mai dabbar taran da aka ci masa.
A jeźliby mu to kradzieżą wzięto, nagrodzi panu rzeczy onej.
13 In naman jeji ne ya kashe ta, zai nuna gawar don shaida, ba za a kuwa sa maƙwabcin yă biya abin da naman jeji ya kashe ba.
Jeźliby od zwierza rozszarpane było, postawi rozszarpane za świadka, a rozszarpanego nie nagrodzi.
14 “In mutum ya yi aron dabba daga wurin maƙwabcinsa, sai dabbar ta ji rauni ko ta mutu, yayinda mai shi ba ya nan, dole wanda ya yi aron dabbar yă biya.
Gdyby też kto pożyczył bydlęcia od bliźniego swego, a okaleczałoby, albo zdechło w niebytności pana jego, koniecznie nagrodzi.
15 Amma idan mai dabbar yana a wurin, wanda ya karɓa aron, ba zai biya kome ba. In an yi hayar dabbar ce, to, kuɗin da aka biya na hayar zai zama a madadin rashin.
Jeźliby pan jego był przy nim, nie będzie nagradzał; a jeźliby najęte było, najem tylko zapłaci.
16 “Idan mutum ya ruɗe budurwa, wadda ba wanda yake nemanta, ya kuma kwanta da ita, dole yă biya kuɗin aurenta, za tă kuma zama matarsa.
Jeźliby kto zwiódł pannę, która nie jest poślubiona, i spałby z nią, da jej koniecznie wiano, i weźmie ją sobie za żonę.
17 In mahaifinta ya ƙi yă ba da ita ga mutumin, dole mutumin yă biya dukiya daidai da abin da akan biya domin budurwai.
Jeźliby żadną miarą ojciec jej nie chciał mu jej dać, odważy srebra według zwyczaju wiana panieńskiego.
18 “Kada ku bar maiya da rai.
Czarownicy żyć nie dopuścisz.
19 “Duk mutumin da ya yi jima’i da dabba dole a kashe shi.
Każdy, kto by się złączał z bydlęciem, śmiercią umrze.
20 “Duk wanda ya yi hadaya ga wani allah ban da Ubangiji, dole a hallaka shi.
Kto by ofiarował bogom, oprócz samego Pana, wytracony będzie.
21 “Kada a wulaƙanta, ko a zalunci baƙo, domin dā ku baƙi ne a ƙasar Masar.
Przychodniowi nie uczynisz krzywdy, ani go uciśniesz: boście byli przychodniami w ziemi Egipskiej.
22 “Kada ku ci zalin gwauruwa, ko maraya.
Żadnej wdowy ani sieroty trapić nie będziecie.
23 In kuka yi haka, idan kuma suka yi kuka gare ni, zan ji kukansu.
Jeźlibyś je bez litości trapił, a one by wołały do mnie, słysząc wysłucham wołanie ich.
24 Zan husata, in kuma kashe ku da takobi; matanku kuma, su ma su zama gwauraye,’ya’yanku kuwa su zama marayu.
I rozgniewa się zapalczywość moja, a pobiję was mieczem, i będą żony wasze wdowami, a synowie wasi sierotami.
25 “In kun ba wa jama’ata matalauta da suke tsakaninku bashin kuɗi, kada ku zama kamar masu ba da rance; kada ku sa yă biya da ruwa.
Jeźlibyś pieniędzy pożyczył ludowi memu ubogiemu, który mieszka z tobą, nie bądziesz mu jako lichwiarz, nie obciążycie go lichwą.
26 In kun ɗauki mayafi maƙwabcinku a matsayin jingina, ku mayar masa kafin fāɗuwar rana,
Jeźli w zastawie weźmiesz szatę bliźniego twego, przed zachodem słońca wrócisz mu ją;
27 domin mayafin ne abin da yake da shi na rufe jikinsa. To, da me zai rufu yă yi barci? Sa’ad da ya yi mini kuka, zan ji, gama ni mai tausayi ne.
Bo to odzienie jego tylko to jest nakrycie ciała jego, na którem sypia; będzieli do mnie wołał, wysłucham go, bom Ja miłosierny.
28 “Kada ku yi maganar saɓo ga Allah, ko ku la’anta mai mulkin mutanenku.
Sędziom nie będziesz złorzeczył, a przełożonego ludu twego nie będziesz przeklinał.
29 “Kada ku jinkirta fitar da zakarku daga rumbunanku, ko harajin kayan da kuka saya. “Dole ku ba ni’ya’yan farinku maza.
Z obfitości zboża, i ciekących rzeczy twych nie omieszkasz pierwiastek ofiarować; pierworodnego z synów twoich oddasz mi.
30 Ku yi haka da shanunku da tumakinku. Bari su kasance da iyayensu mata, har kwana bakwai, amma ku ba ni su a rana ta takwas.
Toż uczynisz z wołów twych i z owiec twoich; siedem dni będzie z matką swoją, a ósmego dnia oddasz mi je.
31 “Za ku kasance mutanena masu tsarki. Saboda kada ku ci naman da namun jeji suka kashe; ku jefa wa karnuka.
Ludem świętym będziecie mi, a mięsa na polu rozszarpanego jeść nie będziecie; psom je wyrzucicie.

< Fitowa 22 >