< Fitowa 22 >

1 “In mutum ya saci saniya ko tunkiya ya yanka, ko ya sayar, zai biya shanu biyar, a maimakon saniyar da ya sata, ko kuma tumaki huɗu, maimakon tunkiyar da ya sata.
«اگر کسی گاو یا گوسفندی را بدزدد و بفروشد یا سر ببرد باید به عوض گاوی که دزدیده پنج گاو و به عوض گوسفند، چهار گوسفند پس بدهد.
2 “In aka iske ɓarawo yana cikin ƙoƙarin shiga yă yi sata, aka buge shi har ya mutu, to, ba za a nemi alhakin jininsa daga wurin kowa ba;
اگر دزدی در حال نَقب زدن گرفتار شود و او را بزنند به طوری که بمیرد، کسی که او را کشته مجرم نخواهد بود.
3 amma in ya faru bayan wayewar gari, to, za a nemi alhakin jinin ɓarawon a hannun wanda ya bugi ɓarawon. “Ɓarawon da aka kama da abin da ya sata, dole yă yi cikakkiyar ramuwa, amma in ba shi da kome, dole a sayar da shi a biya abin da ya sata.
اما اگر این کار در روز روشن واقع شود، کسی که او را کشته مجرم شناخته خواهد شد. «دزدی که گرفتار شود باید هر چه را دزدیده پس دهد. اگر نتواند پس بدهد، خود او را باید فروخت تا غرامت پرداخت شود.
4 In an sami dabbar, ko saniya, ko jaki, ko tunkiya da ya sata da rai a hannunsa, dole ɓarawon yă biya taran da za a ci shi, sau biyu na kowane ɗaya.
اگر کسی گاو یا الاغ یا گوسفندی بدزدد و آن حیوان در دست دزد زنده یافت شود، باید دو برابر قیمت حیوان غرامت پرداخت کند.
5 “In mutum ya sa dabbobinsa su yi kiwo a fili ko a gonar inabi, ya kuma bar dabbobinsa suka yi ɓarna a cikin gonar wani, sai a sa mai dabbar yă biya tara daga amfanin gonarsa mafi kyau duka.
«اگر کسی چارپایان خود را به داخل تاکستان شخص دیگری رها کند، و یا آنها را در مزرعهٔ شخص دیگری بچراند، باید از بهترین محصول خود، برابر خسارت وارده به صاحب تاکستان یا مزرعه غرامت بپردازد.
6 “In gobara ta tashi, ta kuma bazu cikin ƙayayyuwa, har ta cinye tarin hatsi, ko hatsin da ke tsaye, ko dukan gonar, dole wanda ya sa wutar, yă biya taran da aka yanka masa saboda ɓarnan da wutar ta yi.
«اگر کسی در مزرعه‌اش آتشی روشن کند و آتش به مزرعهٔ شخص دیگری سرایت نماید و بافه‌ها یا محصول درو نشده و یا تمام مزرعهٔ او را بسوزاند، آنکه آتش را افروخته است باید غرامت تمام خسارات وارده را بپردازد.
7 “In mutum ya ba maƙwabcinsa azurfa, ko kaya ajiya, aka kuma sace su daga gidan maƙwabcin, in an kama ɓarawon, sai ɓarawon yă biya abin da ya sata har sau biyu.
«اگر کسی پول یا شیئی را پیش شخصی به امانت گذارد تا از آن نگهداری کند، و آن امانت دزدیده شود، اگر دزد دستگیر شود باید دو برابر آنچه را که دزدیده است خسارت دهد.
8 Amma in ba a sami ɓarawon ba, sai wanda aka yi ajiyar a gidansa, yă bayyana a gaban alƙalai a bincika ko yana da hannu a kan kayan maƙwabcinsa.
ولی اگر دزد گرفتار نشود، آنگاه باید شخص امانتدار را نزد قضات ببرند تا معلوم شود آیا خود او در امانت خیانت کرده است یا نه.
9 A kowane rikicin cin amana da zai shiga tsakanin mutum biyu, ko a kan bijimi, ko jaki, ko tunkiya, ko riga, kai, ko a kan kowane irin abin da ya ɓata, da ma abin da aka samu a hannun wani, in akwai jayayya, za a kawo mutumin a gaban alƙalai. Wanda alƙali ya ce shi ne mai laifi, sai yă biya ɗayan taran da za a yanka, har sau biyu.
«هرگاه گاو، گوسفند، الاغ، لباس و یا هر چیز دیگری گم شود و صاحبش ادعا کند که گمشده‌اش پیش فلان شخص است، ولی آن شخص انکار کند، باید هر دو به حضور قضات بیایند و کسی که مقصر شناخته شد دو برابر مالی که دزدیده شده، تاوان دهد.
10 “In mutum ya ba da jaki, ko saniya, ko tunkiya, ko kowace dabba wa maƙwabcinsa ajiya, sai abin ya mutu, ko ya ji rauni, ko an ɗauke shi, in ba shaida,
«اگر کسی گاو یا الاغ یا گوسفند یا هر حیوان دیگری را به دست همسایه به امانت بسپارد و آن حیوان بمیرد، یا آسیب ببیند، و یا غارت شود بی‌آنکه شخصی ببیند،
11 rantsuwa ce za tă raba tsakaninsu a gaban Ubangiji cewa babu hannunsa a dukiyar maƙwabcinsa. Mai dukiyar kuwa zai yarda da rantsuwar, ba za a bukaci wanda aka bai wa amanar yă biya ba.
آنگاه آن همسایه باید به پیشگاه خداوند سوگند یاد کند که آن را ندزدیده است و صاحب مال باید سوگند او را بپذیرد و از گرفتن غرامت، خودداری کند.
12 Amma idan satan dabbar ce aka yi, dole wanda aka bai wa ajiyar yă biya mai dabbar taran da aka ci masa.
ولی اگر حیوان یا مال امانتی از نزد امانتدار دزدیده شود، امانتدار باید به صاحب مال غرامت دهد.
13 In naman jeji ne ya kashe ta, zai nuna gawar don shaida, ba za a kuwa sa maƙwabcin yă biya abin da naman jeji ya kashe ba.
اگر احیاناً جانوری وحشی آن را دریده باشد، شخص امانتدار باید لاشهٔ دریده شده را برای اثبات این امر نشان دهد، که در این صورت غرامت گرفته نمی‌شود.
14 “In mutum ya yi aron dabba daga wurin maƙwabcinsa, sai dabbar ta ji rauni ko ta mutu, yayinda mai shi ba ya nan, dole wanda ya yi aron dabbar yă biya.
«اگر کسی حیوانی را از همسایهٔ خود قرض بگیرد و آن حیوان آسیب ببیند یا کشته شود، البته باید غرامت بپردازد.
15 Amma idan mai dabbar yana a wurin, wanda ya karɓa aron, ba zai biya kome ba. In an yi hayar dabbar ce, to, kuɗin da aka biya na hayar zai zama a madadin rashin.
اما اگر صاحبش در آنجا حاضر بوده باشد، احتیاجی به پرداخت تاوان نیست. اگر حیوان کرایه شده باشد همان کرایه، غرامت را نیز شامل می‌شود.
16 “Idan mutum ya ruɗe budurwa, wadda ba wanda yake nemanta, ya kuma kwanta da ita, dole yă biya kuɗin aurenta, za tă kuma zama matarsa.
«اگر مردی، دوشیزه‌ای را که هنوز نامزد نشده اغفال کند، باید مهریهٔ او را پرداخته، وی را به عقد خود درآورد.
17 In mahaifinta ya ƙi yă ba da ita ga mutumin, dole mutumin yă biya dukiya daidai da abin da akan biya domin budurwai.
ولی اگر پدر دختر با این ازدواج راضی نباشد، آن مرد باید فقط مهریهٔ تعیین شده را به او بپردازد.
18 “Kada ku bar maiya da rai.
«زنی که جادوگری کند، باید کشته شود.
19 “Duk mutumin da ya yi jima’i da dabba dole a kashe shi.
«هر انسانی که با حیوانی نزدیکی نماید، باید کشته شود.
20 “Duk wanda ya yi hadaya ga wani allah ban da Ubangiji, dole a hallaka shi.
«اگر کسی برای خدایی دیگر، غیر از خداوند قربانی کند، باید کشته شود.
21 “Kada a wulaƙanta, ko a zalunci baƙo, domin dā ku baƙi ne a ƙasar Masar.
«به شخص غریب ظلم نکنید. به یاد آورید که شما نیز در سرزمین مصر غریب بودید.
22 “Kada ku ci zalin gwauruwa, ko maraya.
«از بیوه‌زن و یتیم بهره‌کشی نکنید.
23 In kuka yi haka, idan kuma suka yi kuka gare ni, zan ji kukansu.
اگر بر آنها ظلمی روا دارید و ایشان پیش من فریاد برآورند، من به داد آنها می‌رسم،
24 Zan husata, in kuma kashe ku da takobi; matanku kuma, su ma su zama gwauraye,’ya’yanku kuwa su zama marayu.
و بر شما خشمگین شده، شما را به شمشیر خواهم کشت تا زنان شما بیوه شوند و فرزندانتان یتیم گردند.
25 “In kun ba wa jama’ata matalauta da suke tsakaninku bashin kuɗi, kada ku zama kamar masu ba da rance; kada ku sa yă biya da ruwa.
«اگر به یکی از افراد قوم خود که محتاج باشد، پول قرض دادی، مثل یک رباخوار رفتار نکن و از او سود نگیر.
26 In kun ɗauki mayafi maƙwabcinku a matsayin jingina, ku mayar masa kafin fāɗuwar rana,
اگر لباس همسایه‌ات را گرو گرفتی، قبل از غروب آفتاب آن را به او پس بده،
27 domin mayafin ne abin da yake da shi na rufe jikinsa. To, da me zai rufu yă yi barci? Sa’ad da ya yi mini kuka, zan ji, gama ni mai tausayi ne.
چون ممکن است آن لباس تنها پوشش او برای خوابیدن باشد. اگر آن لباس را به او پس ندهی و او پیش من ناله کند من به داد او خواهم رسید، زیرا خدایی رئوف هستم.
28 “Kada ku yi maganar saɓo ga Allah, ko ku la’anta mai mulkin mutanenku.
«به خدا ناسزا نگو و به رهبران قوم خود لعنت نفرست.
29 “Kada ku jinkirta fitar da zakarku daga rumbunanku, ko harajin kayan da kuka saya. “Dole ku ba ni’ya’yan farinku maza.
«نوبر غلات و عصارۀ انگور خود را به موقع به حضور من بیاور. «پسران نخست‌زاده‌ات را به من تقدیم کن.
30 Ku yi haka da shanunku da tumakinku. Bari su kasance da iyayensu mata, har kwana bakwai, amma ku ba ni su a rana ta takwas.
«نخست‌زاده‌های نر گاوان و گوسفندان خود را به من بده. بگذار این نخست‌زاده‌ها یک هفته پیش مادرشان بمانند و در روز هشتم آنها را به من بده.
31 “Za ku kasance mutanena masu tsarki. Saboda kada ku ci naman da namun jeji suka kashe; ku jefa wa karnuka.
«شما قوم مقدّس من هستید، پس گوشت حیوانی را که به‌وسیله جانور وحشی دریده شده، نخورید؛ آن را نزد سگان بیندازید.

< Fitowa 22 >