< Fitowa 22 >
1 “In mutum ya saci saniya ko tunkiya ya yanka, ko ya sayar, zai biya shanu biyar, a maimakon saniyar da ya sata, ko kuma tumaki huɗu, maimakon tunkiyar da ya sata.
“Nxa umuntu angantshontsha inkabi kumbe imvu abeseyibulala kumbe ayithengise, kumele ahlawule ngenkomo ezinhlanu zokuhlawula inkabi, lezimvu ezine zokuhlawula imvu.
2 “In aka iske ɓarawo yana cikin ƙoƙarin shiga yă yi sata, aka buge shi har ya mutu, to, ba za a nemi alhakin jininsa daga wurin kowa ba;
Nxa isela lingafunyanwa ligqekeza ebusuku beselitshaywa life, lowo ozivikelayo kalacala lokuchitha igazi,
3 amma in ya faru bayan wayewar gari, to, za a nemi alhakin jinin ɓarawon a hannun wanda ya bugi ɓarawon. “Ɓarawon da aka kama da abin da ya sata, dole yă yi cikakkiyar ramuwa, amma in ba shi da kome, dole a sayar da shi a biya abin da ya sata.
kodwa kungenzeka ilanga selikhwelile uyabe elomlandu wokuchitha igazi. Isela kumele lihlawule sibili, kodwa nxa lingelalutho, kumele lithengiswe ukwenzela ukuthi lokhu kube yinhlawulo yokuntshontsha kwalo.
4 In an sami dabbar, ko saniya, ko jaki, ko tunkiya da ya sata da rai a hannunsa, dole ɓarawon yă biya taran da za a ci shi, sau biyu na kowane ɗaya.
Nxa isifuyo esintshontshiweyo singatholakala siphila ezandleni zesela, kungaba yinkabi kumbe ubabhemi loba imvu, kumele lihlawule okuphindwe kabili.
5 “In mutum ya sa dabbobinsa su yi kiwo a fili ko a gonar inabi, ya kuma bar dabbobinsa suka yi ɓarna a cikin gonar wani, sai a sa mai dabbar yă biya tara daga amfanin gonarsa mafi kyau duka.
Nxa umuntu angayadlisa izifuyo zakhe ensimini kumbe esivinini abeseziyekela zizihambela besezisiya kudla ensimini yeyinye indoda, kumele ahlawule ngezithelo ezinhle zensimu yakhe loba isivini sakhe.
6 “In gobara ta tashi, ta kuma bazu cikin ƙayayyuwa, har ta cinye tarin hatsi, ko hatsin da ke tsaye, ko dukan gonar, dole wanda ya sa wutar, yă biya taran da aka yanka masa saboda ɓarnan da wutar ta yi.
Nxa kuthungelwa umlilo ulumatha emeveni kuze kutshe lamahlanga amabele loba amabele angakavunwa loba insimu, othungele umlilo kumele ahlawule konke.
7 “In mutum ya ba maƙwabcinsa azurfa, ko kaya ajiya, aka kuma sace su daga gidan maƙwabcin, in an kama ɓarawon, sai ɓarawon yă biya abin da ya sata har sau biyu.
Nxa umuntu anganika umakhelwane wakhe isiliva kumbe impahla ukuba amgcinele izinto lezi besezintshontshwa endlini kamakhelwane, isela lingabanjwa kumele lihlawule okuphindwe kabili.
8 Amma in ba a sami ɓarawon ba, sai wanda aka yi ajiyar a gidansa, yă bayyana a gaban alƙalai a bincika ko yana da hannu a kan kayan maƙwabcinsa.
Kodwa nxa isela lingabanjwanga, umnikazi wendlu kumele ame phambi kwabahluleli ukuze kubonakale ingabe uke wabeka izandla empahleni zalowo omgcinisileyo na.
9 A kowane rikicin cin amana da zai shiga tsakanin mutum biyu, ko a kan bijimi, ko jaki, ko tunkiya, ko riga, kai, ko a kan kowane irin abin da ya ɓata, da ma abin da aka samu a hannun wani, in akwai jayayya, za a kawo mutumin a gaban alƙalai. Wanda alƙali ya ce shi ne mai laifi, sai yă biya ɗayan taran da za a yanka, har sau biyu.
Kuzozonke izehlakalo eziqondene lokugcina ngaphandle komthetho inkabi, ubabhemi, imvu, isigqoko kumbe yonke impahla elahlekileyo omunye umuntu angathi ngayo, ‘Lokhu ngokwami,’ wonke amacele womabili kumele alethe izindaba zawo phambi kwabahluleli. Lowo abahluleli abazakuthi ulecala kumele ahlawule okuphindwe kabili kumakhelwane wakhe.
10 “In mutum ya ba da jaki, ko saniya, ko tunkiya, ko kowace dabba wa maƙwabcinsa ajiya, sai abin ya mutu, ko ya ji rauni, ko an ɗauke shi, in ba shaida,
Nxa umuntu angasisela umakhelwane wakhe ubabhemi, inkabi, imvu kumbe esinye isifuyo ukuze kugcinakale besekusifa kumbe kulimale kumbe kuthathwe kungelamuntu okhangeleyo,
11 rantsuwa ce za tă raba tsakaninsu a gaban Ubangiji cewa babu hannunsa a dukiyar maƙwabcinsa. Mai dukiyar kuwa zai yarda da rantsuwar, ba za a bukaci wanda aka bai wa amanar yă biya ba.
udaba lwabantu laba luzaqedwa ngokufunga phambi kukaThixo ukuthi umakhelwane konanga impahla yomunye umuntu. Umnikazi kumele akwemukele lokhu njalo akulanhlawulo edingakalayo.
12 Amma idan satan dabbar ce aka yi, dole wanda aka bai wa ajiyar yă biya mai dabbar taran da aka ci masa.
Kodwa nxa isifuyo santshontshwa sikumasiselwa kumele ahlawule umnikazi.
13 In naman jeji ne ya kashe ta, zai nuna gawar don shaida, ba za a kuwa sa maƙwabcin yă biya abin da naman jeji ya kashe ba.
Nxa isifuyo sidatshudatshulwe yinyamazana yeganga saba yiziqa, uzaletha izicucu eziseleyo njengobufakazi njalo akusoze kudingakale ukuthi ahlawulele isifuyo esidatshudatshuliweyo.
14 “In mutum ya yi aron dabba daga wurin maƙwabcinsa, sai dabbar ta ji rauni ko ta mutu, yayinda mai shi ba ya nan, dole wanda ya yi aron dabbar yă biya.
Nxa umuntu angaboleka isifuyo kumakhelwane wakhe, besesilimala kumbe sife ngesikhathi umniniso engekho, kumele ahlawule.
15 Amma idan mai dabbar yana a wurin, wanda ya karɓa aron, ba zai biya kome ba. In an yi hayar dabbar ce, to, kuɗin da aka biya na hayar zai zama a madadin rashin.
Kodwa nxa umnikazi ekhona, lowo owasebolekayo akumelanga ahlawule. Nxa isifuyo siqhatshiwe, imali ehlawulwe ukusiqhatsha igoqela inhlawulo yokulahlekelwa.”
16 “Idan mutum ya ruɗe budurwa, wadda ba wanda yake nemanta, ya kuma kwanta da ita, dole yă biya kuɗin aurenta, za tă kuma zama matarsa.
“Nxa indoda ingaqila intombi egcweleyo engakathenjiswa ilale layo, kumele ikhuphe amalobolo, leyontombi ibe ngumkayo.
17 In mahaifinta ya ƙi yă ba da ita ga mutumin, dole mutumin yă biya dukiya daidai da abin da akan biya domin budurwai.
Nxa uyise esala kokuphela ukuthi ayendisele, kumele akhuphe inhlawulo ekhutshelwa amantombazana agcweleyo.
18 “Kada ku bar maiya da rai.
Lingavumeli umthakathi ukuthi aphile.
19 “Duk mutumin da ya yi jima’i da dabba dole a kashe shi.
Wonke umuntu olala lenyamazana kumele abulawe.
20 “Duk wanda ya yi hadaya ga wani allah ban da Ubangiji, dole a hallaka shi.
Loba ngubani onikela kwabanye onkulunkulu ngaphandle kukaThixo kumele abhujiswe.
21 “Kada a wulaƙanta, ko a zalunci baƙo, domin dā ku baƙi ne a ƙasar Masar.
Lingahlukuluzi owezizweni ngoba lani lalingabezizweni eGibhithe.
22 “Kada ku ci zalin gwauruwa, ko maraya.
Lingaqilibezeli umfelokazi kumbe intandane,
23 In kuka yi haka, idan kuma suka yi kuka gare ni, zan ji kukansu.
ngoba lingakwenza, besebekhala kimi ngizakuzwa ukukhala kwabo;
24 Zan husata, in kuma kashe ku da takobi; matanku kuma, su ma su zama gwauraye,’ya’yanku kuwa su zama marayu.
ulaka lwami luzavutha, ngibulale ngenkemba; abafazi benu babe ngabafelokazi labantwabenu babe zintandane.
25 “In kun ba wa jama’ata matalauta da suke tsakaninku bashin kuɗi, kada ku zama kamar masu ba da rance; kada ku sa yă biya da ruwa.
Nxa lingebolekisa imali omunye wabantu bami ohluphekayo phakathi kwenu, akumelanga lenze njengebhizimisi yokweboleka abanye imali, lingamhlawulisi inzuzo.
26 In kun ɗauki mayafi maƙwabcinku a matsayin jingina, ku mayar masa kafin fāɗuwar rana,
Nxa ungathatha ijazi likamakhelwane wakho ulenze isibambiso, kumele ulibuyisele ilanga lingakatshoni,
27 domin mayafin ne abin da yake da shi na rufe jikinsa. To, da me zai rufu yă yi barci? Sa’ad da ya yi mini kuka, zan ji, gama ni mai tausayi ne.
ngoba ijazi lelo yilo lodwa embesa ngalo ubunqunu bakhe. Kambe kuyini okunye abangalala kukho? Nxa bengakhala kimi, ngizabezwa ngoba ngilozwelo.
28 “Kada ku yi maganar saɓo ga Allah, ko ku la’anta mai mulkin mutanenku.
Lingahlambazi uNkulunkulu kumbe lithuke umbusi wabantu bakini.
29 “Kada ku jinkirta fitar da zakarku daga rumbunanku, ko harajin kayan da kuka saya. “Dole ku ba ni’ya’yan farinku maza.
Lingagodli iminikelo eziphaleni zenu loba ezimbizeni zewayini lenu. Kumele lilethe kimi amadodana enu angamazibulo.
30 Ku yi haka da shanunku da tumakinku. Bari su kasance da iyayensu mata, har kwana bakwai, amma ku ba ni su a rana ta takwas.
Yenzani njalo ngenkomo lezimvu zenu. Yekelani zihlale labonina okwensuku eziyisikhombisa kodwa linginike zona ngosuku lwesificaminwembili.
31 “Za ku kasance mutanena masu tsarki. Saboda kada ku ci naman da namun jeji suka kashe; ku jefa wa karnuka.
Lizakuba ngabantu bami abangcwele. Ngakho lingaze ladla inyama yenyamazana eyabe idatshudatshulwe yizilo zeganga; iphoseleni izinja.”