< Fitowa 22 >

1 “In mutum ya saci saniya ko tunkiya ya yanka, ko ya sayar, zai biya shanu biyar, a maimakon saniyar da ya sata, ko kuma tumaki huɗu, maimakon tunkiyar da ya sata.
Yahweh also said, “If someone steals a bull or a sheep, and then slaughters it [to sell it or to sacrifice it] or sells its [meat to someone else], he must pay five bulls for the bull [that he stole], and [he must pay] four sheep for the sheep [that he stole].
2 “In aka iske ɓarawo yana cikin ƙoƙarin shiga yă yi sata, aka buge shi har ya mutu, to, ba za a nemi alhakin jininsa daga wurin kowa ba;
If a thief is caught while he is breaking into someone else’s house [at night], if [the one who catches him] kills the thief, he is not guilty of murdering him.
3 amma in ya faru bayan wayewar gari, to, za a nemi alhakin jinin ɓarawon a hannun wanda ya bugi ɓarawon. “Ɓarawon da aka kama da abin da ya sata, dole yă yi cikakkiyar ramuwa, amma in ba shi da kome, dole a sayar da shi a biya abin da ya sata.
But if that happens during the daytime, [the one who killed the thief] is guilty of murdering him. The thief must pay for what he stole. If he has no [animals with which to pay for the one that he stole], he must be sold to [become someone’s else’s slave and the money must be used] to pay for what he stole.
4 In an sami dabbar, ko saniya, ko jaki, ko tunkiya da ya sata da rai a hannunsa, dole ɓarawon yă biya taran da za a ci shi, sau biyu na kowane ɗaya.
If the thief still has the animal when he is caught, whether it is a bull or a donkey or a sheep, and it is still alive, the thief must give back [the stolen animal as well as giving] two [additional] animals for each one that he stole.
5 “In mutum ya sa dabbobinsa su yi kiwo a fili ko a gonar inabi, ya kuma bar dabbobinsa suka yi ɓarna a cikin gonar wani, sai a sa mai dabbar yă biya tara daga amfanin gonarsa mafi kyau duka.
If someone allows his animals to (graze/eat the grass) in his field or in his vineyard, and if they stray away and eat the crops in another person’s field, the owner of the animals must pay [the owner of those crops] by giving him the best crops from his own field or vineyard.
6 “In gobara ta tashi, ta kuma bazu cikin ƙayayyuwa, har ta cinye tarin hatsi, ko hatsin da ke tsaye, ko dukan gonar, dole wanda ya sa wutar, yă biya taran da aka yanka masa saboda ɓarnan da wutar ta yi.
Suppose someone starts a fire in his own field, and the fire spreads through the grass and starts burning in someone else’s field, and the fire burns grain that is growing or grain that is already [cut and] stacked. Then the person who started the fire must pay completely for the damage.
7 “In mutum ya ba maƙwabcinsa azurfa, ko kaya ajiya, aka kuma sace su daga gidan maƙwabcin, in an kama ɓarawon, sai ɓarawon yă biya abin da ya sata har sau biyu.
Suppose someone gives to another person some money or other valuable goods and asks him to guard them [in his house for a while]. If those things are stolen from that person’s house, if the thief is caught, he must pay back twice [as much as he stole].
8 Amma in ba a sami ɓarawon ba, sai wanda aka yi ajiyar a gidansa, yă bayyana a gaban alƙalai a bincika ko yana da hannu a kan kayan maƙwabcinsa.
But if the thief is not caught, the owner of the house [from which the things were stolen] must stand before the judges, so that the judges can determine whether [the owner of the house] was the one who took the other man’s goods [and sold them to someone else].
9 A kowane rikicin cin amana da zai shiga tsakanin mutum biyu, ko a kan bijimi, ko jaki, ko tunkiya, ko riga, kai, ko a kan kowane irin abin da ya ɓata, da ma abin da aka samu a hannun wani, in akwai jayayya, za a kawo mutumin a gaban alƙalai. Wanda alƙali ya ce shi ne mai laifi, sai yă biya ɗayan taran da za a yanka, har sau biyu.
If two people argue about which one of them owns a bull or a donkey or a sheep or some clothing, or something else that has been lost, the two people who each claim/say that the item belongs to them must stand before the judges. The one whom the judges declare is lying must pay back [to the real owner] twice as many bulls or donkeys or sheep or pieces of clothing.
10 “In mutum ya ba da jaki, ko saniya, ko tunkiya, ko kowace dabba wa maƙwabcinsa ajiya, sai abin ya mutu, ko ya ji rauni, ko an ɗauke shi, in ba shaida,
Suppose someone gives his donkey or bull or sheep or some other animal to someone else and asks him to take care of it [for a while], and the animal dies or is injured or is stolen while no one is watching.
11 rantsuwa ce za tă raba tsakaninsu a gaban Ubangiji cewa babu hannunsa a dukiyar maƙwabcinsa. Mai dukiyar kuwa zai yarda da rantsuwar, ba za a bukaci wanda aka bai wa amanar yă biya ba.
Then the person [who was taking care of the animal] must (swear/solemnly declare), knowing that God is listening, that he did not steal the animal. If he did not steal it the owner of the animal must accept/believe that the other person is telling the truth, and the other person will not have to pay anything back to the owner.
12 Amma idan satan dabbar ce aka yi, dole wanda aka bai wa ajiyar yă biya mai dabbar taran da aka ci masa.
But if the animal was stolen [while he was supposed to be taking care of it], the man who promised to take care of it must pay back the owner for the animal.
13 In naman jeji ne ya kashe ta, zai nuna gawar don shaida, ba za a kuwa sa maƙwabcin yă biya abin da naman jeji ya kashe ba.
If [he says that] the animal was killed by wild animals, he must bring back the remains of the animal that was killed and show it to the animal’s owner. If he does that, he will not have to pay anything for the animal.
14 “In mutum ya yi aron dabba daga wurin maƙwabcinsa, sai dabbar ta ji rauni ko ta mutu, yayinda mai shi ba ya nan, dole wanda ya yi aron dabbar yă biya.
If someone borrows an animal, and if that animal is hurt or dies when its owner is not there, the one who borrowed it must pay the owner for the animal.
15 Amma idan mai dabbar yana a wurin, wanda ya karɓa aron, ba zai biya kome ba. In an yi hayar dabbar ce, to, kuɗin da aka biya na hayar zai zama a madadin rashin.
But if that happens when the owner of the animal is there, the one who borrowed it will not have to pay back anything. If the man who borrowed it only rented it, the money that he paid to rent it will be enough to pay for the animal [dying or being injured].”
16 “Idan mutum ya ruɗe budurwa, wadda ba wanda yake nemanta, ya kuma kwanta da ita, dole yă biya kuɗin aurenta, za tă kuma zama matarsa.
“If a man persuades a girl/woman to have sex with him, a girl/woman who (is a virgin/has never had sex with any man) and who is not engaged to be married, he must pay the bride price for her and marry her.
17 In mahaifinta ya ƙi yă ba da ita ga mutumin, dole mutumin yă biya dukiya daidai da abin da akan biya domin budurwai.
But if her father refuses to allow her to marry him, he must pay to the woman’s father the amount of money that is equal to the amount of bride price money that men pay for virgins.
18 “Kada ku bar maiya da rai.
You must execute any woman who (practices sorcery/is a shaman).
19 “Duk mutumin da ya yi jima’i da dabba dole a kashe shi.
You must execute any person who has sex with an animal.
20 “Duk wanda ya yi hadaya ga wani allah ban da Ubangiji, dole a hallaka shi.
You [must offer sacrifices] only to Yahweh. You must execute anyone who offers a sacrifice to any [other] god.
21 “Kada a wulaƙanta, ko a zalunci baƙo, domin dā ku baƙi ne a ƙasar Masar.
You must not mistreat a foreigner [who comes to live among you]. Do not forget that you were previously foreigners in Egypt.
22 “Kada ku ci zalin gwauruwa, ko maraya.
You must not mistreat any widow or any orphan.
23 In kuka yi haka, idan kuma suka yi kuka gare ni, zan ji kukansu.
If you mistreat them and they cry out to me [for help], I will hear them.
24 Zan husata, in kuma kashe ku da takobi; matanku kuma, su ma su zama gwauraye,’ya’yanku kuwa su zama marayu.
And I will be angry with you, and I will cause you to be killed in a war [MTY]. Your wives will become widows, and your children will no longer have fathers.
25 “In kun ba wa jama’ata matalauta da suke tsakaninku bashin kuɗi, kada ku zama kamar masu ba da rance; kada ku sa yă biya da ruwa.
If you lend money to any of my people who are poor, do not act like a moneylender and require him to pay interest on the money.
26 In kun ɗauki mayafi maƙwabcinku a matsayin jingina, ku mayar masa kafin fāɗuwar rana,
If he gives you his cloak to guarantee [that he will pay the money back], you must give the cloak back to him before the sun goes down,
27 domin mayafin ne abin da yake da shi na rufe jikinsa. To, da me zai rufu yă yi barci? Sa’ad da ya yi mini kuka, zan ji, gama ni mai tausayi ne.
because he needs it to keep him warm [during the night]. (That is the only covering that poor people have when they sleep at night./What else will he cover himself with during the night?) [RHQ] [If you do not act mercifully toward him by returning his cloak], when he cries out to me asking for my help, I will help him, because I [always act] mercifully.
28 “Kada ku yi maganar saɓo ga Allah, ko ku la’anta mai mulkin mutanenku.
Do not (revile/speak evil about) me, and do not (curse/ask me to do harmful things to) any ruler of your people.
29 “Kada ku jinkirta fitar da zakarku daga rumbunanku, ko harajin kayan da kuka saya. “Dole ku ba ni’ya’yan farinku maza.
(Do not withhold from/Give) me the best parts of the grain that you harvest and of the olive oil and the wine that you produce.
30 Ku yi haka da shanunku da tumakinku. Bari su kasance da iyayensu mata, har kwana bakwai, amma ku ba ni su a rana ta takwas.
You must dedicate your firstborn sons to me. Similarly, your firstborn [male] cattle and sheep belong to me. After those animals are born, allow them to stay with their mothers for seven days. On the eighth day, offer them to me [as a sacrifice].
31 “Za ku kasance mutanena masu tsarki. Saboda kada ku ci naman da namun jeji suka kashe; ku jefa wa karnuka.
You are people who are (completely dedicated to/set apart for) me. [And I detest] the meat of any animal that has been killed by wild animals. Therefore you should not eat such meat. Instead, throw it where the dogs [can eat it].”

< Fitowa 22 >