< Fitowa 22 >
1 “In mutum ya saci saniya ko tunkiya ya yanka, ko ya sayar, zai biya shanu biyar, a maimakon saniyar da ya sata, ko kuma tumaki huɗu, maimakon tunkiyar da ya sata.
“Tko ukrade goveče ili marvinče od sitne stoke, pa bilo da ga zakolje, bilo da ga proda, onda za jedno goveče neka se vrati petero goveda, a za malo marvinče četvero marvinčadi.
2 “In aka iske ɓarawo yana cikin ƙoƙarin shiga yă yi sata, aka buge shi har ya mutu, to, ba za a nemi alhakin jininsa daga wurin kowa ba;
Ako se lopov zateče gdje probija zid, pa mu se zada smrtan udarac, njegovu krv ne treba osvećivati.
3 amma in ya faru bayan wayewar gari, to, za a nemi alhakin jinin ɓarawon a hannun wanda ya bugi ɓarawon. “Ɓarawon da aka kama da abin da ya sata, dole yă yi cikakkiyar ramuwa, amma in ba shi da kome, dole a sayar da shi a biya abin da ya sata.
No ako je već izišlo sunce, njegovu krv treba osvetiti. Lopov mora štetu nadoknaditi. Ako nema ništa, njega za njegovu krađu treba prodati.
4 In an sami dabbar, ko saniya, ko jaki, ko tunkiya da ya sata da rai a hannunsa, dole ɓarawon yă biya taran da za a ci shi, sau biyu na kowane ɗaya.
Nađe li se ukradeno živinče živo u njegovu vlasništvu - goveče, magare ili koja glava sitne stoke - treba da ga plati dvostruko.”
5 “In mutum ya sa dabbobinsa su yi kiwo a fili ko a gonar inabi, ya kuma bar dabbobinsa suka yi ɓarna a cikin gonar wani, sai a sa mai dabbar yă biya tara daga amfanin gonarsa mafi kyau duka.
“Tko opustoši njivu ili vinograd pustivši svoju stoku da obrsti tuđe, neka nadoknadi onim što najbolje nađe na svojoj njivi i u svome vinogradu.
6 “In gobara ta tashi, ta kuma bazu cikin ƙayayyuwa, har ta cinye tarin hatsi, ko hatsin da ke tsaye, ko dukan gonar, dole wanda ya sa wutar, yă biya taran da aka yanka masa saboda ɓarnan da wutar ta yi.
Tko zapali vatru pa ona zahvati drač te izgori žito u snopu, u klasu ili na njivi, onaj tko je vatru zapalio mora štetu nadoknaditi.
7 “In mutum ya ba maƙwabcinsa azurfa, ko kaya ajiya, aka kuma sace su daga gidan maƙwabcin, in an kama ɓarawon, sai ɓarawon yă biya abin da ya sata har sau biyu.
Kad tko položi kod znanca novac ili stvari na čuvanje, pa budu pokradene iz njegove kuće, ako se lopov pronađe, mora dvostruko platiti.
8 Amma in ba a sami ɓarawon ba, sai wanda aka yi ajiyar a gidansa, yă bayyana a gaban alƙalai a bincika ko yana da hannu a kan kayan maƙwabcinsa.
Ako se lopov ne pronađe, vlasnik kuće neka se primakne k Bogu, da se dokaže kako on nije spustio svoje ruke na dobra svoga bližnjega.
9 A kowane rikicin cin amana da zai shiga tsakanin mutum biyu, ko a kan bijimi, ko jaki, ko tunkiya, ko riga, kai, ko a kan kowane irin abin da ya ɓata, da ma abin da aka samu a hannun wani, in akwai jayayya, za a kawo mutumin a gaban alƙalai. Wanda alƙali ya ce shi ne mai laifi, sai yă biya ɗayan taran da za a yanka, har sau biyu.
Za svaki prekršaj pronevjere - radilo se o govečetu, magaretu, sitnoj stoci, odjeći ili bilo kojoj izgubljenoj stvari za koju se ustvrdi: to je ono! - treba spor iznijeti pred Boga. Onaj koga Bog proglasi krivim neka plati dvostruko drugome.
10 “In mutum ya ba da jaki, ko saniya, ko tunkiya, ko kowace dabba wa maƙwabcinsa ajiya, sai abin ya mutu, ko ya ji rauni, ko an ɗauke shi, in ba shaida,
Kad tko povjeri svome susjedu magare, goveče, glavu sitne stoke ili bilo kakvo živinče, pa ono ugine, osakati se ili ga tko odvede a da ne bude svjedoka,
11 rantsuwa ce za tă raba tsakaninsu a gaban Ubangiji cewa babu hannunsa a dukiyar maƙwabcinsa. Mai dukiyar kuwa zai yarda da rantsuwar, ba za a bukaci wanda aka bai wa amanar yă biya ba.
zakletva pred Jahvom neka odluči među obojicom je li čuvar posegao za dobrom svoga bližnjega ili nije. Neka je vlasniku to dovoljno, a čuvar nije dužan da nadoknađuje.
12 Amma idan satan dabbar ce aka yi, dole wanda aka bai wa ajiyar yă biya mai dabbar taran da aka ci masa.
Nađe li se da je on ukrao, mora štetu nadoknaditi.
13 In naman jeji ne ya kashe ta, zai nuna gawar don shaida, ba za a kuwa sa maƙwabcin yă biya abin da naman jeji ya kashe ba.
Ako ga zvijer razdere, neka ga donese za dokaz, tako da za razderano ne daje odštete.
14 “In mutum ya yi aron dabba daga wurin maƙwabcinsa, sai dabbar ta ji rauni ko ta mutu, yayinda mai shi ba ya nan, dole wanda ya yi aron dabbar yă biya.
Kad tko posudi živinu na izor od svoga susjeda, pa se ona osakati ili ugine dok joj vlasnik nije bio s njom, neka plati odštetu.
15 Amma idan mai dabbar yana a wurin, wanda ya karɓa aron, ba zai biya kome ba. In an yi hayar dabbar ce, to, kuɗin da aka biya na hayar zai zama a madadin rashin.
Je li vlasnik bio s njom, odštete mu ne daje; ali ako je bila unajmljena na izor, neka dođe po svoju nadnicu.”
16 “Idan mutum ya ruɗe budurwa, wadda ba wanda yake nemanta, ya kuma kwanta da ita, dole yă biya kuɗin aurenta, za tă kuma zama matarsa.
“Ako tko zavede djevojku koja nije zaručena i s njom legne, neka za nju dadne ženidbenu procjenu i uzme je za ženu.
17 In mahaifinta ya ƙi yă ba da ita ga mutumin, dole mutumin yă biya dukiya daidai da abin da akan biya domin budurwai.
Ako njezin otac odbije da mu je dadne, zavodnik mora odmjeriti srebra u vrijednosti ženidbene procjene za djevojku.
18 “Kada ku bar maiya da rai.
Ne dopuštaj da vračarica živi!
19 “Duk mutumin da ya yi jima’i da dabba dole a kashe shi.
Tko bi god sa živinom legao, treba ga kazniti smrću.
20 “Duk wanda ya yi hadaya ga wani allah ban da Ubangiji, dole a hallaka shi.
Tko bi prinosio žrtve kojemu kumiru - osim Jahvi jedinom - neka bude izručen prokletstvu, potpuno uništen.
21 “Kada a wulaƙanta, ko a zalunci baƙo, domin dā ku baƙi ne a ƙasar Masar.
Ne tlači pridošlicu niti mu nanosi nepravde, jer ste i sami bili pridošlice u zemlji egipatskoj.
22 “Kada ku ci zalin gwauruwa, ko maraya.
Ne cvilite udovice i siročeta!
23 In kuka yi haka, idan kuma suka yi kuka gare ni, zan ji kukansu.
Ako ih ucviliš i oni zavape k meni, sigurno ću njihove vapaje uslišati.
24 Zan husata, in kuma kashe ku da takobi; matanku kuma, su ma su zama gwauraye,’ya’yanku kuwa su zama marayu.
Moj će se gnjev raspaliti i mačem ću vas pogubiti. Tako će vam žene ostati udovice a djeca siročad.
25 “In kun ba wa jama’ata matalauta da suke tsakaninku bashin kuɗi, kada ku zama kamar masu ba da rance; kada ku sa yă biya da ruwa.
Ako uzajmiš novca kome od moga naroda, siromahu koji je kod tebe, ne postupaj prema njemu kao lihvar! Ne nameći mu kamata!
26 In kun ɗauki mayafi maƙwabcinku a matsayin jingina, ku mayar masa kafin fāɗuwar rana,
Uzmeš li svome susjedu ogrtač u zalog, moraš mu ga vratiti prije zalaza sunca.
27 domin mayafin ne abin da yake da shi na rufe jikinsa. To, da me zai rufu yă yi barci? Sa’ad da ya yi mini kuka, zan ji, gama ni mai tausayi ne.
TÓa to mu je jedini pokrivač kojim omata svoje tijelo i u kojem može leći. Ako k meni zavapi, uslišat ću ga jer sam ja milostiv!
28 “Kada ku yi maganar saɓo ga Allah, ko ku la’anta mai mulkin mutanenku.
Ne huli Boga i ne psuj glavara svoga naroda.
29 “Kada ku jinkirta fitar da zakarku daga rumbunanku, ko harajin kayan da kuka saya. “Dole ku ba ni’ya’yan farinku maza.
Ne oklijevaj s prinosima od svoga obilja s gumna i od svoga mladog vina! Meni daj prvorođenca od svojih sinova.
30 Ku yi haka da shanunku da tumakinku. Bari su kasance da iyayensu mata, har kwana bakwai, amma ku ba ni su a rana ta takwas.
Isto učini sa svojim govedima i sitnom stokom: sedam dana neka ostane sa svojom majkom, a osmoga dana da si ga meni dao!
31 “Za ku kasance mutanena masu tsarki. Saboda kada ku ci naman da namun jeji suka kashe; ku jefa wa karnuka.
Budite narod meni posvećen! Zato nemojte jesti mesa od životinje koju je rastrgala zvjerad nego je bacite paščadi!”