< Fitowa 20 >

1 Sai Allah ya faɗi waɗannan kalmomi ya ce,
خدا با موسی سخن گفت و این احکام را صادر کرد:
2 “Ni ne Ubangiji Allahnka, wanda ya fitar da ku daga Masar, daga ƙasar bauta.
«من خداوند، خدای تو هستم، که تو را از اسارت و بندگی مصر آزاد کردم.
3 “Ba za ka yi wa kanka waɗansu alloli ba sai ni.
«تو را خدایان دیگر غیر از من نباشد.
4 Ba za ka yi wa kanka waɗansu alloli a siffar wani abu a sama a bisa, ko a ƙarƙashin ƙasa, ko a ƙarƙashin ruwa ba.
«هیچگونه بُتی به شکل آنچه بالا در آسمان و آنچه بر زمین و آنچه در دریاست برای خود درست نکن.
5 Ba za ka durƙusa gare su, ko ka yi musu sujada ba. Gama ni, Ubangiji Allahnka mai kishi ne, nakan hukunta’ya’ya har tsara ta uku da ta huɗu na waɗanda suke ƙina,
در برابر آنها زانو نزن و آنها را پرستش نکن، زیرا من که خداوند، خدای تو می‌باشم، خدای غیور هستم و کسانی را که با من دشمنی کنند، مجازات می‌کنم. این مجازات، شامل حال فرزندان آنها تا نسل سوم و چهارم نیز می‌گردد.
6 amma ina nuna ƙauna ga tsara dubbai na waɗanda suke ƙaunata, suke kuma kiyaye umarnaina.
اما بر کسانی که مرا دوست داشته باشند و دستورهای مرا پیروی کنند، تا هزار نسل رحمت می‌کنم.
7 Ba za ka yi amfani da sunan Ubangiji Allahnka a banza ba, gama Ubangiji zai hukunta duk wanda ya mai da sunansa banza.
«از نام من که خداوند، خدای تو هستم به ناشایستگی استفاده نکن. اگر نام مرا با بی‌احترامی به زبان بیاوری یا به آن قسم دروغ بخوری، تو را مجازات می‌کنم.
8 Ka tuna da ranar Asabbaci domin ka kiyaye ta da tsarki.
«روز شَبّات را به یاد داشته باش و آن را مقدّس بدار.
9 Kwana shida za ka yi dukan aikinka,
در هفته شش روز کار کن،
10 amma rana ta bakwai Asabbaci ne ga Ubangiji, Allahnka. A ranar ba za ka yi wani aiki ba, ko kai, ko ɗanka, ko’yarka, ko bawa, ko baiwa, ko dabbarka, ko baƙon da yake zama tare da kai.
ولی در روز هفتم که شَبّات یهوه خدای توست هیچ کار نکن، نه خودت، نه پسرت، نه دخترت، نه غلامت، نه کنیزت، نه مهمانانت و نه چارپایانت.
11 Gama kwana shida Ubangiji ya halicci sama da ƙasa, da teku, da duk abin da yake cikinsu, amma ya huta a rana ta bakwai. Saboda haka Ubangiji ya albarkaci ranar Asabbaci, ya kuma mai da ita mai tsarki.
چون خداوند در شش روز، آسمان و زمین و دریا و هر آنچه را که در آنهاست آفرید و روز هفتم دست از کار کشید. پس او روز شَبّات را مبارک خواند و آن را تقدیس کرد.
12 Ka girmama mahaifinka da mahaifiyarka, domin ka yi tsawon rai a ƙasar da Ubangiji Allahnka yake ba ka.
«پدر و مادر خود را گرامی بدار تا در سرزمینی که خداوند، خدای تو به تو خواهد بخشید، عمر طولانی داشته باشی.
13 Ba za ka yi kisankai ba.
«قتل نکن.
14 Ba za ka yi zina ba.
«زنا نکن.
15 Ba za ka yi sata ba.
«دزدی نکن.
16 Ba za ka ba da shaidar ƙarya a kan maƙwabcinka ba.
«بر همنوع خود شهادت دروغ نده.
17 Ba za ka yi ƙyashin gidan maƙwabcinka ba. Ba za ka yi ƙyashin matar maƙwabcinka ba, ko bawansa, ko baiwarsa, ko sansa, ko jakinsa, ko duk abin da yake na maƙwabcinka ba.”
«به خانۀ همسایه‌ات طمع نکن. به زن همسایه‌ات، یا غلام و کنیزش، یا گاو و الاغش، یا اموالش طمع نکن.»
18 Da mutane suka ga tsawa da walƙiya, suka ji karar ƙaho, suka kuma ga dutsen yana hayaƙi, sai suka yi rawar jiki don tsoro. Suka tsaya da nisa
وقتی قوم اسرائیل رعد و برق و بالا رفتن دود را از کوه دیدند و صدای شیپور را شنیدند، از ترس لرزیدند. آنها در فاصله‌ای دور از کوه ایستادند
19 suka ce wa Musa, “Ka yi magana da mu da kanka, za mu kasa kunne. Amma kada Allah ya yi mana magana, don kada mu mutu.”
و به موسی گفتند: «تو خود پیام خدا را بگیر و به ما برسان و ما خواهیم شنید. اما خدا مستقیم با ما صحبت نکند، چون می‌ترسیم بمیریم.»
20 Musa ya ce wa mutane, “Kada ku ji tsoro, gama Allah ya zo don yă gwada ku, don ku riƙa girmama shi, don kuma kada ku yi zunubi.”
موسی گفت: «نترسید، چون خدا برای این آمده است که شما را امتحان کند تا از این پس، از او بترسید و گناه نکنید.»
21 Sa’ad da mutane suka tsattsaya da nesa, sai Musa ya matsa kusa da girgije mai duhu, inda Allah yake.
در حالی که همهٔ قوم آنجا ایستاده بودند، دیدند که موسی به ظلمت غلیظی که خدا در آن بود، نزدیک شد.
22 Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka faɗa wa Isra’ilawa wannan. ‘Kun gani da kanku cewa na yi magana da ku daga sama.
آنگاه خداوند از موسی خواست تا به قوم اسرائیل چنین بگوید: «شما خود دیدید چگونه از آسمان با شما صحبت کردم،
23 Kada ku yi waɗansu alloli in ban da ni, kada ku yi wa kanku allolin azurfa ko na zinariya.
پس دیگر برای خود خدایانی از طلا و نقره نسازید و آنها را پرستش نکنید.
24 “‘Ku yi mini bagaden ƙasa, ku kuma miƙa mini hadaya ta ƙonawa da hadaya ta salama, za ku hadayar da tumakinku da awakinku da shanu. Duk inda na sa a girmama sunana, zan zo wurinku, in sa muku albarka.
«مذبحی که برای من می‌سازید باید از خاک زمین باشد. از گله و رمهٔ خود قربانیهای سوختنی و قربانیهای سلامتی روی این مذبح قربانی کنید. در جایی که من برای گرامیداشت نام خود تعیین می‌کنم، مذبح بسازید تا من آمده، شما را در آنجا برکت دهم.
25 In kuka yi mini bagade dutse, kada ku gina shi da sassaƙaƙƙun duwatsu, gama inda guduma ta taɓa duwatsun, sun haramtu ke nan.
اگر خواستید مذبح را از سنگ بنا کنید، سنگها را با ابزار نشکنید و نتراشید، چون سنگهایی که روی آنها ابزار به کار رفته باشد مناسب مذبح من نیستند.
26 Kada ku gina wa bagadena matakala, domin kada yayinda wani yana hawa, mutane su ga tsiraicinsa.’
برای مذبح، پله نگذارید مبادا وقتی از پله‌ها بالا می‌روید عریانی شما دیده شود.

< Fitowa 20 >