< Fitowa 20 >

1 Sai Allah ya faɗi waɗannan kalmomi ya ce,
Dieu prononça toutes ces paroles, en disant:
2 “Ni ne Ubangiji Allahnka, wanda ya fitar da ku daga Masar, daga ƙasar bauta.
« Je suis Yahvé, ton Dieu, qui t'ai fait sortir du pays d'Égypte, de la maison de servitude.
3 “Ba za ka yi wa kanka waɗansu alloli ba sai ni.
« Tu n'auras pas d'autres dieux devant moi.
4 Ba za ka yi wa kanka waɗansu alloli a siffar wani abu a sama a bisa, ko a ƙarƙashin ƙasa, ko a ƙarƙashin ruwa ba.
« Tu ne te feras pas d'idole, ni d'image de ce qui est dans les cieux en haut, sur la terre en bas, ou dans les eaux au-dessous de la terre;
5 Ba za ka durƙusa gare su, ko ka yi musu sujada ba. Gama ni, Ubangiji Allahnka mai kishi ne, nakan hukunta’ya’ya har tsara ta uku da ta huɗu na waɗanda suke ƙina,
tu ne te prosterneras pas devant elles et tu ne les serviras pas, car moi, Yahvé ton Dieu, je suis un Dieu jaloux, qui punit l'iniquité des pères sur les enfants, sur la troisième et la quatrième génération de ceux qui me haïssent,
6 amma ina nuna ƙauna ga tsara dubbai na waɗanda suke ƙaunata, suke kuma kiyaye umarnaina.
et qui fait preuve de bonté envers les milliers de ceux qui m'aiment et qui gardent mes commandements.
7 Ba za ka yi amfani da sunan Ubangiji Allahnka a banza ba, gama Ubangiji zai hukunta duk wanda ya mai da sunansa banza.
« Tu n'abuseras pas du nom de Yahvé ton Dieu, car Yahvé ne laisse pas impuni celui qui abuse de son nom.
8 Ka tuna da ranar Asabbaci domin ka kiyaye ta da tsarki.
« Souviens-toi du jour du sabbat, pour le sanctifier.
9 Kwana shida za ka yi dukan aikinka,
Tu travailleras six jours et tu feras tout ton ouvrage,
10 amma rana ta bakwai Asabbaci ne ga Ubangiji, Allahnka. A ranar ba za ka yi wani aiki ba, ko kai, ko ɗanka, ko’yarka, ko bawa, ko baiwa, ko dabbarka, ko baƙon da yake zama tare da kai.
mais le septième jour est un sabbat pour Yahvé, ton Dieu. Tu ne feras aucun ouvrage, ni toi, ni ton fils, ni ta fille, ni ton serviteur, ni ta servante, ni ton bétail, ni l'étranger qui sera dans tes portes.
11 Gama kwana shida Ubangiji ya halicci sama da ƙasa, da teku, da duk abin da yake cikinsu, amma ya huta a rana ta bakwai. Saboda haka Ubangiji ya albarkaci ranar Asabbaci, ya kuma mai da ita mai tsarki.
Car en six jours, Yahvé a fait le ciel et la terre, la mer et tout ce qui s'y trouve, et il s'est reposé le septième jour.
12 Ka girmama mahaifinka da mahaifiyarka, domin ka yi tsawon rai a ƙasar da Ubangiji Allahnka yake ba ka.
« Honore ton père et ta mère, afin que tes jours se prolongent dans le pays que Yahvé ton Dieu te donne.
13 Ba za ka yi kisankai ba.
« Tu ne commettras pas de meurtre.
14 Ba za ka yi zina ba.
« Tu ne commettras pas d'adultère.
15 Ba za ka yi sata ba.
« Tu ne voleras pas.
16 Ba za ka ba da shaidar ƙarya a kan maƙwabcinka ba.
« Tu ne porteras pas de faux témoignage contre ton prochain.
17 Ba za ka yi ƙyashin gidan maƙwabcinka ba. Ba za ka yi ƙyashin matar maƙwabcinka ba, ko bawansa, ko baiwarsa, ko sansa, ko jakinsa, ko duk abin da yake na maƙwabcinka ba.”
« Tu ne convoiteras pas la maison de ton prochain. Tu ne convoiteras pas la femme de ton prochain, ni son serviteur, ni sa servante, ni son bœuf, ni son âne, ni rien de ce qui appartient à ton prochain. »
18 Da mutane suka ga tsawa da walƙiya, suka ji karar ƙaho, suka kuma ga dutsen yana hayaƙi, sai suka yi rawar jiki don tsoro. Suka tsaya da nisa
Tout le peuple perçut les tonnerres, les éclairs, le son de la trompette et la montagne fumante. Quand le peuple vit cela, il trembla et resta à distance.
19 suka ce wa Musa, “Ka yi magana da mu da kanka, za mu kasa kunne. Amma kada Allah ya yi mana magana, don kada mu mutu.”
Ils dirent à Moïse: « Parle-nous toi-même, et nous écouterons; mais ne laisse pas Dieu nous parler, de peur que nous ne mourions. »
20 Musa ya ce wa mutane, “Kada ku ji tsoro, gama Allah ya zo don yă gwada ku, don ku riƙa girmama shi, don kuma kada ku yi zunubi.”
Moïse dit au peuple: « N'ayez pas peur, car Dieu est venu pour vous mettre à l'épreuve, et pour que sa crainte soit devant vous, afin que vous ne péchiez pas. »
21 Sa’ad da mutane suka tsattsaya da nesa, sai Musa ya matsa kusa da girgije mai duhu, inda Allah yake.
Le peuple resta à distance, et Moïse s'approcha de l'épaisse obscurité où se trouvait Dieu.
22 Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka faɗa wa Isra’ilawa wannan. ‘Kun gani da kanku cewa na yi magana da ku daga sama.
Yahvé dit à Moïse: « Voici ce que tu diras aux enfants d'Israël: « Vous avez vu vous-mêmes que je vous ai parlé depuis le ciel.
23 Kada ku yi waɗansu alloli in ban da ni, kada ku yi wa kanku allolin azurfa ko na zinariya.
Vous ne vous ferez certainement pas des dieux d'argent ou des dieux d'or pour être à côté de moi.
24 “‘Ku yi mini bagaden ƙasa, ku kuma miƙa mini hadaya ta ƙonawa da hadaya ta salama, za ku hadayar da tumakinku da awakinku da shanu. Duk inda na sa a girmama sunana, zan zo wurinku, in sa muku albarka.
Vous me ferez un autel de terre, et vous y sacrifierez vos holocaustes et vos sacrifices de prospérité, vos brebis et vos bœufs. En tout lieu où j'inscrirai mon nom, je viendrai vers vous et je vous bénirai.
25 In kuka yi mini bagade dutse, kada ku gina shi da sassaƙaƙƙun duwatsu, gama inda guduma ta taɓa duwatsun, sun haramtu ke nan.
Si tu me fais un autel de pierre, tu ne le construiras pas en pierres taillées, car si tu lèves ton outil dessus, tu le souilles.
26 Kada ku gina wa bagadena matakala, domin kada yayinda wani yana hawa, mutane su ga tsiraicinsa.’
Tu ne monteras pas par des marches vers mon autel, afin que ta nudité n'y soit pas exposée'.

< Fitowa 20 >