< Fitowa 20 >

1 Sai Allah ya faɗi waɗannan kalmomi ya ce,
God spoke all these words:
2 “Ni ne Ubangiji Allahnka, wanda ya fitar da ku daga Masar, daga ƙasar bauta.
“I am Yahweh your God, who brought you out of the land of Egypt, out of the house of slavery.
3 “Ba za ka yi wa kanka waɗansu alloli ba sai ni.
You must have no other gods before me.
4 Ba za ka yi wa kanka waɗansu alloli a siffar wani abu a sama a bisa, ko a ƙarƙashin ƙasa, ko a ƙarƙashin ruwa ba.
You must not make for yourself a carved figure nor the likeness of anything that is in heaven above, or that is in the earth beneath, or that is in the water below.
5 Ba za ka durƙusa gare su, ko ka yi musu sujada ba. Gama ni, Ubangiji Allahnka mai kishi ne, nakan hukunta’ya’ya har tsara ta uku da ta huɗu na waɗanda suke ƙina,
You must not bow down to them or worship them, for I, Yahweh your God, am a jealous God. I punish the ancestors' wickedness by bringing punishment on the descendants, to the third and the fourth generation of those who hate me.
6 amma ina nuna ƙauna ga tsara dubbai na waɗanda suke ƙaunata, suke kuma kiyaye umarnaina.
But I show covenant faithfulness to thousands of those who love me and keep my commandments.
7 Ba za ka yi amfani da sunan Ubangiji Allahnka a banza ba, gama Ubangiji zai hukunta duk wanda ya mai da sunansa banza.
You must not take the name of Yahweh your God, in vain, for I will not hold guiltless anyone who takes my name in vain.
8 Ka tuna da ranar Asabbaci domin ka kiyaye ta da tsarki.
Remember the Sabbath day, to set it apart to me.
9 Kwana shida za ka yi dukan aikinka,
You must labor and do all your work for six days.
10 amma rana ta bakwai Asabbaci ne ga Ubangiji, Allahnka. A ranar ba za ka yi wani aiki ba, ko kai, ko ɗanka, ko’yarka, ko bawa, ko baiwa, ko dabbarka, ko baƙon da yake zama tare da kai.
But the seventh day is a Sabbath for Yahweh your God. On it you must not do any work, you, or your son, or your daughter, or your male servant, or your female servant, or your cattle, or the foreigner who is within your gates.
11 Gama kwana shida Ubangiji ya halicci sama da ƙasa, da teku, da duk abin da yake cikinsu, amma ya huta a rana ta bakwai. Saboda haka Ubangiji ya albarkaci ranar Asabbaci, ya kuma mai da ita mai tsarki.
For in six days Yahweh made the heavens and earth, the sea, and everything that is in them, and rested on the seventh day. Therefore Yahweh blessed the Sabbath day and set it apart.
12 Ka girmama mahaifinka da mahaifiyarka, domin ka yi tsawon rai a ƙasar da Ubangiji Allahnka yake ba ka.
Honor your father and your mother, so that you may live a long time in the land that Yahweh your God is giving you.
13 Ba za ka yi kisankai ba.
You must not murder anyone.
14 Ba za ka yi zina ba.
You must not commit adultery.
15 Ba za ka yi sata ba.
You must not steal from anyone.
16 Ba za ka ba da shaidar ƙarya a kan maƙwabcinka ba.
You must not give false testimony against your neighbor.
17 Ba za ka yi ƙyashin gidan maƙwabcinka ba. Ba za ka yi ƙyashin matar maƙwabcinka ba, ko bawansa, ko baiwarsa, ko sansa, ko jakinsa, ko duk abin da yake na maƙwabcinka ba.”
You must not covet your neighbor's house; you must not covet your neighbor's wife, his male servant, his female servant, his ox, his donkey, or anything that belongs to your neighbor.”
18 Da mutane suka ga tsawa da walƙiya, suka ji karar ƙaho, suka kuma ga dutsen yana hayaƙi, sai suka yi rawar jiki don tsoro. Suka tsaya da nisa
All the people saw the thundering and the lightning, and heard the voice of the trumpet, and saw the mountain smoking. When the people saw it, they trembled and stood far off.
19 suka ce wa Musa, “Ka yi magana da mu da kanka, za mu kasa kunne. Amma kada Allah ya yi mana magana, don kada mu mutu.”
They said to Moses, “Speak to us, and we will listen; but do not let God speak to us, or we will die.”
20 Musa ya ce wa mutane, “Kada ku ji tsoro, gama Allah ya zo don yă gwada ku, don ku riƙa girmama shi, don kuma kada ku yi zunubi.”
Moses said to the people, “Do not be afraid, for God has come to test you so that the honor of him may be in you, and so that you do not sin.”
21 Sa’ad da mutane suka tsattsaya da nesa, sai Musa ya matsa kusa da girgije mai duhu, inda Allah yake.
So the people stood far off, and Moses approached the thick darkness where God was.
22 Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka faɗa wa Isra’ilawa wannan. ‘Kun gani da kanku cewa na yi magana da ku daga sama.
Yahweh said to Moses, “This is what you must tell the Israelites: 'You yourselves have seen that I have talked with you from heaven.
23 Kada ku yi waɗansu alloli in ban da ni, kada ku yi wa kanku allolin azurfa ko na zinariya.
You will not make for yourselves other gods alongside me, gods of silver or gods of gold.
24 “‘Ku yi mini bagaden ƙasa, ku kuma miƙa mini hadaya ta ƙonawa da hadaya ta salama, za ku hadayar da tumakinku da awakinku da shanu. Duk inda na sa a girmama sunana, zan zo wurinku, in sa muku albarka.
You must make an earthen altar for me, and you must sacrifice on it your burnt offerings, fellowship offerings, sheep, and oxen. In every place where I cause my name to be honored, I will come to you and bless you.
25 In kuka yi mini bagade dutse, kada ku gina shi da sassaƙaƙƙun duwatsu, gama inda guduma ta taɓa duwatsun, sun haramtu ke nan.
If you make me an altar of stone, you must not build it of cut stones, for if you use your tools on it, you will have defiled it.
26 Kada ku gina wa bagadena matakala, domin kada yayinda wani yana hawa, mutane su ga tsiraicinsa.’
You must not go up to my altar on steps, so that your nakedness is not exposed.'”

< Fitowa 20 >