< Fitowa 20 >
1 Sai Allah ya faɗi waɗannan kalmomi ya ce,
And God spoke all these words, saying,
2 “Ni ne Ubangiji Allahnka, wanda ya fitar da ku daga Masar, daga ƙasar bauta.
I am Jehovah thy God, who brought thee out of the land of Egypt, out of the house of bondage.
3 “Ba za ka yi wa kanka waɗansu alloli ba sai ni.
Thou shall have no other gods before me.
4 Ba za ka yi wa kanka waɗansu alloli a siffar wani abu a sama a bisa, ko a ƙarƙashin ƙasa, ko a ƙarƙashin ruwa ba.
Thou shall not make to thee a graven image, nor any likeness of anything that is in heaven above, or that is on the earth beneath, or that is in the water under the earth.
5 Ba za ka durƙusa gare su, ko ka yi musu sujada ba. Gama ni, Ubangiji Allahnka mai kishi ne, nakan hukunta’ya’ya har tsara ta uku da ta huɗu na waɗanda suke ƙina,
Thou shall not bow down thyself to them, nor serve them, for I, Jehovah thy God, am a jealous God, visiting the iniquity of the fathers upon the sons, upon the third and upon the fourth generation of those who hate me,
6 amma ina nuna ƙauna ga tsara dubbai na waɗanda suke ƙaunata, suke kuma kiyaye umarnaina.
and showing loving kindness to thousands of those who love me and keep my commandments.
7 Ba za ka yi amfani da sunan Ubangiji Allahnka a banza ba, gama Ubangiji zai hukunta duk wanda ya mai da sunansa banza.
Thou shall not take the name of Jehovah thy God in vain, for Jehovah will not hold him guiltless who takes his name in vain.
8 Ka tuna da ranar Asabbaci domin ka kiyaye ta da tsarki.
Remember the sabbath day, to keep it holy.
9 Kwana shida za ka yi dukan aikinka,
Six days thou shall labor, and do all thy work,
10 amma rana ta bakwai Asabbaci ne ga Ubangiji, Allahnka. A ranar ba za ka yi wani aiki ba, ko kai, ko ɗanka, ko’yarka, ko bawa, ko baiwa, ko dabbarka, ko baƙon da yake zama tare da kai.
but the seventh day is a sabbath to Jehovah thy God. Thou shall not do any work, thou, nor thy son, nor thy daughter, thy man-servant, nor thy maid-servant, nor thy cattle, nor thy stranger that is within thy gates,
11 Gama kwana shida Ubangiji ya halicci sama da ƙasa, da teku, da duk abin da yake cikinsu, amma ya huta a rana ta bakwai. Saboda haka Ubangiji ya albarkaci ranar Asabbaci, ya kuma mai da ita mai tsarki.
for in six days Jehovah made heaven and earth, the sea, and all that is in them, and rested the seventh day. Therefore Jehovah blessed the sabbath day, and hallowed it.
12 Ka girmama mahaifinka da mahaifiyarka, domin ka yi tsawon rai a ƙasar da Ubangiji Allahnka yake ba ka.
Honor thy father and thy mother, that thy days may be long in the land which Jehovah thy God gives thee.
13 Ba za ka yi kisankai ba.
Thou shall not murder.
Thou shall not commit adultery.
16 Ba za ka ba da shaidar ƙarya a kan maƙwabcinka ba.
Thou shall not bear false witness against thy neighbor.
17 Ba za ka yi ƙyashin gidan maƙwabcinka ba. Ba za ka yi ƙyashin matar maƙwabcinka ba, ko bawansa, ko baiwarsa, ko sansa, ko jakinsa, ko duk abin da yake na maƙwabcinka ba.”
Thou shall not covet thy neighbor's house. Thou shall not covet thy neighbor's wife, nor his man-servant, nor his maid-servant, nor his ox, nor his donkey, nor anything that is thy neighbor's.
18 Da mutane suka ga tsawa da walƙiya, suka ji karar ƙaho, suka kuma ga dutsen yana hayaƙi, sai suka yi rawar jiki don tsoro. Suka tsaya da nisa
And all the people perceived the thunderings, and the lightnings, and the voice of the trumpet, and the mountain smoking. And when the people saw it, they trembled, and stood afar off.
19 suka ce wa Musa, “Ka yi magana da mu da kanka, za mu kasa kunne. Amma kada Allah ya yi mana magana, don kada mu mutu.”
And they said to Moses, Speak thou with us, and we will hear, but let not God speak with us, lest we die.
20 Musa ya ce wa mutane, “Kada ku ji tsoro, gama Allah ya zo don yă gwada ku, don ku riƙa girmama shi, don kuma kada ku yi zunubi.”
And Moses said to the people, Fear not, for God has come to prove you, and that his fear may be before you, that ye not sin.
21 Sa’ad da mutane suka tsattsaya da nesa, sai Musa ya matsa kusa da girgije mai duhu, inda Allah yake.
And the people stood afar off, and Moses drew near to the thick darkness where God was.
22 Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka faɗa wa Isra’ilawa wannan. ‘Kun gani da kanku cewa na yi magana da ku daga sama.
And Jehovah said to Moses, Thus thou shall say to the sons of Israel, Ye yourselves have seen that I have talked with you from heaven.
23 Kada ku yi waɗansu alloli in ban da ni, kada ku yi wa kanku allolin azurfa ko na zinariya.
Ye shall not make other gods with me; gods of silver, or gods of gold, ye shall not make to you.
24 “‘Ku yi mini bagaden ƙasa, ku kuma miƙa mini hadaya ta ƙonawa da hadaya ta salama, za ku hadayar da tumakinku da awakinku da shanu. Duk inda na sa a girmama sunana, zan zo wurinku, in sa muku albarka.
An altar of earth thou shall make to me, and shall sacrifice on it thy burnt offerings, and thy peace offerings, thy sheep, and thine oxen. In every place where I record my name I will come to thee and I will bless thee.
25 In kuka yi mini bagade dutse, kada ku gina shi da sassaƙaƙƙun duwatsu, gama inda guduma ta taɓa duwatsun, sun haramtu ke nan.
And if thou make to me an altar of stone, thou shall not build it of hewn stones, for if thou lift up thy tool upon it, thou have polluted it.
26 Kada ku gina wa bagadena matakala, domin kada yayinda wani yana hawa, mutane su ga tsiraicinsa.’
Neither shall thou go up by steps to my altar, that thy nakedness be not uncovered on it.