< Fitowa 20 >

1 Sai Allah ya faɗi waɗannan kalmomi ya ce,
I mluvil Bůh všecka slova tato, řka:
2 “Ni ne Ubangiji Allahnka, wanda ya fitar da ku daga Masar, daga ƙasar bauta.
Já jsem Hospodin Bůh tvůj, kterýž jsem tě vyvedl z země Egyptské, z domu služby.
3 “Ba za ka yi wa kanka waɗansu alloli ba sai ni.
Nebudeš míti bohů jiných přede mnou.
4 Ba za ka yi wa kanka waɗansu alloli a siffar wani abu a sama a bisa, ko a ƙarƙashin ƙasa, ko a ƙarƙashin ruwa ba.
Neučiníš sobě rytiny, ani jakého podobenství těch věcí, kteréž jsou na nebi svrchu, ani těch, kteréž na zemi dole, ani těch, kteréž u vodách pod zemí.
5 Ba za ka durƙusa gare su, ko ka yi musu sujada ba. Gama ni, Ubangiji Allahnka mai kishi ne, nakan hukunta’ya’ya har tsara ta uku da ta huɗu na waɗanda suke ƙina,
Nebudeš se jim klaněti, ani jich ctíti. Nebo já jsem Hospodin Bůh tvůj, Bůh silný, horlivý, navštěvující nepravost otců na synech do třetího i čtvrtého pokolení těch, kteříž nenávidí mne,
6 amma ina nuna ƙauna ga tsara dubbai na waɗanda suke ƙaunata, suke kuma kiyaye umarnaina.
A činící milosrdenství nad tisíci těmi, kteříž mne milují, a ostříhají přikázaní mých.
7 Ba za ka yi amfani da sunan Ubangiji Allahnka a banza ba, gama Ubangiji zai hukunta duk wanda ya mai da sunansa banza.
Nevezmeš jména Hospodina Boha svého nadarmo; neboť nenechá bez pomsty Hospodin toho, kdož by bral jméno jeho nadarmo.
8 Ka tuna da ranar Asabbaci domin ka kiyaye ta da tsarki.
Pomni na den sobotní, abys jej světil.
9 Kwana shida za ka yi dukan aikinka,
Šest dní pracovati budeš, a dělati všeliké dílo své;
10 amma rana ta bakwai Asabbaci ne ga Ubangiji, Allahnka. A ranar ba za ka yi wani aiki ba, ko kai, ko ɗanka, ko’yarka, ko bawa, ko baiwa, ko dabbarka, ko baƙon da yake zama tare da kai.
Ale dne sedmého odpočinutí jest Hospodina Boha tvého. Nebudeš dělati žádného díla, ty i syn tvůj i dcera tvá, služebník tvůj i děvka tvá, hovado tvé i příchozí, kterýž jest v branách tvých.
11 Gama kwana shida Ubangiji ya halicci sama da ƙasa, da teku, da duk abin da yake cikinsu, amma ya huta a rana ta bakwai. Saboda haka Ubangiji ya albarkaci ranar Asabbaci, ya kuma mai da ita mai tsarki.
Nebo v šesti dnech učinil Hospodin nebe a zemi, moře a všecko, což v nich jest, a odpočinul dne sedmého; protož požehnal Hospodin dne sobotního, a posvětil ho.
12 Ka girmama mahaifinka da mahaifiyarka, domin ka yi tsawon rai a ƙasar da Ubangiji Allahnka yake ba ka.
Cti otce svého i matku svou, ať se prodlejí dnové tvoji na zemi, kterouž Hospodin Bůh tvůj dá tobě.
13 Ba za ka yi kisankai ba.
Nezabiješ.
14 Ba za ka yi zina ba.
Nesesmilníš.
15 Ba za ka yi sata ba.
Nepokradeš.
16 Ba za ka ba da shaidar ƙarya a kan maƙwabcinka ba.
Nepromluvíš proti bližnímu svému křivého svědectví.
17 Ba za ka yi ƙyashin gidan maƙwabcinka ba. Ba za ka yi ƙyashin matar maƙwabcinka ba, ko bawansa, ko baiwarsa, ko sansa, ko jakinsa, ko duk abin da yake na maƙwabcinka ba.”
Nepožádáš domu bližního svého, aniž požádáš manželky bližního svého, ani služebníka jeho, ani děvky jeho, ani vola jeho, ani osla jeho, ani cožkoli jest bližního tvého.
18 Da mutane suka ga tsawa da walƙiya, suka ji karar ƙaho, suka kuma ga dutsen yana hayaƙi, sai suka yi rawar jiki don tsoro. Suka tsaya da nisa
Veškeren pak lid viděl hřímání to a blýskání, a zvuk trouby, a horu kouřící se. To když viděl lid, pohnuli se a stáli zdaleka.
19 suka ce wa Musa, “Ka yi magana da mu da kanka, za mu kasa kunne. Amma kada Allah ya yi mana magana, don kada mu mutu.”
A řekli Mojžíšovi: Mluv ty s námi, a poslouchati budeme; a nechť nemluví s námi Bůh, abychom nezemřeli.
20 Musa ya ce wa mutane, “Kada ku ji tsoro, gama Allah ya zo don yă gwada ku, don ku riƙa girmama shi, don kuma kada ku yi zunubi.”
Odpověděl Mojžíš lidu: Nebojte se; nebo pro zkušení vás sám Bůh přišel, aby bázeň jeho byla mezi vámi, abyste nehřešili.
21 Sa’ad da mutane suka tsattsaya da nesa, sai Musa ya matsa kusa da girgije mai duhu, inda Allah yake.
Tedy stál lid zdaleka; Mojžíš pak přistoupil k mrákotě, kdež byl Bůh.
22 Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka faɗa wa Isra’ilawa wannan. ‘Kun gani da kanku cewa na yi magana da ku daga sama.
I řekl Hospodin Mojžíšovi: Tak povíš synům Izraelským: Vy jste sami viděli, že s nebe mluvil jsem s vámi.
23 Kada ku yi waɗansu alloli in ban da ni, kada ku yi wa kanku allolin azurfa ko na zinariya.
Protož nevyzdvihujte ničehož ku poctě se mnou; bohů stříbrných a bohů zlatých neučiníte sobě.
24 “‘Ku yi mini bagaden ƙasa, ku kuma miƙa mini hadaya ta ƙonawa da hadaya ta salama, za ku hadayar da tumakinku da awakinku da shanu. Duk inda na sa a girmama sunana, zan zo wurinku, in sa muku albarka.
Oltář z země uděláš mi a obětovati budeš na něm zápaly své, a pokojné oběti své, ovce své a voly své. Na kterémkoli místě rozkáži slaviti památku jména svého, přijdu k tobě a požehnám tobě.
25 In kuka yi mini bagade dutse, kada ku gina shi da sassaƙaƙƙun duwatsu, gama inda guduma ta taɓa duwatsun, sun haramtu ke nan.
Jestliže mi pak vzděláš oltář kamenný, nedělej ho z kamene tesaného; nebo jestliže pozdvihneš železa na něj, poškvrníš ho.
26 Kada ku gina wa bagadena matakala, domin kada yayinda wani yana hawa, mutane su ga tsiraicinsa.’
Aniž po stupních vstupovati budeš k oltáři mému, aby hanba tvá u něho odkryta nebyla.

< Fitowa 20 >