< Fitowa 2 >

1 Ana nan, sai wani Balawe ya auri wata Balawiya,
Odšel je mož iz Lévijeve hiše in za ženo vzel Lévijevo hčer.
2 ta kuwa yi ciki, ta haifi ɗa. Sa’ad da ta ga jaririn kyakkyawa ne, sai ta ɓoye shi har watanni uku.
Ženska je spočela in rodila sina in ko je videla, da je bil čeden otrok, ga je skrivala tri mesece.
3 Amma da ba tă iya ɓoye shi kuma ba, sai ta yi kwandon kyauro ta shafa masa kwalta. Bayan haka sai ta sa jaririn a cikin kwandon, ta je ta ajiye kwandon tare da jaririn a cikin kyauro, a bakin kogin.
Ko pa ga ni mogla več skrivati, je zanj vzela pletenico iz ločja, jo namazala z blatom in s smolo in vanjo položila otroka in to položila v rogoz poleg rečnega brega.
4 ’Yar’uwarsa ta tsaya da ɗan rata tana lura da abin da zai faru da shi.
Njegova sestra pa je stala daleč stran, da izve kaj se bo z njim zgodilo.
5 Sai’yar Fir’auna ta gangara zuwa kogi domin tă yi wanka, bayinta kuwa suna tafiya a bakin kogi. Sai ta ga kwandon a ciyawa, ta aiki ɗaya daga cikin masu hidimarta tă ɗauko mata.
In dol je prišla faraonova hči, da se pri reki umije, njene služabnice pa so hodile vzdolž rečnega brega in ko je med rogozom zagledala pletenico, je poslala svojo služabnico, da odide ponjo.
6 Da ta buɗe kwandon, sai ta ga yaro yana kuka, ta kuwa ji tausayinsa. Ta ce, “Wannan ɗaya daga cikin jariran Ibraniyawa ne.”
Ko jo je ta odprla, je zagledala otroka in glej, dojenček je jokal. Do njega je imela sočutje ter rekla: »To je eden izmed hebrejskih otrok.«
7 Sai’yar’uwarsa ta tambayi’yar Fir’auna, ta ce, “In tafi in samo ɗaya daga cikin matan Ibraniyawa tă yi miki renon yaron?”
Potem je njegova sestra rekla faraonovi hčeri: »Ali naj grem in k tebi pokličem dojiljo izmed hebrejskih žensk, da bo lahko otroka dojila zate?«
8 Sai ta amsa ta ce, “I, tafi.” Sai yarinyar ta tafi ta kawo mahaifiyar yaron.
Faraonova hči ji je rekla: »Pojdi.« Deklica je odšla in poklicala otrokovo mater.
9 Diyar Fir’auna ta ce mata, “Ɗauki jaririn, ki yi mini renonsa, zan kuwa biya ki.” Saboda haka ta ɗauki yaron, ta yi renonsa.
Faraonova hči ji je rekla: »Odnesi tega otroka proč in ga dôji zame, jaz pa ti bom dajala tvoja plačila.« In ženska je vzela otroka ter ga dojila.
10 Sa’ad da ya yi girma, sai ta kawo shi wajen’yar Fir’auna, ya kuwa zama ɗanta, ta kuma ba shi suna Musa, tana cewa, “Na tsamo shi daga ruwa.”
Otrok je zrastel in privedla ga je k faraonovi hčeri in ta je postal njen sin. Njegovo ime je imenovala Mojzes. Rekla je: »Ker sem ga potegnila iz vode.«
11 Wata rana, bayan Musa ya yi girma, sai ya haura, ya tafi inda mutanensa suke, ya kuma ga yadda suke shan wahala da aiki. Ya ga wani mutumin Masar yana dūkan mutumin Ibraniyawa, ɗaya daga cikin mutanensa.
Pripetilo se je v tistih dneh, ko je Mojzes odrasel, da je odšel k svojim bratom, gledal na njihova bremena in oprezal za Egipčanom, ki je udarjal Hebrejca, enega izmed njegovih bratov.
12 Da ya leƙa nan da can bai kuwa ga kowa ba, sai ya kashe mutumin Masar, ya ɓoye shi a yashi.
Pogledal je to pot in tisto pot in ko je videl, da tam ni bilo nobenega človeka, je Egipčana usmrtil in ga skril v pesek.
13 Kashegari ya fita, sai ya ga Ibraniyawa biyu suna faɗa. Ya tambayi mai laifin ya ce, “Don me kake bugun ɗan’uwanka, mutumin Ibraniyawa?”
Ko je drug dan odšel ven, glej, dva moža izmed Hebrejcev sta se skupaj prepirala in temu, ki je storil napačno, je rekel: »Čemu udarjaš svojega rojaka?«
14 Mutumin ya ce masa, “Wa ya mai da kai mai mulki da mai hukunci a kanmu? Kana so ne ka kashe ni kamar yadda ka kashe mutumin Masar nan?” Sai Musa ya tsorata, ya yi tunani ya ce, “To, fa, abin nan da na yi, ya zama sananne.”
Ta pa je rekel: »Kdo te je naredil princa in sodnika nad nama? Ali me nameravaš ubiti, kakor si ubil Egipčana?« Mojzes se je zbal ter rekel: »Ta stvar se je zagotovo izvedela.«
15 Da Fir’auna ya ji wannan, sai ya yi ƙoƙari yă kashe Musa, amma Musa ya gudu daga wajen Fir’auna, ya tafi ƙasar Midiyan inda ya zauna kusa da wata rijiya.
Torej, ko je faraon slišal to stvar, je iskal Mojzesa, da ga ubije. Mojzes pa je pobegnil izpred faraonovega obličja in prebival v midjánski deželi in se usedel poleg vodnjaka.
16 To, fa, akwai wani firist na Midiyan, yana da’ya’ya mata bakwai, suka zo su shayar da dabbobin mahaifinsu.
Torej duhovnik iz Midjána je imel sedem hčera in prišle so, zajele vodo in napolnile korita, da bi napojile trop svojega očeta.
17 Sai waɗansu makiyaya suka zo suka kore su, amma Musa ya tashi ya taimake su ya shayar da dabbobinsu.
Prišli pa so pastirji ter jih odgnali proč, toda Mojzes je vstal, jim pomagal in napojil njihov trop.
18 Da’yan matan suka komo wurin Reyuwel mahaifinsu, sai ya tambaye su ya ce, “Yaya kuka dawo da wuri yau?”
Ko so prišle k svojemu očetu Reguélu, je rekel: »Kako je to, da ste danes prišle tako zgodaj?«
19 Suka amsa suka ce, “Wani mutumin Masar ne ya taimake mu daga hannun waɗansu makiyaya. Har ma ya ɗebo ruwa ya shayar da dabbobin.”
Rekle so: »Egipčan nas je osvobodil iz roke pastirjev in nam prav tako zajel dovolj vode in napojil trop.«
20 Ya tambayi’yan matansa, “To ina yake? Don me kuka bar shi a can? A gayyace shi, yă zo, yă ci wani abu.”
Svojim hčeram je rekel: »In kje je? Zakaj je to, da ste človeka pustile? Pokličite ga, da bo lahko jedel kruh.«
21 Musa ya yarda yă zauna da mutumin wanda ya ba da’yarsa Ziffora aure da Musa.
Mojzes je bil zadovoljen, da prebiva s človekom in ta je Mojzesu dal svojo hčer Cipóro.
22 Ziffora ta haifi wa Musa ɗa, ya kuma raɗa masa suna Gershom cewa, “Na zama baƙo a baƙuwar ƙasa.”
Rodila mu je sina in njegovo ime je imenoval Geršóm, kajti rekel je: »Tujec sem bil v tuji deželi.«
23 Ana nan dai, a kwana a tashi, sai sarkin Masar ya mutu. Isra’ilawa suka yi kuka mai zafi saboda bautarsu mai wuya, sai kukar neman taimakonsu saboda bauta, ya kai wurin Allah.
Pripetilo se je tekom časa, da je egiptovski kralj umrl, Izraelovi otroci pa so vzdihovali zaradi razloga suženjstva in vpili in njihovo vpitje je zaradi razloga suženjstva prišlo do Boga.
24 Allah kuwa ya ji kukansu sai ya tuna da alkawarinsa da Ibrahim da Ishaku da Yaƙub.
Bog je slišal njihovo stokanje in Bog se je spomnil svoje zaveze z Abrahamom, Izakom in Jakobom.
25 Sai Allah ya dubi Isra’ilawa, ya kuma damu da su.
Bog je pogledal na Izraelove otroke in Bog je imel do njih spoštovanje.

< Fitowa 2 >