< Fitowa 2 >

1 Ana nan, sai wani Balawe ya auri wata Balawiya,
Så var det en mann av Levis hus som gikk bort og tok en Levis datter til ekte.
2 ta kuwa yi ciki, ta haifi ɗa. Sa’ad da ta ga jaririn kyakkyawa ne, sai ta ɓoye shi har watanni uku.
Og kvinnen blev fruktsommelig og fødte en sønn; og da hun så at det var et vakkert barn, skjulte hun ham i tre måneder.
3 Amma da ba tă iya ɓoye shi kuma ba, sai ta yi kwandon kyauro ta shafa masa kwalta. Bayan haka sai ta sa jaririn a cikin kwandon, ta je ta ajiye kwandon tare da jaririn a cikin kyauro, a bakin kogin.
Men da hun ikke lenger kunne skjule ham, tok hun en kiste til ham av rør og smurte den over med jordbek og tjære, og hun la gutten i den og satte den i sivet ved elvebredden.
4 ’Yar’uwarsa ta tsaya da ɗan rata tana lura da abin da zai faru da shi.
Men hans søster stod et stykke fra for å få vite hvorledes det gikk ham.
5 Sai’yar Fir’auna ta gangara zuwa kogi domin tă yi wanka, bayinta kuwa suna tafiya a bakin kogi. Sai ta ga kwandon a ciyawa, ta aiki ɗaya daga cikin masu hidimarta tă ɗauko mata.
Da kom Faraos datter ned til elven for å bade sig, mens hennes jomfruer gikk frem og tilbake på elvebredden; hun fikk se kisten midt i sivet og sendte sin pike avsted og lot den hente.
6 Da ta buɗe kwandon, sai ta ga yaro yana kuka, ta kuwa ji tausayinsa. Ta ce, “Wannan ɗaya daga cikin jariran Ibraniyawa ne.”
Da hun åpnet den, så hun barnet, og se, det var en gutt som lå der og gråt; da ynkedes hun over ham og sa: Det er en av hebreernes guttebarn.
7 Sai’yar’uwarsa ta tambayi’yar Fir’auna, ta ce, “In tafi in samo ɗaya daga cikin matan Ibraniyawa tă yi miki renon yaron?”
Da sa hans søster til Faraos datter: Skal jeg gå og hente en amme til dig blandt de hebraiske kvinner, så hun kan fostre op barnet for dig?
8 Sai ta amsa ta ce, “I, tafi.” Sai yarinyar ta tafi ta kawo mahaifiyar yaron.
Faraos datter svarte henne: Ja, gå! Og piken gikk og hentet guttens mor.
9 Diyar Fir’auna ta ce mata, “Ɗauki jaririn, ki yi mini renonsa, zan kuwa biya ki.” Saboda haka ta ɗauki yaron, ta yi renonsa.
Da sa Faraos datter til henne: Ta denne gutt og fostre ham op for mig; jeg vil gi dig lønn for det. Og konen tok gutten og fostret ham op.
10 Sa’ad da ya yi girma, sai ta kawo shi wajen’yar Fir’auna, ya kuwa zama ɗanta, ta kuma ba shi suna Musa, tana cewa, “Na tsamo shi daga ruwa.”
Da gutten blev voksen, gikk hun med ham til Faraos datter, og han blev som en sønn for henne; hun kalte ham Moses, for - sa hun - av vannet har jeg dradd ham op.
11 Wata rana, bayan Musa ya yi girma, sai ya haura, ya tafi inda mutanensa suke, ya kuma ga yadda suke shan wahala da aiki. Ya ga wani mutumin Masar yana dūkan mutumin Ibraniyawa, ɗaya daga cikin mutanensa.
Og det hendte på den tid da Moses var blitt voksen, at han gikk ut til sine brødre og så på deres slit og slep, og han fikk se en egyptisk mann som slo en hebraisk mann, en av hans brødre.
12 Da ya leƙa nan da can bai kuwa ga kowa ba, sai ya kashe mutumin Masar, ya ɓoye shi a yashi.
Da vendte han sig hit og dit og så at det ikke var nogen der, og så slo han egypteren ihjel og skjulte ham i sanden.
13 Kashegari ya fita, sai ya ga Ibraniyawa biyu suna faɗa. Ya tambayi mai laifin ya ce, “Don me kake bugun ɗan’uwanka, mutumin Ibraniyawa?”
Den andre dag gikk han atter ut og så to hebraiske menn som holdt på å slåss; da sa han til ham som hadde urett: Hvorfor slår du din landsmann?
14 Mutumin ya ce masa, “Wa ya mai da kai mai mulki da mai hukunci a kanmu? Kana so ne ka kashe ni kamar yadda ka kashe mutumin Masar nan?” Sai Musa ya tsorata, ya yi tunani ya ce, “To, fa, abin nan da na yi, ya zama sananne.”
Han svarte: Hvem har satt dig til høvding og dommer over oss? Tenker du å slå mig ihjel, likesom du slo egypteren ihjel? Da blev Moses redd og sa: Sannelig, saken er blitt kjent.
15 Da Fir’auna ya ji wannan, sai ya yi ƙoƙari yă kashe Musa, amma Musa ya gudu daga wajen Fir’auna, ya tafi ƙasar Midiyan inda ya zauna kusa da wata rijiya.
Da Farao fikk høre det, søkte han å slå Moses ihjel; men Moses flyktet for Farao, og han tok bolig i landet Midian og bodde ved en brønn.
16 To, fa, akwai wani firist na Midiyan, yana da’ya’ya mata bakwai, suka zo su shayar da dabbobin mahaifinsu.
Presten i Midian hadde syv døtre; de kom og øste op vann og fylte vannrennene for å vanne sin fars småfe.
17 Sai waɗansu makiyaya suka zo suka kore su, amma Musa ya tashi ya taimake su ya shayar da dabbobinsu.
Så kom det nogen gjætere og drev dem bort; men Moses stod op og hjalp dem og vannet deres småfe.
18 Da’yan matan suka komo wurin Reyuwel mahaifinsu, sai ya tambaye su ya ce, “Yaya kuka dawo da wuri yau?”
Da de så kom hjem til Re'uel, sin far, sa han: Hvorfor kommer I så snart idag?
19 Suka amsa suka ce, “Wani mutumin Masar ne ya taimake mu daga hannun waɗansu makiyaya. Har ma ya ɗebo ruwa ya shayar da dabbobin.”
De svarte: En egyptisk mann hjalp oss mot gjæterne, og han øste også vann for oss og vannet småfeet.
20 Ya tambayi’yan matansa, “To ina yake? Don me kuka bar shi a can? A gayyace shi, yă zo, yă ci wani abu.”
Da sa han til sine døtre: Hvor er han da? Hvorfor lot I mannen bli igjen der? Be ham inn, så han kan ete med oss!
21 Musa ya yarda yă zauna da mutumin wanda ya ba da’yarsa Ziffora aure da Musa.
Og Moses samtykket i å bli hos mannen; og han lot Moses få sin datter Sippora til hustru.
22 Ziffora ta haifi wa Musa ɗa, ya kuma raɗa masa suna Gershom cewa, “Na zama baƙo a baƙuwar ƙasa.”
Hun fikk en sønn, og han kalte ham Gersom; for han sa: Jeg er blitt en gjest i et fremmed land.
23 Ana nan dai, a kwana a tashi, sai sarkin Masar ya mutu. Isra’ilawa suka yi kuka mai zafi saboda bautarsu mai wuya, sai kukar neman taimakonsu saboda bauta, ya kai wurin Allah.
Da lang tid var gått, døde kongen i Egypten, og Israels barn sukket over sin trældom og klaget; og deres rop over trældommen steg op til Gud.
24 Allah kuwa ya ji kukansu sai ya tuna da alkawarinsa da Ibrahim da Ishaku da Yaƙub.
Og Gud hørte deres sukk, og Gud kom i hu sin pakt med Abraham, Isak og Jakob.
25 Sai Allah ya dubi Isra’ilawa, ya kuma damu da su.
Og Gud så til Israels barn, og Gud kjentes ved dem.

< Fitowa 2 >