< Fitowa 2 >

1 Ana nan, sai wani Balawe ya auri wata Balawiya,
Un homme de la maison de Lévi alla prendre pour femme une fille de Lévi.
2 ta kuwa yi ciki, ta haifi ɗa. Sa’ad da ta ga jaririn kyakkyawa ne, sai ta ɓoye shi har watanni uku.
La femme conçut et enfanta un fils. Elle vit que c'était un bel enfant, et elle le cacha pendant trois mois.
3 Amma da ba tă iya ɓoye shi kuma ba, sai ta yi kwandon kyauro ta shafa masa kwalta. Bayan haka sai ta sa jaririn a cikin kwandon, ta je ta ajiye kwandon tare da jaririn a cikin kyauro, a bakin kogin.
Quand elle ne put plus le cacher, elle prit pour lui un panier de papyrus, qu'elle enduisit de goudron et de poix. Elle y mit l'enfant, et le déposa dans les roseaux au bord du fleuve.
4 ’Yar’uwarsa ta tsaya da ɗan rata tana lura da abin da zai faru da shi.
Sa sœur se tenait à l'écart, pour voir ce qu'on lui ferait.
5 Sai’yar Fir’auna ta gangara zuwa kogi domin tă yi wanka, bayinta kuwa suna tafiya a bakin kogi. Sai ta ga kwandon a ciyawa, ta aiki ɗaya daga cikin masu hidimarta tă ɗauko mata.
La fille de Pharaon descendit pour se baigner au bord du fleuve. Ses servantes se promenaient au bord du fleuve. Elle vit la corbeille parmi les roseaux, et envoya son serviteur la chercher.
6 Da ta buɗe kwandon, sai ta ga yaro yana kuka, ta kuwa ji tausayinsa. Ta ce, “Wannan ɗaya daga cikin jariran Ibraniyawa ne.”
Elle l'ouvrit, vit l'enfant, et voici que l'enfant pleurait. Elle eut pitié de lui et dit: « C'est un des enfants des Hébreux. »
7 Sai’yar’uwarsa ta tambayi’yar Fir’auna, ta ce, “In tafi in samo ɗaya daga cikin matan Ibraniyawa tă yi miki renon yaron?”
Alors sa sœur dit à la fille de Pharaon: « Dois-je aller appeler pour toi une nourrice parmi les femmes hébreues, afin qu'elle allaite l'enfant pour toi? »
8 Sai ta amsa ta ce, “I, tafi.” Sai yarinyar ta tafi ta kawo mahaifiyar yaron.
La fille de Pharaon lui dit: « Va. » La jeune femme alla appeler la mère de l'enfant.
9 Diyar Fir’auna ta ce mata, “Ɗauki jaririn, ki yi mini renonsa, zan kuwa biya ki.” Saboda haka ta ɗauki yaron, ta yi renonsa.
La fille de Pharaon lui dit: « Emmène cet enfant et allaite-le pour moi, et je te donnerai ton salaire. » La femme prit l'enfant et le soigna.
10 Sa’ad da ya yi girma, sai ta kawo shi wajen’yar Fir’auna, ya kuwa zama ɗanta, ta kuma ba shi suna Musa, tana cewa, “Na tsamo shi daga ruwa.”
L'enfant grandit, elle l'amena à la fille de Pharaon, et il devint son fils. Elle lui donna le nom de Moïse, et dit: « Parce que je l'ai tiré de l'eau. »
11 Wata rana, bayan Musa ya yi girma, sai ya haura, ya tafi inda mutanensa suke, ya kuma ga yadda suke shan wahala da aiki. Ya ga wani mutumin Masar yana dūkan mutumin Ibraniyawa, ɗaya daga cikin mutanensa.
En ces jours-là, lorsque Moïse eut grandi, il alla vers ses frères et vit leurs fardeaux. Il vit un Égyptien qui frappait un Hébreu, l'un de ses frères.
12 Da ya leƙa nan da can bai kuwa ga kowa ba, sai ya kashe mutumin Masar, ya ɓoye shi a yashi.
Il regarda de tous côtés, et voyant qu'il n'y avait personne, il tua l'Egyptien et le cacha dans le sable.
13 Kashegari ya fita, sai ya ga Ibraniyawa biyu suna faɗa. Ya tambayi mai laifin ya ce, “Don me kake bugun ɗan’uwanka, mutumin Ibraniyawa?”
Le deuxième jour, il sortit, et voici que deux hommes d'entre les Hébreux se battaient l'un contre l'autre. Il dit à celui qui avait fait le mal: « Pourquoi frappes-tu ton compagnon? »
14 Mutumin ya ce masa, “Wa ya mai da kai mai mulki da mai hukunci a kanmu? Kana so ne ka kashe ni kamar yadda ka kashe mutumin Masar nan?” Sai Musa ya tsorata, ya yi tunani ya ce, “To, fa, abin nan da na yi, ya zama sananne.”
Il dit: « Qui t'a fait prince et juge sur nous? As-tu l'intention de me tuer, comme tu as tué l'Égyptien? » Moïse eut peur, et il dit: « Cette chose est certainement connue. »
15 Da Fir’auna ya ji wannan, sai ya yi ƙoƙari yă kashe Musa, amma Musa ya gudu daga wajen Fir’auna, ya tafi ƙasar Midiyan inda ya zauna kusa da wata rijiya.
Lorsque Pharaon apprit cette chose, il chercha à faire mourir Moïse. Mais Moïse s'enfuit de la face de Pharaon, et habita dans le pays de Madian, et il s'assit près d'un puits.
16 To, fa, akwai wani firist na Midiyan, yana da’ya’ya mata bakwai, suka zo su shayar da dabbobin mahaifinsu.
Or le prêtre de Madian avait sept filles. Elles venaient puiser de l'eau et remplissaient les auges pour abreuver le troupeau de leur père.
17 Sai waɗansu makiyaya suka zo suka kore su, amma Musa ya tashi ya taimake su ya shayar da dabbobinsu.
Les bergers vinrent et les chassèrent, mais Moïse se leva, les aida et abreuva le troupeau.
18 Da’yan matan suka komo wurin Reyuwel mahaifinsu, sai ya tambaye su ya ce, “Yaya kuka dawo da wuri yau?”
Lorsqu'elles arrivèrent auprès de Réuel, leur père, celui-ci leur dit: « Comment se fait-il que vous soyez rentrées si tôt aujourd'hui? ».
19 Suka amsa suka ce, “Wani mutumin Masar ne ya taimake mu daga hannun waɗansu makiyaya. Har ma ya ɗebo ruwa ya shayar da dabbobin.”
Ils dirent: « Un Égyptien nous a délivrés de la main des bergers; de plus, il a puisé de l'eau pour nous et abreuvé le troupeau. »
20 Ya tambayi’yan matansa, “To ina yake? Don me kuka bar shi a can? A gayyace shi, yă zo, yă ci wani abu.”
Il dit à ses filles: « Où est-il? Pourquoi avez-vous laissé cet homme? Appelez-le, qu'il mange du pain. »
21 Musa ya yarda yă zauna da mutumin wanda ya ba da’yarsa Ziffora aure da Musa.
Moïse se contenta d'habiter avec cet homme. Il donna à Moïse Zippora, sa fille.
22 Ziffora ta haifi wa Musa ɗa, ya kuma raɗa masa suna Gershom cewa, “Na zama baƙo a baƙuwar ƙasa.”
Elle enfanta un fils, qu'il appela Gershom, car il disait: « J'ai vécu comme un étranger dans un pays étranger. »
23 Ana nan dai, a kwana a tashi, sai sarkin Masar ya mutu. Isra’ilawa suka yi kuka mai zafi saboda bautarsu mai wuya, sai kukar neman taimakonsu saboda bauta, ya kai wurin Allah.
Au cours de ces nombreux jours, le roi d'Égypte mourut, et les enfants d'Israël poussèrent des soupirs à cause de la servitude, et ils crièrent, et leur cri monta vers Dieu à cause de la servitude.
24 Allah kuwa ya ji kukansu sai ya tuna da alkawarinsa da Ibrahim da Ishaku da Yaƙub.
Dieu entendit leurs gémissements, et il se souvint de son alliance avec Abraham, Isaac et Jacob.
25 Sai Allah ya dubi Isra’ilawa, ya kuma damu da su.
Dieu vit les enfants d'Israël, et il comprit.

< Fitowa 2 >