< Fitowa 2 >

1 Ana nan, sai wani Balawe ya auri wata Balawiya,
(There was a man who/My father) was descended from [Jacob’s son] Levi. He married a woman who was [also] descended from Levi.
2 ta kuwa yi ciki, ta haifi ɗa. Sa’ad da ta ga jaririn kyakkyawa ne, sai ta ɓoye shi har watanni uku.
She became pregnant and gave birth to (a baby boy/me). When she saw that he/I was a good-looking baby, she hid him/me for three months, [because she was not willing to do what the king commanded].
3 Amma da ba tă iya ɓoye shi kuma ba, sai ta yi kwandon kyauro ta shafa masa kwalta. Bayan haka sai ta sa jaririn a cikin kwandon, ta je ta ajiye kwandon tare da jaririn a cikin kyauro, a bakin kogin.
When she was unable to (hide him/me/keep it a secret) any longer, she got a basket made from tall reeds. She covered the basket with tar ([to make it waterproof/so water could not get in]). Then she put him/me in the basket and put the basket in [the water] in the middle of the tall grass at the edge of the Nile [River].
4 ’Yar’uwarsa ta tsaya da ɗan rata tana lura da abin da zai faru da shi.
His/My older sister was standing not far away, [watching to see] what would happen to him/me.
5 Sai’yar Fir’auna ta gangara zuwa kogi domin tă yi wanka, bayinta kuwa suna tafiya a bakin kogi. Sai ta ga kwandon a ciyawa, ta aiki ɗaya daga cikin masu hidimarta tă ɗauko mata.
[Soon] the king’s daughter went down to the river to bathe. Her female servants were walking along the riverbank. She saw the basket amid the tall grass [in the river]. So she sent [one of] her servants to get it.
6 Da ta buɗe kwandon, sai ta ga yaro yana kuka, ta kuwa ji tausayinsa. Ta ce, “Wannan ɗaya daga cikin jariran Ibraniyawa ne.”
When [the servant brought the basket to her], she opened it, and was surprised to see (a baby that was/me), crying. She felt sorry for him/me, and said, “This [must] be one of the Hebrews’ babies.”
7 Sai’yar’uwarsa ta tambayi’yar Fir’auna, ta ce, “In tafi in samo ɗaya daga cikin matan Ibraniyawa tă yi miki renon yaron?”
Then (the baby’s/my) [older] sister [approached] the king’s daughter and said, “Do you want me to go and find someone from among the Hebrew women who will [be able to] nurse the baby for you?”
8 Sai ta amsa ta ce, “I, tafi.” Sai yarinyar ta tafi ta kawo mahaifiyar yaron.
The king’s daughter said to her, “[Yes], go [and find one].” So the girl went and summoned (the baby’s/my) mother.
9 Diyar Fir’auna ta ce mata, “Ɗauki jaririn, ki yi mini renonsa, zan kuwa biya ki.” Saboda haka ta ɗauki yaron, ta yi renonsa.
The king’s daughter said to her, “[Please] take this baby and nurse him for me. I will pay you [for doing that].” So (the woman/my mother) took him/me and nursed him/me.
10 Sa’ad da ya yi girma, sai ta kawo shi wajen’yar Fir’auna, ya kuwa zama ɗanta, ta kuma ba shi suna Musa, tana cewa, “Na tsamo shi daga ruwa.”
([A few years later]/when (the child/I) grew [older]), she brought him/me to the king’s daughter. She adopted him/me [as though I was] her own son. She named him/me Moses, [which sounds like the Hebrew words ‘pull out’], because she said “I pulled him out of the water.”
11 Wata rana, bayan Musa ya yi girma, sai ya haura, ya tafi inda mutanensa suke, ya kuma ga yadda suke shan wahala da aiki. Ya ga wani mutumin Masar yana dūkan mutumin Ibraniyawa, ɗaya daga cikin mutanensa.
One day, after Moses/I had grown up, he/I went out [of the palace area] to see his/my people, [the Hebrews]. He/I saw how they were being [forced to work] very hard. He/I [also] saw an Egyptian [man] beating one of his/my Hebrew people.
12 Da ya leƙa nan da can bai kuwa ga kowa ba, sai ya kashe mutumin Masar, ya ɓoye shi a yashi.
He/I looked around [to see if anyone was watching]. Seeing no one, he/I killed the Egyptian man and buried his [body] in the sand.
13 Kashegari ya fita, sai ya ga Ibraniyawa biyu suna faɗa. Ya tambayi mai laifin ya ce, “Don me kake bugun ɗan’uwanka, mutumin Ibraniyawa?”
The next day he/I returned [to the same place]. He/I was surprised to see two Hebrew men who were fighting [each other]. He/I said to the man who started the fight, “Why are you (you should not be) striking your fellow [Hebrew].”
14 Mutumin ya ce masa, “Wa ya mai da kai mai mulki da mai hukunci a kanmu? Kana so ne ka kashe ni kamar yadda ka kashe mutumin Masar nan?” Sai Musa ya tsorata, ya yi tunani ya ce, “To, fa, abin nan da na yi, ya zama sananne.”
The man replied, “(Who made you our ruler and judge?/No one made you our ruler and judge!) [RHQ] [You have no right to interfere with us] Are you going to kill me just like you killed that Egyptian man [yesterday]?” Then Moses/I was afraid, [because] he/I thought, “[Since that man knows what I did], surely [other people] know, [too].”
15 Da Fir’auna ya ji wannan, sai ya yi ƙoƙari yă kashe Musa, amma Musa ya gudu daga wajen Fir’auna, ya tafi ƙasar Midiyan inda ya zauna kusa da wata rijiya.
[And that was correct]. The king heard about what he/I had done [to that Egyptian. So he ordered his soldiers to] execute/kill Moses/me. But he/I fled from the king [and left Egypt. He/I traveled east to] the Midian [region] and started to live there.
16 To, fa, akwai wani firist na Midiyan, yana da’ya’ya mata bakwai, suka zo su shayar da dabbobin mahaifinsu.
The man who was the (priest/one who offered the people’s gifts to God) for the Midian people, [whose name was Jethro], had seven daughters. [One day] as Moses/I sat down beside a well, those girls came [to the well] and got water, and filled the troughs in order to give water to their father’s flock [of sheep].
17 Sai waɗansu makiyaya suka zo suka kore su, amma Musa ya tashi ya taimake su ya shayar da dabbobinsu.
Some (shepherds/men who took care of other sheep) came and started to chase away the girls. But Moses/I helped/rescued the girls, and got water for their sheep.
18 Da’yan matan suka komo wurin Reyuwel mahaifinsu, sai ya tambaye su ya ce, “Yaya kuka dawo da wuri yau?”
When the girls returned to their father [Jethro], [whose other name is] Reuel, he asked them, “How is it that you were able to [give water to the sheep and] come home so quickly today?”
19 Suka amsa suka ce, “Wani mutumin Masar ne ya taimake mu daga hannun waɗansu makiyaya. Har ma ya ɗebo ruwa ya shayar da dabbobin.”
They replied, “A man from Egypt kept [MTY] other shepherds from sending us away. He also got water for us [from the well] and gave water to the flock [of sheep].”
20 Ya tambayi’yan matansa, “To ina yake? Don me kuka bar shi a can? A gayyace shi, yă zo, yă ci wani abu.”
He said to his daughters, “Where is he? (Why did you leave him [out there]?/You should not leave him [out there]!) [RHQ] Invite him [in], so he can have something to eat [MTY]!”
21 Musa ya yarda yă zauna da mutumin wanda ya ba da’yarsa Ziffora aure da Musa.
[So they did], and Moses/I [accepted and ate with them]. And Moses/I decided to live there. Later Jethro gave him/me his daughter Zipporah [to be his/my wife].
22 Ziffora ta haifi wa Musa ɗa, ya kuma raɗa masa suna Gershom cewa, “Na zama baƙo a baƙuwar ƙasa.”
Later she gave birth to a son, and Moses/I named him Gershom, [which sounds like the Hebrew words that mean ‘foreigner’], because he/I said, “I am living as a foreigner in [this] land.”
23 Ana nan dai, a kwana a tashi, sai sarkin Masar ya mutu. Isra’ilawa suka yi kuka mai zafi saboda bautarsu mai wuya, sai kukar neman taimakonsu saboda bauta, ya kai wurin Allah.
Many years later the king of Egypt died. The Israeli people [in Egypt] were still groaning because of the [hard work they had to do as] slaves. They called out for [someone to] help them, and God heard them call out [PRS].
24 Allah kuwa ya ji kukansu sai ya tuna da alkawarinsa da Ibrahim da Ishaku da Yaƙub.
He heard them groaning. And he (thought about/did not forget) that he had solemnly promised to Abraham, Isaac, and Jacob [to bless their descendants].
25 Sai Allah ya dubi Isra’ilawa, ya kuma damu da su.
God saw how the Israeli people were [being badly treated], and he was concerned about them.

< Fitowa 2 >