< Fitowa 2 >

1 Ana nan, sai wani Balawe ya auri wata Balawiya,
Then there went a man of the house of Leui, and tooke to wife a daughter of Leui,
2 ta kuwa yi ciki, ta haifi ɗa. Sa’ad da ta ga jaririn kyakkyawa ne, sai ta ɓoye shi har watanni uku.
And the woman coceiued and bare a sonne: and when she saw that he was faire, she hid him three moneths.
3 Amma da ba tă iya ɓoye shi kuma ba, sai ta yi kwandon kyauro ta shafa masa kwalta. Bayan haka sai ta sa jaririn a cikin kwandon, ta je ta ajiye kwandon tare da jaririn a cikin kyauro, a bakin kogin.
But when she could no longer hide him, she tooke for him an arke made of reede, and daubed it with slime and with pitch, and laide the childe therein, and put it among the bulrushes by the riuers brinke.
4 ’Yar’uwarsa ta tsaya da ɗan rata tana lura da abin da zai faru da shi.
Now his sister stood a farre off, to wit what would come of him.
5 Sai’yar Fir’auna ta gangara zuwa kogi domin tă yi wanka, bayinta kuwa suna tafiya a bakin kogi. Sai ta ga kwandon a ciyawa, ta aiki ɗaya daga cikin masu hidimarta tă ɗauko mata.
Then ye daughter of Pharaoh came downe to wash her in the riuer, and her maidens walked by the riuers side: and when shee sawe the arke among the bulrushes, she sent her maide to fet it.
6 Da ta buɗe kwandon, sai ta ga yaro yana kuka, ta kuwa ji tausayinsa. Ta ce, “Wannan ɗaya daga cikin jariran Ibraniyawa ne.”
Then she opened it, and sawe it was a childe: and beholde, the babe wept: so she had compassion on it, and sayde, This is one of the Ebrewes children.
7 Sai’yar’uwarsa ta tambayi’yar Fir’auna, ta ce, “In tafi in samo ɗaya daga cikin matan Ibraniyawa tă yi miki renon yaron?”
Then said his sister vnto Pharaohs daughter, Shall I go and cal vnto thee a nurce of the Ebrew women to nurce thee the childe?
8 Sai ta amsa ta ce, “I, tafi.” Sai yarinyar ta tafi ta kawo mahaifiyar yaron.
And Pharaohs daughter sayde to her, Goe. So the maide went and called the childes mother,
9 Diyar Fir’auna ta ce mata, “Ɗauki jaririn, ki yi mini renonsa, zan kuwa biya ki.” Saboda haka ta ɗauki yaron, ta yi renonsa.
To whome Pharaohs daughter sayde, Take this childe away, and nurce it for me, and I wil reward thee. Then the woman tooke the childe and nurced him.
10 Sa’ad da ya yi girma, sai ta kawo shi wajen’yar Fir’auna, ya kuwa zama ɗanta, ta kuma ba shi suna Musa, tana cewa, “Na tsamo shi daga ruwa.”
Nowe the childe grewe, and she brought him vnto Pharaohs daughter, and he was as her sonne, and she called his name Moses, because, said she, I drewe him out of the water.
11 Wata rana, bayan Musa ya yi girma, sai ya haura, ya tafi inda mutanensa suke, ya kuma ga yadda suke shan wahala da aiki. Ya ga wani mutumin Masar yana dūkan mutumin Ibraniyawa, ɗaya daga cikin mutanensa.
And in those dayes, when Moses was growen, he went forth vnto his brethren, and looked on their burdens: also he sawe an Egyptian smiting an Ebrewe one of his brethren.
12 Da ya leƙa nan da can bai kuwa ga kowa ba, sai ya kashe mutumin Masar, ya ɓoye shi a yashi.
And he looked rounde about, and when he sawe no man, hee slewe the Egyptian, and hid him in the sande.
13 Kashegari ya fita, sai ya ga Ibraniyawa biyu suna faɗa. Ya tambayi mai laifin ya ce, “Don me kake bugun ɗan’uwanka, mutumin Ibraniyawa?”
Againe he came forth the second day, and behold, two Ebrewes stroue: and he said vnto him that did the wrong, Wherefore smitest thou thy fellowe?
14 Mutumin ya ce masa, “Wa ya mai da kai mai mulki da mai hukunci a kanmu? Kana so ne ka kashe ni kamar yadda ka kashe mutumin Masar nan?” Sai Musa ya tsorata, ya yi tunani ya ce, “To, fa, abin nan da na yi, ya zama sananne.”
And hee answered, Who made thee a man of authoritie, and a iudge ouer vs? Thinkest thou to kill mee, as thou killedst the Egyptian? Then Moses feared and sayde, Certainly this thing is knowen.
15 Da Fir’auna ya ji wannan, sai ya yi ƙoƙari yă kashe Musa, amma Musa ya gudu daga wajen Fir’auna, ya tafi ƙasar Midiyan inda ya zauna kusa da wata rijiya.
Now Pharaoh heard this matter, and sought to slay Moses: therefore Moses fled from Pharaoh, and dwelt in the lande of Midian, and hee sate downe by a well.
16 To, fa, akwai wani firist na Midiyan, yana da’ya’ya mata bakwai, suka zo su shayar da dabbobin mahaifinsu.
And the Priest of Midian had seue daughters, which came and drewe water, and filled the troghes, for to water their fathers sheepe.
17 Sai waɗansu makiyaya suka zo suka kore su, amma Musa ya tashi ya taimake su ya shayar da dabbobinsu.
Then the shepherds came and droue them away: but Moses rose vp and defended them, and watered their sheepe.
18 Da’yan matan suka komo wurin Reyuwel mahaifinsu, sai ya tambaye su ya ce, “Yaya kuka dawo da wuri yau?”
And whe they came to Reuel their father, he said, Howe are ye come so soone to day?
19 Suka amsa suka ce, “Wani mutumin Masar ne ya taimake mu daga hannun waɗansu makiyaya. Har ma ya ɗebo ruwa ya shayar da dabbobin.”
And they saide, A man of Egypt deliuered vs from the hand of the shepherdes, and also drew vs water ynough, and watered the sheepe.
20 Ya tambayi’yan matansa, “To ina yake? Don me kuka bar shi a can? A gayyace shi, yă zo, yă ci wani abu.”
Then he saide vnto his daughters, And where is he? why haue ye so left the man? call him that he may eate bread.
21 Musa ya yarda yă zauna da mutumin wanda ya ba da’yarsa Ziffora aure da Musa.
And Moses agreed to dwell with the man: who gaue vnto Moses Zipporah his daughter:
22 Ziffora ta haifi wa Musa ɗa, ya kuma raɗa masa suna Gershom cewa, “Na zama baƙo a baƙuwar ƙasa.”
And she bare a sonne, whose name he called Gershom: for he said, I haue bene a stranger in a strange lande.
23 Ana nan dai, a kwana a tashi, sai sarkin Masar ya mutu. Isra’ilawa suka yi kuka mai zafi saboda bautarsu mai wuya, sai kukar neman taimakonsu saboda bauta, ya kai wurin Allah.
Then in processe of time, the King of Egypt dyed, and the children of Israel sighed for the bondage and cryed: and their crie for the bondage came vp vnto God.
24 Allah kuwa ya ji kukansu sai ya tuna da alkawarinsa da Ibrahim da Ishaku da Yaƙub.
Then God heard their mone, and God remembred his couenant with Abraham, Izhak, and Iaakob.
25 Sai Allah ya dubi Isra’ilawa, ya kuma damu da su.
So God looked vpon the children of Israel, and God had respect vnto them.

< Fitowa 2 >