< Fitowa 19 >

1 A rana ta farko a cikin watan uku bayan da Isra’ilawa suka bar Masar, a wannan rana, suka iso Hamadar Sinai.
İzrailybı Misireençe qığepç'iyne xhebıd'esde vuzane ts'eppiyne yiğıl Sinayne sahreeqa hiviyxhar.
2 Bayan da suka tashi daga Refidim, suka shiga Hamadar Sinai, sai Isra’ilawa suka yi sansani a gaban dutsen.
Refidimğançe qığeepç'ı, manbı qavaylenbı Sinayne sahreeqa. Manbışe suvalqa ı'lqəəne cigee çadırbı giyxə.
3 Sai Musa ya hau kan dutsen don yă sadu da Allah, Ubangiji kuwa ya kira shi daga dutsen ya ce, “Wannan shi ne abin da za ka faɗa wa gidan Yaƙub, da kuma abin da za ka faɗa wa mutanen Isra’ila.
Mısa suvalqa Allahısqana ılqeç'e. Rəbbee mana suvale qort'ul eyhen: – Yaaq'ubıke g'abıynbışik'le, İzrailybışik'le eyhe:
4 ‘Ku da kanku kun ga abin da na yi wa Masar, da yadda na ɗauko ku a kan fikafikan gaggafa na kawo ku wurina.
«Şok'le Zı Misirbışik hı'iynıd, nəxübiy şu q'aacirın xhinne xılibışil Zasqa qabıyid g'acuyn.
5 Yanzu, in kuka yi mini cikakken biyayya, kuka kuma kiyaye yarjejjeniyata, to, za ku zama keɓeɓɓiyar taska a gare ni a cikin dukan al’ummai. Ko da yake duk duniya tawa ce,
Həşdiyle şu Yizde cuvabıl yugda k'ırı gyaqqeene, Yizda şokana mugaavile havaaceene, manisa milletbışile Zas delesın millet şu vuxhes. İn dyunyecad Yizın vodun,
6 za ku zama firistoci masu tsarki da kuma al’umma keɓaɓɓiya a gare ni.’ Waɗannan su ne kalmomin da za ka faɗa wa Isra’ilawa.”
şunab Yizdemee kaahinaaşin ç'ak'ınbı, paççahar vuxhes, muq'addasın millet ixhes». Man gırgıne İzrailybışik'le eyhe.
7 Sai Musa ya koma ya aika a kira dukan dattawan mutane, ya bayyana dukan kalmomin da Ubangiji ya umarta, ya faɗa.
Mısa avqa giç'u milletın ağsaqqalar sav'u, Rəbbee uvhuyn gırgın manbışis yuşan ha'a.
8 Dukan mutane suka amsa gaba ɗaya suka ce, “Za mu yi duk abin da Ubangiji ya faɗa.” Sai Musa ya mayar wa Ubangiji amsar da mutane suka bayar.
Milletıncad inəxdun alidghıniy qele: – Rəbbee uvhuyn gırgın şi ha'asın! Mısee manbışin alidghıniy Rəbbis hixhar ha'a.
9 Ubangiji kuwa ya ce wa Musa, “Ina zuwa wurinka a cikin baƙin hadari, domin mutane su ji ni ina maganar da kai, domin su amince da kai koyaushe.” Sa’an nan Musa ya faɗa wa Ubangiji abin da mutane suka ce.
Rəbbee Mısayk'le eyhen: – Zı yiğne k'anyaqa k'ışşeyne buludee ayres, milletık'le Zı vaka yuşan ha'a g'ayxhı valqa gırgıne gahbışiscad inyam he'ecenva. Mısee milletın uvhuyn Rəbbilqa hixhara'ang'a,
10 Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Tafi wurin mutanen, ka tsarkake su yau da gobe, ka sa su wanke tufafinsu.
Rəbbee meed Mısayk'le eyhen: – Milletısqa hark'ın manbışik'le eyhe: g'iynayiy g'iyqa manbı məttıba vuxhecen, tanalinbıd hoğlecen.
11 Su zama da shiri a rana ta uku, gama a ranar ce Ubangiji zai sauko a kan Dutsen Sinai a idon dukan mutane.
Qıtsıqiys Rəbbee nəxüdiy uvhu, həməxübub vuxhecen, Rəbb milletne ulene ögiyl Sinayne suvalqa giç'es.
12 Sai ka yi wa jama’a iyaka kewaye da dutsen, ka kuma faɗa musu cewa, ‘Ku mai da hankali, kada ku hau dutsen ko ku taɓa gefensa. Duk wanda ya taɓa dutsen, lalle za a kashe shi.
Suvayne hiqiy-alla milletnemee sarhad ts'ıts'av'u manbışik'le eyhe: «Suvalqa ılqımeebaç'e, mançik xıl simet'a. Suvayk xıl set'una g'ılymaraççe, gik'e.
13 Za a jajjefe shi da duwatsu, ko a harbe shi da kibiyoyi, ba hannun da zai taɓa shi. Mutum ko dabbar da ya taɓa, ba za a bar shi da rai ba.’ Lokacin da aka ji muryar ƙaho ne kawai za su iya taru a gindin dutsen.”
Məxrına ixheene, g'ayeyqqaye hele vukukaye gek'a gik'e, saccu mang'uk xıl simet'a. İnsan ixheyir həyvan vuxheyib əq'ənançecab gyuvk'e, g'ılymabaççe». G'argıne gaçençe xıliyna syuty hav'umee, manbışisse suvalqa ılqeepç'es vəəxə.
14 Bayan da Musa ya gangara wurin mutane, ya tsarkake su, sai suka wanke tufafinsu.
Mısa suvayle g'iç'u milletık'le gicəpxeva eyhe. Manbışed tanalinbı hoyğalanbı.
15 Sa’an nan ya ce wa mutane, “Ku shirya kanku domin rana ta uku. Ku ƙame kanku daga yin jima’i.”
Mang'vee milletık'le eyhen: – Qıtsıqiys Rəbbee nəxüdiy uvhu, həməxübub vuxhe. Sayid yik'el aqqe yadaaşik xıl simet'a.
16 A safiyar rana ta uku, aka yi tsawa, da walƙiyoyi, sai ga girgije mai duhu a bisa dutsen, aka tsananta busar ƙaho, sai dukan jama’ar da suke cikin sansani suka yi rawar jiki.
Xhebıd'esde yiğıl miç'eed xəy g'əhədaqqə giyğal, ts'ayilpan eyxhe, k'ışşeyn bulud suval ooqa sadayle, g'argıne gaçençenab it'umna syuty vooxhe. Çadırbışisneebın gırgın insanar mançile it'umba qəvəyq'ənanbı.
17 Sa’an nan Musa ya jagoranci mutane daga sansani domin su sadu da Allah, sai suka tsaya a gefen dutsen.
Mısee Allah qızaxecenva insanar cone çadırbışisse suvaysqa saa'a.
18 Dutsen Sinai kuwa ya tunnuƙe duka da hayaƙi, gama Ubangiji ya sauko a bisan dutsen cikin wuta. Hayaƙin ya hau kamar hayaƙin da yake fitowa daga matoya, duk dutsen ya yi rawa da ƙarfi,
Rəbb Sinayne suvalqa ts'ayine ar giç'uva suva kumayncab alyabat'a. Mane suvayle xənne peşteençen xhinne kuma ı'lqəə eyxhe. Mane gahıl suva it'umba ı'ğviykarna,
19 sai karar ƙaho ya yi ta ƙaruwa. Sa’an nan Musa ya yi magana, murya Allah kuwa ta amsa masa.
ittehesu g'argıne gaçençena syutyub geeb qooxhe giviyğal. Mısee eyhençis Allahee alidghıniy xəybı g'əhədəqqəne sesika qele ıxha.
20 Ubangiji ya sauko a kan ƙwanƙolin Dutsen Sinai, ya kira Musa zuwa ƙwanƙolin dutsen. Musa kuwa ya haura
Rəbb Sinay eyhene suvayne q'omaqa giç'u, maqa Mısa qoyt'al. Mısa maqa ılqeç'umee,
21 sai Ubangiji ya ce masa, “Ka sauka ka faɗa wa jama’a, kada su kuskura su ƙetare layin iyakan nan, garin son zuwa don ganin Ubangiji, gama duk waɗanda suka yi haka za su mutu.
Rəbbee mang'uk'le eyhen: – Giç'e milletık'le eyhe, Rəbb g'acesva çosva gyuvxhune sarhadıle ılğımebaç'ecen. Uvhuyn hide'eene con gellesınbı hapt'asınbı.
22 Ko firistocin da za su kusato Ubangiji sai su tsarkake kansu, don kada in hallaka su.”
Rəbbisqa qeepxhesın kaahinaaşin ç'ak'ınbıb gicəpxı' vuxhes vukkan. Uvhuyn hide'eene Rəbbee manbışikınıd ha'asın.
23 Musa ya ce wa Ubangiji, “Mutanen ba za su hau Dutsen Sinai ba, gama kai da kanka ka gargaɗe mu, ‘Ku sa iyaka kewaye da dutsen ku kuma tsarkake shi.’”
Mısee Rəbbik'le eyhen: – Nya'a Ğu şak'le uvhu dişdiy «Suvayne hiqiy-alla sarhad ts'ıts'av'u mançike er hee'eva». Mançil-allad milletın Sinayne suvalqa gov gyuvxhes deş.
24 Ubangiji ya amsa, “Sauka ka kawo Haruna tare da kai. Amma kada firistoci da mutane su zarce iyakan nan, a kan za su zo wurin Ubangiji, don kada in hallaka su.”
Rəbbee eyhen: – Giç'e, vakasana inyaqa Harun ayre. İlahiyetçeeşine ç'ak'ınbışeb, milletınıd suvalqa Rəbbisqa ı'lqəəva sarhad ılğımooç'ecen. Uvhuyn hide'eene Rəbbee cokun ha'asın.
25 Saboda haka Musa ya sauka wurin mutane ya kuma faɗa musu.
Mısa suvayle giç'u man uvhuynbı milletılqa hixhar ha'a.

< Fitowa 19 >