< Fitowa 19 >

1 A rana ta farko a cikin watan uku bayan da Isra’ilawa suka bar Masar, a wannan rana, suka iso Hamadar Sinai.
V tretjem mesecu, ko so Izraelovi otroci odšli iz egiptovske dežele, istega dne, so prišli v Sinajsko divjino.
2 Bayan da suka tashi daga Refidim, suka shiga Hamadar Sinai, sai Isra’ilawa suka yi sansani a gaban dutsen.
Kajti odšli so iz Refidíma in prišli v sinajsko puščavo in se utaborili v divjini in tam je Izrael taboril pred goro.
3 Sai Musa ya hau kan dutsen don yă sadu da Allah, Ubangiji kuwa ya kira shi daga dutsen ya ce, “Wannan shi ne abin da za ka faɗa wa gidan Yaƙub, da kuma abin da za ka faɗa wa mutanen Isra’ila.
Mojzes je odšel gor k Bogu in Gospod je zaklical k njemu z gore, rekoč: »Tako boš rekel Jakobovi hiši in povedal Izraelovim otrokom:
4 ‘Ku da kanku kun ga abin da na yi wa Masar, da yadda na ɗauko ku a kan fikafikan gaggafa na kawo ku wurina.
›Videli ste, kaj sem storil Egipčanom in kako sem vas nosil na orljih perutih in vas privedel k sebi.
5 Yanzu, in kuka yi mini cikakken biyayya, kuka kuma kiyaye yarjejjeniyata, to, za ku zama keɓeɓɓiyar taska a gare ni a cikin dukan al’ummai. Ko da yake duk duniya tawa ce,
Zdaj torej, če boste zares poslušali moj glas in se držali moje zaveze, potem mi boste izvoljen zaklad nad vsemi ljudstvi, kajti vsa zemlja je moja,
6 za ku zama firistoci masu tsarki da kuma al’umma keɓaɓɓiya a gare ni.’ Waɗannan su ne kalmomin da za ka faɗa wa Isra’ilawa.”
vi pa mi boste kraljestvo duhovnikov in svet narod.‹ To so besede, ki jih boš govoril Izraelovim otrokom.«
7 Sai Musa ya koma ya aika a kira dukan dattawan mutane, ya bayyana dukan kalmomin da Ubangiji ya umarta, ya faɗa.
Mojzes je prišel ter dal poklicati starešine ljudstva in pred njihove obraze položil vse te besede, ki mu jih je Gospod zapovedal.
8 Dukan mutane suka amsa gaba ɗaya suka ce, “Za mu yi duk abin da Ubangiji ya faɗa.” Sai Musa ya mayar wa Ubangiji amsar da mutane suka bayar.
Vse ljudstvo je skupaj odgovorilo ter reklo: »Vse, kar je Gospod govoril, bomo storili.« In Mojzes je besede ljudstva ponovil Gospodu.
9 Ubangiji kuwa ya ce wa Musa, “Ina zuwa wurinka a cikin baƙin hadari, domin mutane su ji ni ina maganar da kai, domin su amince da kai koyaushe.” Sa’an nan Musa ya faɗa wa Ubangiji abin da mutane suka ce.
Gospod je rekel Mojzesu: »Glej, k tebi pridem v gostem oblaku, da bo ljudstvo lahko slišalo, ko govorim s teboj in ti verjelo na veke.« In Mojzes je besede ljudstva povedal Gospodu.
10 Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Tafi wurin mutanen, ka tsarkake su yau da gobe, ka sa su wanke tufafinsu.
Gospod je rekel Mojzesu: »Pojdi k ljudstvu in posvečuj jih danes in jutri in naj si operejo svoja oblačila
11 Su zama da shiri a rana ta uku, gama a ranar ce Ubangiji zai sauko a kan Dutsen Sinai a idon dukan mutane.
in bodite pripravljeni za tretji dan, kajti tretji dan bo Gospod prišel dol, v očeh vsega ljudstva, na goro Sinaj.
12 Sai ka yi wa jama’a iyaka kewaye da dutsen, ka kuma faɗa musu cewa, ‘Ku mai da hankali, kada ku hau dutsen ko ku taɓa gefensa. Duk wanda ya taɓa dutsen, lalle za a kashe shi.
Ti pa boš ljudstvu postavil meje naokoli, rekoč: ›Pazite se, da ne greste gor na goro ali se dotaknete njene meje. Kdorkoli se dotakne gore, bo zagotovo usmrčen.
13 Za a jajjefe shi da duwatsu, ko a harbe shi da kibiyoyi, ba hannun da zai taɓa shi. Mutum ko dabbar da ya taɓa, ba za a bar shi da rai ba.’ Lokacin da aka ji muryar ƙaho ne kawai za su iya taru a gindin dutsen.”
Niti roka se ga ne bo dotaknila, temveč naj bo zagotovo kamnan ali prestreljen; bodisi bo to žival ali človek, naj ta ne živi. Ko zadoni trobljenje naj pridejo h gori.‹«
14 Bayan da Musa ya gangara wurin mutane, ya tsarkake su, sai suka wanke tufafinsu.
Mojzes je odšel dol z gore k ljudstvu in ljudstvo posvetil, in ti so si oprali svoja oblačila.
15 Sa’an nan ya ce wa mutane, “Ku shirya kanku domin rana ta uku. Ku ƙame kanku daga yin jima’i.”
Ljudstvu je rekel: »Bodite pripravljeni na tretji dan. Ne približujte se k svojim ženam.«
16 A safiyar rana ta uku, aka yi tsawa, da walƙiyoyi, sai ga girgije mai duhu a bisa dutsen, aka tsananta busar ƙaho, sai dukan jama’ar da suke cikin sansani suka yi rawar jiki.
Na tretji dan se je zjutraj pripetilo, da so bila grmenja in bliski in na gori gost oblak in silno glasen zvok šofarja, tako da je vse ljudstvo, ki je bilo v taboru, trepetalo.
17 Sa’an nan Musa ya jagoranci mutane daga sansani domin su sadu da Allah, sai suka tsaya a gefen dutsen.
Mojzes je ljudstvo privedel iz tabora, da se sreča z Bogom. Stali so pri spodnjem delu gore.
18 Dutsen Sinai kuwa ya tunnuƙe duka da hayaƙi, gama Ubangiji ya sauko a bisan dutsen cikin wuta. Hayaƙin ya hau kamar hayaƙin da yake fitowa daga matoya, duk dutsen ya yi rawa da ƙarfi,
Gora Sinaj je bila povsem v dimu, ker se je Gospod nanjo spustil v ognju in njen dim se je vzpenjal kakor dim iz talilne peči in celotna gora se je silno tresla.
19 sai karar ƙaho ya yi ta ƙaruwa. Sa’an nan Musa ya yi magana, murya Allah kuwa ta amsa masa.
Ko je glas šofarja zategnjeno donel in postajal glasnejši in glasnejši, je Mojzes spregovoril in Bog mu je odgovoril z glasom.
20 Ubangiji ya sauko a kan ƙwanƙolin Dutsen Sinai, ya kira Musa zuwa ƙwanƙolin dutsen. Musa kuwa ya haura
Gospod je prišel dol na goro Sinaj, na vrh gore in Gospod je Mojzesa poklical gor na vrh gore in Mojzes je odšel gor.
21 sai Ubangiji ya ce masa, “Ka sauka ka faɗa wa jama’a, kada su kuskura su ƙetare layin iyakan nan, garin son zuwa don ganin Ubangiji, gama duk waɗanda suka yi haka za su mutu.
Gospod je rekel Mojzesu: »Pojdi dol, naroči ljudstvu, da se ne bi prebili h Gospodu, da bi strmeli in se mnogi izmed njih pogubijo.
22 Ko firistocin da za su kusato Ubangiji sai su tsarkake kansu, don kada in hallaka su.”
Naj se tudi duhovniki, ki pridejo bliže h Gospodu, posvétijo, da ne bi Gospod izbruhnil nad njimi.«
23 Musa ya ce wa Ubangiji, “Mutanen ba za su hau Dutsen Sinai ba, gama kai da kanka ka gargaɗe mu, ‘Ku sa iyaka kewaye da dutsen ku kuma tsarkake shi.’”
Mojzes pa je rekel Gospodu: »Ljudstvo se ne more povzpeti na goro Sinaj, kajti zapovedal si nam, rekoč: ›Postavi meje okoli gore in jo posvéti.‹«
24 Ubangiji ya amsa, “Sauka ka kawo Haruna tare da kai. Amma kada firistoci da mutane su zarce iyakan nan, a kan za su zo wurin Ubangiji, don kada in hallaka su.”
Gospod mu je rekel: »Proč, spusti se in prišel boš gor, ti in Aron s teboj. Toda duhovniki in ljudstvo naj se ne prebijejo, da pridejo h Gospodu, da ne bi nad njimi izbruhnil.«
25 Saboda haka Musa ya sauka wurin mutane ya kuma faɗa musu.
Tako je Mojzes odšel dol k ljudstvu in jim spregovoril.

< Fitowa 19 >