< Fitowa 19 >

1 A rana ta farko a cikin watan uku bayan da Isra’ilawa suka bar Masar, a wannan rana, suka iso Hamadar Sinai.
بنی‌اسرائیل در ماه سوم خروجشان از مصر، در همان نخستین روز ماه، به صحرای سینا رسیدند.
2 Bayan da suka tashi daga Refidim, suka shiga Hamadar Sinai, sai Isra’ilawa suka yi sansani a gaban dutsen.
آنان پس از ترک رفیدیم وارد بیابان سینا شدند و در مقابل کوه سینا اردو زدند.
3 Sai Musa ya hau kan dutsen don yă sadu da Allah, Ubangiji kuwa ya kira shi daga dutsen ya ce, “Wannan shi ne abin da za ka faɗa wa gidan Yaƙub, da kuma abin da za ka faɗa wa mutanen Isra’ila.
موسی برای ملاقات با خدا به بالای کوه رفت. خداوند از میان کوه خطاب به موسی فرمود: «این دستورها را به خاندان یعقوب بده؛ آنها را به بنی‌اسرائیل اعلان کن:
4 ‘Ku da kanku kun ga abin da na yi wa Masar, da yadda na ɗauko ku a kan fikafikan gaggafa na kawo ku wurina.
”شما دیدید که من با مصری‌ها چه کردم و چطور مانند عقابی که بچه‌هایش را روی بالهای خود می‌برد، شما را برداشته، پیش خود آوردم.
5 Yanzu, in kuka yi mini cikakken biyayya, kuka kuma kiyaye yarjejjeniyata, to, za ku zama keɓeɓɓiyar taska a gare ni a cikin dukan al’ummai. Ko da yake duk duniya tawa ce,
حال اگر مطیع من باشید و عهد مرا نگاه دارید، از میان همهٔ اقوام، شما قوم خاص من خواهید بود؛ زیرا سراسر جهان مال من است.
6 za ku zama firistoci masu tsarki da kuma al’umma keɓaɓɓiya a gare ni.’ Waɗannan su ne kalmomin da za ka faɗa wa Isra’ilawa.”
شما برای من مملکتی از کاهنان و قومی مقدّس خواهید بود.“این است آنچه باید به بنی‌اسرائیل بگویی.»
7 Sai Musa ya koma ya aika a kira dukan dattawan mutane, ya bayyana dukan kalmomin da Ubangiji ya umarta, ya faɗa.
پس موسی از کوه فرود آمد و مشایخ بنی‌اسرائیل را دور خود جمع کرد و هر چه را که خداوند به او فرموده بود به ایشان بازگفت.
8 Dukan mutane suka amsa gaba ɗaya suka ce, “Za mu yi duk abin da Ubangiji ya faɗa.” Sai Musa ya mayar wa Ubangiji amsar da mutane suka bayar.
همهٔ قوم یکصدا جواب دادند: «هر آنچه خداوند از ما خواسته است، انجام می‌دهیم.» پس موسی نزد خداوند بازگشت تا آنچه قوم گفته بودند به او بازگوید.
9 Ubangiji kuwa ya ce wa Musa, “Ina zuwa wurinka a cikin baƙin hadari, domin mutane su ji ni ina maganar da kai, domin su amince da kai koyaushe.” Sa’an nan Musa ya faɗa wa Ubangiji abin da mutane suka ce.
آنگاه خداوند به موسی فرمود: «من در ابر غلیظی نزد تو می‌آیم تا هنگامی که با تو گفتگو می‌کنم قوم به گوش خود صدای مرا بشنوند و از این پس گفتار تو را باور کنند.» موسی سخنان قوم را به خداوند عرض کرد
10 Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Tafi wurin mutanen, ka tsarkake su yau da gobe, ka sa su wanke tufafinsu.
و خداوند به موسی فرمود: «حال پایین برو و قوم را برای آمدن من آماده کن. ایشان را امروز و فردا تقدیس کن و به آنها بگو لباسهای خود را بشویند،
11 Su zama da shiri a rana ta uku, gama a ranar ce Ubangiji zai sauko a kan Dutsen Sinai a idon dukan mutane.
و روز سوم آماده باشند، زیرا در آن روز خداوند در برابر چشمان همۀ قوم بر کوه سینا نزول خواهد کرد.
12 Sai ka yi wa jama’a iyaka kewaye da dutsen, ka kuma faɗa musu cewa, ‘Ku mai da hankali, kada ku hau dutsen ko ku taɓa gefensa. Duk wanda ya taɓa dutsen, lalle za a kashe shi.
حدودی دور تا دور کوه تعیین کن که قوم از آن جلوتر نیایند و به ایشان بگو که از کوه بالا نروند و حتی دامنۀ آن را لمس نکنند. هر که کوه را لمس کند کشته خواهد شد.
13 Za a jajjefe shi da duwatsu, ko a harbe shi da kibiyoyi, ba hannun da zai taɓa shi. Mutum ko dabbar da ya taɓa, ba za a bar shi da rai ba.’ Lokacin da aka ji muryar ƙaho ne kawai za su iya taru a gindin dutsen.”
او باید سنگسار گردد و یا با تیر کشته شود بدون اینکه کسی به او دست بزند. این قانون شامل حیوانات نیز می‌شود. پس به کوه نزدیک نشوید تا اینکه صدای شیپور برخیزد، آنگاه می‌توانید از کوه بالا بروید.»
14 Bayan da Musa ya gangara wurin mutane, ya tsarkake su, sai suka wanke tufafinsu.
موسی از کوه فرود آمد و بنی‌اسرائیل را تقدیس نمود و آنها لباسهای خود را شستند.
15 Sa’an nan ya ce wa mutane, “Ku shirya kanku domin rana ta uku. Ku ƙame kanku daga yin jima’i.”
موسی به ایشان فرمود: «خود را برای روز سوم آماده کنید، و تا آن روز با زنان خود نزدیکی ننمایید.»
16 A safiyar rana ta uku, aka yi tsawa, da walƙiyoyi, sai ga girgije mai duhu a bisa dutsen, aka tsananta busar ƙaho, sai dukan jama’ar da suke cikin sansani suka yi rawar jiki.
صبح روز سوم، صدای هولناک رعد و برق شنیده شد و ابر غلیظی روی کوه پدید آمد. سپس صدای بسیار بلندی چون صدای شیپور برخاست. تمام قوم از ترس لرزیدند.
17 Sa’an nan Musa ya jagoranci mutane daga sansani domin su sadu da Allah, sai suka tsaya a gefen dutsen.
آنگاه موسی آنها را برای ملاقات با خدا از اردوگاه بیرون برد. همه در پای کوه ایستادند.
18 Dutsen Sinai kuwa ya tunnuƙe duka da hayaƙi, gama Ubangiji ya sauko a bisan dutsen cikin wuta. Hayaƙin ya hau kamar hayaƙin da yake fitowa daga matoya, duk dutsen ya yi rawa da ƙarfi,
تمام کوه سینا از دود پوشیده شد، زیرا خداوند در آتش بر آن نزول کرد. از کوه دود برخاست و مانند دود کوره، در هوا بالا رفت و تمام کوه به شدت لرزید.
19 sai karar ƙaho ya yi ta ƙaruwa. Sa’an nan Musa ya yi magana, murya Allah kuwa ta amsa masa.
در حالی که صدای کَرِنا هر لحظه بلندتر می‌شد، موسی با خدا سخن می‌گفت و خدا هم با صدایی نظیر صدای رعد به او جواب می‌داد.
20 Ubangiji ya sauko a kan ƙwanƙolin Dutsen Sinai, ya kira Musa zuwa ƙwanƙolin dutsen. Musa kuwa ya haura
وقتی خداوند بر قلهٔ کوه سینا نزول کرده بود، موسی را فرا خواند و موسی نیز به قلهٔ کوه بالا رفت.
21 sai Ubangiji ya ce masa, “Ka sauka ka faɗa wa jama’a, kada su kuskura su ƙetare layin iyakan nan, garin son zuwa don ganin Ubangiji, gama duk waɗanda suka yi haka za su mutu.
خداوند به موسی فرمود: «پایین برو و به قوم هشدار بده که از حدود تعیین شده تجاوز نکنند و برای دیدن خداوند بالا نیایند و گرنه هلاک می‌شوند.
22 Ko firistocin da za su kusato Ubangiji sai su tsarkake kansu, don kada in hallaka su.”
حتی کاهنانی که به من نزدیک می‌شوند باید خود را تقدیس کنند تا خداوند بر ایشان غضبناک نشود.»
23 Musa ya ce wa Ubangiji, “Mutanen ba za su hau Dutsen Sinai ba, gama kai da kanka ka gargaɗe mu, ‘Ku sa iyaka kewaye da dutsen ku kuma tsarkake shi.’”
موسی عرض کرد: «قوم نمی‌توانند از کوه سینا بالا بیایند، زیرا تو خود به ما هشدار داده، گفتی:”حدودی دور تا دور کوه تعیین کن و آن را مقدّس بشمار.“»
24 Ubangiji ya amsa, “Sauka ka kawo Haruna tare da kai. Amma kada firistoci da mutane su zarce iyakan nan, a kan za su zo wurin Ubangiji, don kada in hallaka su.”
خداوند فرمود: «پایین برو و هارون را با خود بالا بیاور. در ضمن نگذار کاهنان یا قوم از آن حد تجاوز کنند تا نزد من بالا بیایند، زیرا آنها را در هم شکسته، نابود خواهم کرد.»
25 Saboda haka Musa ya sauka wurin mutane ya kuma faɗa musu.
پس موسی نزد قوم پایین رفت و آنچه خداوند به او فرموده بود به ایشان بازگفت.

< Fitowa 19 >