< Fitowa 19 >

1 A rana ta farko a cikin watan uku bayan da Isra’ilawa suka bar Masar, a wannan rana, suka iso Hamadar Sinai.
In the third month of the departure of Israel out of the land of Egypt, on this day they came into the wilderness of Sinai:
2 Bayan da suka tashi daga Refidim, suka shiga Hamadar Sinai, sai Isra’ilawa suka yi sansani a gaban dutsen.
For departing out of Raphidim, and coming to the desert of Sinai, they camped in the same place, and there Israel pitched their tents over against the mountain.
3 Sai Musa ya hau kan dutsen don yă sadu da Allah, Ubangiji kuwa ya kira shi daga dutsen ya ce, “Wannan shi ne abin da za ka faɗa wa gidan Yaƙub, da kuma abin da za ka faɗa wa mutanen Isra’ila.
And Moses went up to God: and the Lord called unto him from the mountain, and said: Thus shalt thou say to the house of Jacob, and tell the children of Israel:
4 ‘Ku da kanku kun ga abin da na yi wa Masar, da yadda na ɗauko ku a kan fikafikan gaggafa na kawo ku wurina.
You have seen what I have done to the Egyptians, how I have carried you upon the wings of eagles, and have taken you to myself.
5 Yanzu, in kuka yi mini cikakken biyayya, kuka kuma kiyaye yarjejjeniyata, to, za ku zama keɓeɓɓiyar taska a gare ni a cikin dukan al’ummai. Ko da yake duk duniya tawa ce,
If therefore you will hear my voice, and keep my covenant, you shall be my peculiar possession above all people: for all the earth is mine.
6 za ku zama firistoci masu tsarki da kuma al’umma keɓaɓɓiya a gare ni.’ Waɗannan su ne kalmomin da za ka faɗa wa Isra’ilawa.”
And you shall be to me a priestly kingdom, and a holy nation. Those are the words thou shalt speak to the children of Israel.
7 Sai Musa ya koma ya aika a kira dukan dattawan mutane, ya bayyana dukan kalmomin da Ubangiji ya umarta, ya faɗa.
Moses came, and calling together the elders of the people, he declared all the words which the Lord had commanded.
8 Dukan mutane suka amsa gaba ɗaya suka ce, “Za mu yi duk abin da Ubangiji ya faɗa.” Sai Musa ya mayar wa Ubangiji amsar da mutane suka bayar.
And all the people answered together: All that the Lord hath spoken, we will do. And when Moses had related the people’s words to the Lord,
9 Ubangiji kuwa ya ce wa Musa, “Ina zuwa wurinka a cikin baƙin hadari, domin mutane su ji ni ina maganar da kai, domin su amince da kai koyaushe.” Sa’an nan Musa ya faɗa wa Ubangiji abin da mutane suka ce.
The Lord said to him: Lo, now will I come to thee in the darkness of a cloud, that the people may hear me speaking to thee, and may believe thee for ever. And Moses told the words of the people to the Lord.
10 Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Tafi wurin mutanen, ka tsarkake su yau da gobe, ka sa su wanke tufafinsu.
And he said to him: Go to the people, and sanctify them today, and tomorrow, and let them wash their garments.
11 Su zama da shiri a rana ta uku, gama a ranar ce Ubangiji zai sauko a kan Dutsen Sinai a idon dukan mutane.
And let them be ready against the third day: for on the third day the Lord will come down in the sight of all the people upon mount Sinai.
12 Sai ka yi wa jama’a iyaka kewaye da dutsen, ka kuma faɗa musu cewa, ‘Ku mai da hankali, kada ku hau dutsen ko ku taɓa gefensa. Duk wanda ya taɓa dutsen, lalle za a kashe shi.
And thou shalt appoint certain limits to the people round about, and thou shalt say to them: Take heed you go not up into the mount, and that ye touch not the borders thereof: every one that toucheth the mount dying he shall die.
13 Za a jajjefe shi da duwatsu, ko a harbe shi da kibiyoyi, ba hannun da zai taɓa shi. Mutum ko dabbar da ya taɓa, ba za a bar shi da rai ba.’ Lokacin da aka ji muryar ƙaho ne kawai za su iya taru a gindin dutsen.”
No hands shall touch him, but he shall be stoned to death, or shall be shot through with arrows: whether it be beast, or man, he shall not live. When the trumpet shall begin to sound, then let them go up into the mount.
14 Bayan da Musa ya gangara wurin mutane, ya tsarkake su, sai suka wanke tufafinsu.
And Moses came down from the mount to the people, and sanctified them. And when they had washed their garments,
15 Sa’an nan ya ce wa mutane, “Ku shirya kanku domin rana ta uku. Ku ƙame kanku daga yin jima’i.”
He said to them: Be ready against the third day, and come not near your wives.
16 A safiyar rana ta uku, aka yi tsawa, da walƙiyoyi, sai ga girgije mai duhu a bisa dutsen, aka tsananta busar ƙaho, sai dukan jama’ar da suke cikin sansani suka yi rawar jiki.
And now the third day was come, and the morning appeared: and behold thunders began to be heard, and lightning to flash, and a very thick cloud to cover the mount, and the noise of the trumpet sounded exceeding loud, and the people that was in the camp, feared.
17 Sa’an nan Musa ya jagoranci mutane daga sansani domin su sadu da Allah, sai suka tsaya a gefen dutsen.
And when Moses had brought them forth to meet God from the place of the camp, they stood at the bottom of the mount.
18 Dutsen Sinai kuwa ya tunnuƙe duka da hayaƙi, gama Ubangiji ya sauko a bisan dutsen cikin wuta. Hayaƙin ya hau kamar hayaƙin da yake fitowa daga matoya, duk dutsen ya yi rawa da ƙarfi,
And all mount Sinai was on a smoke: because the Lord was come down upon it in fire, and the smoke arose from it as out of a furnace: and all the mount was terrible.
19 sai karar ƙaho ya yi ta ƙaruwa. Sa’an nan Musa ya yi magana, murya Allah kuwa ta amsa masa.
And the sound of the trumpet grew by degrees louder and louder, and was drawn out to a greater length: Moses spoke, and God answered him.
20 Ubangiji ya sauko a kan ƙwanƙolin Dutsen Sinai, ya kira Musa zuwa ƙwanƙolin dutsen. Musa kuwa ya haura
And the Lord came down upon mount Sinai, in the very top of the mount, and he called Moses unto the top thereof. And when he was gone up thither,
21 sai Ubangiji ya ce masa, “Ka sauka ka faɗa wa jama’a, kada su kuskura su ƙetare layin iyakan nan, garin son zuwa don ganin Ubangiji, gama duk waɗanda suka yi haka za su mutu.
He said unto him: Go down, and charge the people: lest they should have a mind to pass the limits to see the Lord, and a very great multitude of them should perish.
22 Ko firistocin da za su kusato Ubangiji sai su tsarkake kansu, don kada in hallaka su.”
The priests also that come to the Lord, let them be sanctified, lest he strike them.
23 Musa ya ce wa Ubangiji, “Mutanen ba za su hau Dutsen Sinai ba, gama kai da kanka ka gargaɗe mu, ‘Ku sa iyaka kewaye da dutsen ku kuma tsarkake shi.’”
And Moses said to the Lord: The people cannot come up to mount Sinai: for thou did charge, and command, saying: Set limits about the mount, and sanctify it.
24 Ubangiji ya amsa, “Sauka ka kawo Haruna tare da kai. Amma kada firistoci da mutane su zarce iyakan nan, a kan za su zo wurin Ubangiji, don kada in hallaka su.”
And the Lord said to him: Go, get thee down: and thou shalt come up, thou and Aaron with thee: but let not the priests and the people pass the limits, nor come up to the Lord, lest he kill them.
25 Saboda haka Musa ya sauka wurin mutane ya kuma faɗa musu.
And Moses went down to the people and told them all.

< Fitowa 19 >