< Fitowa 19 >

1 A rana ta farko a cikin watan uku bayan da Isra’ilawa suka bar Masar, a wannan rana, suka iso Hamadar Sinai.
I den tredje Måned efter Israeliternes Udvandring af Ægypten, på denne Dag nåede de Sinaj Ørken.
2 Bayan da suka tashi daga Refidim, suka shiga Hamadar Sinai, sai Isra’ilawa suka yi sansani a gaban dutsen.
De brød op fra Refdim og kom til Sinaj Ørken og slog Lejr i Ørkenen. Der slog. Israel Lejr lige over for Bjerget,
3 Sai Musa ya hau kan dutsen don yă sadu da Allah, Ubangiji kuwa ya kira shi daga dutsen ya ce, “Wannan shi ne abin da za ka faɗa wa gidan Yaƙub, da kuma abin da za ka faɗa wa mutanen Isra’ila.
men Moses steg op til Gud. Da råbte HERREN til ham fra Bjerget: "Dette skal du sige til Jakobs Hus og kundgøre for Israels Børn:
4 ‘Ku da kanku kun ga abin da na yi wa Masar, da yadda na ɗauko ku a kan fikafikan gaggafa na kawo ku wurina.
I har set, hvad jeg gjorde ved Ægypterne, og hvorledes jeg bar eder på Ørnevinger og bragte eder hid til mig.
5 Yanzu, in kuka yi mini cikakken biyayya, kuka kuma kiyaye yarjejjeniyata, to, za ku zama keɓeɓɓiyar taska a gare ni a cikin dukan al’ummai. Ko da yake duk duniya tawa ce,
Hvis I nu vil lyde min Røst og holde min Pagt, så skal I være min Ejendom blandt alle Folkene, thi mig hører hele Jorden til,
6 za ku zama firistoci masu tsarki da kuma al’umma keɓaɓɓiya a gare ni.’ Waɗannan su ne kalmomin da za ka faɗa wa Isra’ilawa.”
og I skal blive mig et Kongerige af Præster og et helligt Folk! Det er de Ord, du skal tale til Israels Børn!"
7 Sai Musa ya koma ya aika a kira dukan dattawan mutane, ya bayyana dukan kalmomin da Ubangiji ya umarta, ya faɗa.
Da gik Moses hen og kaldte Folkets Ældste sammen og forelagde dem alle disse Ord, som HERREN havde pålagt ham.
8 Dukan mutane suka amsa gaba ɗaya suka ce, “Za mu yi duk abin da Ubangiji ya faɗa.” Sai Musa ya mayar wa Ubangiji amsar da mutane suka bayar.
Og hele Folket svarede, alle som een: "Alt, hvad HERREN har sagt, vil vi gøre!" Da bragte Moses HERREN Folkets Svar.
9 Ubangiji kuwa ya ce wa Musa, “Ina zuwa wurinka a cikin baƙin hadari, domin mutane su ji ni ina maganar da kai, domin su amince da kai koyaushe.” Sa’an nan Musa ya faɗa wa Ubangiji abin da mutane suka ce.
Derpå sagde HERREN til Moses: "Se, jeg vil komme til dig i en tæt Sky, for at Folket kan høre, at jeg taler med dig, og for stedse tro også på dig!" Og Moses kundgjorde HERREN Folkets Svar.
10 Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Tafi wurin mutanen, ka tsarkake su yau da gobe, ka sa su wanke tufafinsu.
Da sagde HERREN til Moses: "Gå til Folket og lad dem hellige sig i Dag og i Morgen og tvætte deres Klæder
11 Su zama da shiri a rana ta uku, gama a ranar ce Ubangiji zai sauko a kan Dutsen Sinai a idon dukan mutane.
og holde sig rede til i Overmorgen, thi i Overmorgen vil HERREN stige ned for alt Folkets Øjne på Sinaj Bjerg.
12 Sai ka yi wa jama’a iyaka kewaye da dutsen, ka kuma faɗa musu cewa, ‘Ku mai da hankali, kada ku hau dutsen ko ku taɓa gefensa. Duk wanda ya taɓa dutsen, lalle za a kashe shi.
Og du skal rundt om spærre af for Folket og sige til dem: Vog eder for at gå op på Bjerget, ja for blot at røre ved Yderkanten deraf; enhver, der rører ved Bjerget, er dødsens!
13 Za a jajjefe shi da duwatsu, ko a harbe shi da kibiyoyi, ba hannun da zai taɓa shi. Mutum ko dabbar da ya taɓa, ba za a bar shi da rai ba.’ Lokacin da aka ji muryar ƙaho ne kawai za su iya taru a gindin dutsen.”
Ingen Hånd må røre ved ham, han skal stenes eller skydes ned; hvad enten det er et Dyr eller et Menneske, skal det miste Livet. Når Væderhornet lyder, skal de stige op på Bjerget."
14 Bayan da Musa ya gangara wurin mutane, ya tsarkake su, sai suka wanke tufafinsu.
Så steg Moses ned fra Bjerget til Folket og lod Folket hellige sig, og de tvættede deres Klæder;
15 Sa’an nan ya ce wa mutane, “Ku shirya kanku domin rana ta uku. Ku ƙame kanku daga yin jima’i.”
og han sagde til Folket: Hold eder rede til i Overmorgen, ingen må komme en Kvinde nær!"
16 A safiyar rana ta uku, aka yi tsawa, da walƙiyoyi, sai ga girgije mai duhu a bisa dutsen, aka tsananta busar ƙaho, sai dukan jama’ar da suke cikin sansani suka yi rawar jiki.
Da Morgenen gryede den tredje Dag, begyndte det at tordne og lyne, og en tung Sky lagde sig over Bjerget, og der hørtes vældige Stød i Horn. Da skælvede alt Folket i Lejren.
17 Sa’an nan Musa ya jagoranci mutane daga sansani domin su sadu da Allah, sai suka tsaya a gefen dutsen.
Så førte Moses Folket fra Lejren hen for Gud, og de stillede sig neden for Bjerget.
18 Dutsen Sinai kuwa ya tunnuƙe duka da hayaƙi, gama Ubangiji ya sauko a bisan dutsen cikin wuta. Hayaƙin ya hau kamar hayaƙin da yake fitowa daga matoya, duk dutsen ya yi rawa da ƙarfi,
Men hele Sinaj Bjerg hylledes i Røg, fordi HERREN steg ned derpå i Ild, og Røgen stod i Vejret som Røg fra en Smelteovn; og hele Folket skælvede så1e.
19 sai karar ƙaho ya yi ta ƙaruwa. Sa’an nan Musa ya yi magana, murya Allah kuwa ta amsa masa.
Og Stødene i Hornene blev stærkere og stærkere; Moses talte, og Gud svarede ham med høj Røst.
20 Ubangiji ya sauko a kan ƙwanƙolin Dutsen Sinai, ya kira Musa zuwa ƙwanƙolin dutsen. Musa kuwa ya haura
Og da HERREN var steget ned på Sinaj Bjerg, på Toppen af Bjerget, kaldte han Moses op på Toppen af Bjerget, og Moses steg derop.
21 sai Ubangiji ya ce masa, “Ka sauka ka faɗa wa jama’a, kada su kuskura su ƙetare layin iyakan nan, garin son zuwa don ganin Ubangiji, gama duk waɗanda suka yi haka za su mutu.
Da sagde HERREN til Moses: "Stig ned og indskærp Folket, at de ikke må trænge sig frem til HERREN for at se ham, at der ikke skal ske et stort Mandefald iblandt dem.
22 Ko firistocin da za su kusato Ubangiji sai su tsarkake kansu, don kada in hallaka su.”
Selv Præsterne, som ellers træder frem for HERREN, skal hellige sig, for at ikke HERREN skal tynde ud i deres Rækker."
23 Musa ya ce wa Ubangiji, “Mutanen ba za su hau Dutsen Sinai ba, gama kai da kanka ka gargaɗe mu, ‘Ku sa iyaka kewaye da dutsen ku kuma tsarkake shi.’”
Da sagde Moses til HERREN: "Folket kan jo ikke stige op på Sinaj Bjerg, thi du har selv indskærpet os at afspærre Bjerget og hellige det."
24 Ubangiji ya amsa, “Sauka ka kawo Haruna tare da kai. Amma kada firistoci da mutane su zarce iyakan nan, a kan za su zo wurin Ubangiji, don kada in hallaka su.”
Men HERREN sagde til ham: "Stig nu ned og kom atter herop sammen med Aron; men Præsterne og Folket må ikke trænge sig frem for at komme op til HERREN, at han ikke skal tynde ud i deres Rækker."
25 Saboda haka Musa ya sauka wurin mutane ya kuma faɗa musu.
Da steg Moses ned til Folket og sagde det til dem.

< Fitowa 19 >