< Fitowa 18 >
1 Ana nan sai Yetro firist na Midiyan, kuma surukin Musa, ya ji duk abin da Allah ya yi wa Musa da mutanensa Isra’ila, da kuma yadda Ubangiji ya fitar da Isra’ila daga Masar.
UJethro, umphristi waseMidiyani owayenguyisezala kaMosi, wezwa konke uNkulunkulu ayekwenzele uMosi labantu bakhe bako-Israyeli, lokuthi uThixo wayebakhuphe njani eGibhithe abako-Israyeli.
2 Bayan da Musa ya tura matarsa Ziffora gida, sai surukinsa Yetro ya karɓe ta
Ngemva kokuba uMosi esethumele umkakhe uZiphora kibo, uyisezala uJethro wamemukela,
3 da’ya’yanta biyu maza. Ana kira ɗaya Gershom, domin Musa ya ce, “Na zama baƙo a baƙuwar ƙasa”;
lamadodana akhe amabili. Eyinye indodana kwakuthiwa nguGeshomu, ngoba uMosi wathi, “Sengibe ngumuntu wezizweni elizweni elingayisilo lami.”
4 ɗayan kuma Eliyezer, domin ya ce, “Allah mahaifina ya taimake ni ya cece ni daga takobin Fir’auna.”
Eyinye kwakuthiwa ngu-Eliyezari ngoba wathi, “UNkulunkulu kababa wayengumsizi wami: wangisindisa enkembeni kaFaro.”
5 Yetro surukin Musa tare da’ya’yan Musa da matarsa suka zo wurin Musa a hamada, inda suka kafa sansani kusa da dutsen Allah
UJethro, uyisezala kaMosi kanye lamadodana lenkosikazi kaMosi beza kuye enkangala lapho ayehlala khona eduzane lentaba kaNkulunkulu.
6 Yetro ya riga ya aika wa Musa cewa, “Ni surukinka Yetro, ina zuwa wurinka tare da matarka da’ya’yanka maza biyu.”
UJethro wayethumele ilizwi kuye wathi, “Mina uyihlozala uJethro ngiyeza kuwe lenkosikazi yakho lamadodana ayo amabili.”
7 Sai Musa ya tafi yă taryi surukinsa, ya sunkuya ya yi masa sumba. Suka gai da juna, sa’an nan suka shiga tenti.
Ngakho uMosi waphuma wayahlangabeza uyisezala wasemkhothamela, wamanga. Babingelelana basebengena ethenteni.
8 Musa kuwa ya faɗa wa surukinsa duk abubuwan da Ubangiji ya yi wa Fir’auna da Masarawa domin Isra’ila, da batun wahalolin da suka sha a hanya, da yadda Ubangiji ya cece su.
UMosi watshela uyisezala ngakho konke uThixo ayekwenze kuFaro labantu baseGibhithe ngenxa yabantu bako-Israyeli langezinhlupho zonke ezabehlela endleleni lokuthi uThixo wayebasindise njani.
9 Yetro ya yi murna da jin duk abubuwa masu kyau da Ubangiji ya yi wa Isra’ila, wajen cetonsu daga hannun Masarawa.
UJethro wathokoza ukuzwa ngezinto zonke ezinhle uThixo ayezenzele u-Israyeli ekubasindiseni esandleni samaGibhithe.
10 “Yabo ga Ubangiji wanda ya cece ku daga hannun Masarawa da na Fir’auna, wanda kuma ya cece mutanensa daga hannun Masarawa.
Wathi, “Kadunyiswe uThixo owalisindisa esandleni samaGibhithe loFaro, njalo owasindisa abantu esandleni samaGibhithe.
11 Yanzu na san cewa Ubangiji ya fi kowane allah, gama ya yi wannan ga masu girman kai da kuma waɗanda suka wulaƙanta Isra’ila.”
Khathesi sengikwazi ukuthi uThixo ulamandla ukwedlula abanye onkulunkulu ngenxa yokuthi wenza lokhu kubo bonke abaphatha u-Israyeli ngobuqholo.”
12 Sa’an nan Yetro surukin Musa, ya kawo hadaya ta ƙonawa da waɗansu hadayu wa Allah, Haruna ya zo tare da dukan dattawan Isra’ila, suka ci abinci tare da surukin Musa a gaban Allah.
Lapho-ke uJethro, uyisezala kaMosi, waletha umnikelo wokutshiswa leminye imihlatshelo kuNkulunkulu, njalo u-Aroni weza labadala bako-Israyeli ukuze bazokudla isinkwa loyisezala kaMosi phambi kukaNkulunkulu.
13 Kashegari, Musa ya zauna domin yă yi wa mutane shari’a, sai suka tsaya kewaye da shi daga safe har yamma.
Ngelanga elilandelayo uMosi wathatha isihlalo sakhe sokuba ngumthonisi wabantu, njalo bema bemgombolozele kusukela ekuseni kwaze kwaba ntambama.
14 Sa’ad da surukinsa ya lura da duk abin da Musa yake yi saboda mutane, sai ya ce, “Mene ne wannan da kake yi wa mutane? Don me kai kaɗai kake zama kana yin shari’a wa mutane, yayinda mutanen nan suke tsaya kewaye da kai daga safe har yamma?”
Kwathi uyisezala esebone konke uMosi ayekwenzela abantu wathi, “Kuyini lokhu okwenzela abantu? Kungani uhlala unguwe wedwa ukuba ngumahluli, abantu bonke bemi bekuhanqile kusukela ekuseni kuze kube kusihlwa?”
15 Musa ya amsa ya ce, “Saboda mutanen suna zuwa wurina, don su nemi nufin Allah.
UMosi wamphendula wathi, “Ngenxa yokuthi abantu beza kimi ukuzodinga intando kaNkulunkulu.
16 Duk lokacin da suke da gardama, akan kawo su a wurina, ni kuma sai in raba tsakaninsu, in kuma koya musu dokokin Allah da farillansa.”
Lapho kusiba lengxabano, ilethwa kimi, njalo ngiyahlulela emaceleni womabili besengibatshela ngemithetho lemilayo kaNkulunkulu.”
17 Surukin Musa ya amsa ya ce, “Abin da kake yi ba daidai ba ne.
Uyisezala kaMosi waphendula wathi, “Konke okwenzayo kakulunganga.
18 Kai da dukan mutanen da suke zuwa wurinka za ku gajiyar da kanku. Aikin ya fi ƙarfinka; ba za ka iya yinsa kai kaɗai ba.
Wena labantu laba abeza kuwe lizazidinisa. Umsebenzi lo unzima kuwe: ungeke wawenza wedwa.
19 Ka kasa kunne gare ni yanzu, zan ba ka shawara, Allah kuma yă kasance tare da kai. Kai za ka zama wakilin mutane a gaban Allah, ka kuma kawo gardamansu gare shi.
Ngilalela ngikucebise, njalo uNkulunkulu makabe lawe. Kumele ube ngummeli wabantu kuNkulunkulu, ulethe ingxabano zabo kuye.
20 Ka koya musu dokokinsa da farillarsa, ka kuma nuna musu hanyar rayuwa da ayyukan da za su yi.
Bafundise izimiso lemithetho yakhe, ubatshengise indlela yokuphila lokuthi baziphathe njani.
21 Amma ka zaɓi mutane masu iyawa daga dukan mutane, maza masu tsoron Allah, amintattu, masu ƙin rashawa, ka sanya su shugabanni na dubbai, ɗari-ɗari, hamsin-hamsin da goma-goma.
Kodwa khetha amadoda alamandla phakathi kwabantu bonke, amadoda amesabayo uNkulunkulu, azonda inzuzo eza ngobuqili, ubusubabeka babe zinduna zezinkulungwane, zamakhulu, zamatshumi amahlanu, lezamatshumi.
22 Bari waɗannan mutane su sassanta mutane a kan ƙananan matsaloli, amma kowace babban matsala, ko bukata ta musamman, sai su kawo wurinka, ƙananan matsaloli kuma sai su yanke hukuncin da kansu. Ta haka ne za su taimaka wajen ɗaukan nauyin jama’a, don su sa aikin yă zama maka da sauƙi.
Benze babe ngabahluleli babantu ngezikhathi zonke, kodwa kabalethe wonke amacala anzima kuwe bona baqume amacala alula. Lokho kuzakwenza ukuthi umthwalo wakho ube lula ngoba bazabe besabelana lawe.
23 In ka yi haka, Allah ya umarta za ka iya jimre gajiyar, kuma dukan mutanen nan za su koma gida da murna.”
Nxa ungakwenza lokhu njengokulaya kukaNkulunkulu, uzakwenelisa ukuphumuza ingqondo njalo abantu bonke laba bazabuyela emakhaya besuthisekile.”
24 Musa ya kasa kunne ga surukinsa, ya kuma aikata duk abin da ya faɗa.
UMosi wamlalela uyisezala wenza konke ayekutshilo.
25 Ya zaɓi mutane masu iyawa daga cikin dukan Isra’ila, ya naɗa su shugabannin mutane, shugabanni a kan dubbai, ɗari-ɗari, hamsin-hamsin da goma-goma.
Wakhetha amadoda alamandla phakathi kwabako-Israyeli wonke wawenza abakhokheli babantu, izinduna zezinkulungwane, ezamakhulu, ezamatshumi amahlanu lezamatshumi.
26 Suka yi hidimar alƙalanci na mutane a dukan lokaci. Gardandamin da suke da wuya, suka kawo wurin Musa, amma ƙananan batuttuwa, suka shari’anta a tsakaninsu.
Baba ngabahluleli babantu ngazozonke izikhathi. Amacala anzima bawaletha kuMosi, kodwa alula bawathonisa bona ngokwabo.
27 Sa’an nan Musa ya sallame surukinsa Yetro, ya kuwa koma ƙasarsa.
UMosi wavalelisana loyisezala, uJethro wasebuyela elizweni lakhe.