< Fitowa 18 >

1 Ana nan sai Yetro firist na Midiyan, kuma surukin Musa, ya ji duk abin da Allah ya yi wa Musa da mutanensa Isra’ila, da kuma yadda Ubangiji ya fitar da Isra’ila daga Masar.
Or, quand Jéthro prêtre de Madian, parent de Moïse, eut appris tout ce que Dieu avait fait à Moïse et à Israël son peuple, et que le Seigneur avait retiré Israël de l’Egypte,
2 Bayan da Musa ya tura matarsa Ziffora gida, sai surukinsa Yetro ya karɓe ta
Il prit Séphora femme de Moïse, que celui-ci lui avait renvoyée,
3 da’ya’yanta biyu maza. Ana kira ɗaya Gershom, domin Musa ya ce, “Na zama baƙo a baƙuwar ƙasa”;
Et ses deux fils dont l’un s’appelait Gersam, son père ayant dit: J’ai été voyageur dans une terre étrangère;
4 ɗayan kuma Eliyezer, domin ya ce, “Allah mahaifina ya taimake ni ya cece ni daga takobin Fir’auna.”
Et l’autre Eliézer; car le Dieu de mon père, avait-il dit, fut mon aide, et il m’a délivré du glaive de Pharaon.
5 Yetro surukin Musa tare da’ya’yan Musa da matarsa suka zo wurin Musa a hamada, inda suka kafa sansani kusa da dutsen Allah
Jéthro donc, parent de Moïse, vint, ainsi que ses fils et sa femme, vers Moïse dans le désert, où il avait campé près de la montagne de Dieu.
6 Yetro ya riga ya aika wa Musa cewa, “Ni surukinka Yetro, ina zuwa wurinka tare da matarka da’ya’yanka maza biyu.”
Et il envoya vers Moïse, disant: Moi Jéthro ton parent, je viens à toi, ainsi que ta femme et tes deux fils avec elle.
7 Sai Musa ya tafi yă taryi surukinsa, ya sunkuya ya yi masa sumba. Suka gai da juna, sa’an nan suka shiga tenti.
Moïse étant sorti au-devant de son parent, se prosterna et l’embrassa; et ils se saluèrent mutuellement par des paroles de paix. Et lorsque Jéthro fut entré dans la tente,
8 Musa kuwa ya faɗa wa surukinsa duk abubuwan da Ubangiji ya yi wa Fir’auna da Masarawa domin Isra’ila, da batun wahalolin da suka sha a hanya, da yadda Ubangiji ya cece su.
Moïse raconta à son parent tout ce qu’avait fait le Seigneur à Pharaon et aux Egyptiens à cause d’Israël, et toute la peine qui lui était arrivée dans le chemin!, et que le Seigneur les avait délivrés.
9 Yetro ya yi murna da jin duk abubuwa masu kyau da Ubangiji ya yi wa Isra’ila, wajen cetonsu daga hannun Masarawa.
Et Jéthro se réjouit de tous les biens qu’avait faits le Seigneur à Israël, de ce qu’il l’avait délivré de la main des Egyptiens,
10 “Yabo ga Ubangiji wanda ya cece ku daga hannun Masarawa da na Fir’auna, wanda kuma ya cece mutanensa daga hannun Masarawa.
Et il dit: Béni le Seigneur, qui vous a délivrés de la main des Egyptiens, et de la main de Pharaon; qui a délivré son peuple de la main de l’Egypte.
11 Yanzu na san cewa Ubangiji ya fi kowane allah, gama ya yi wannan ga masu girman kai da kuma waɗanda suka wulaƙanta Isra’ila.”
Maintenant je connais que le Seigneur est grand au-dessus de tous les dieux, parce que c’est en vain qu’ils ont agi insolemment contre eux.
12 Sa’an nan Yetro surukin Musa, ya kawo hadaya ta ƙonawa da waɗansu hadayu wa Allah, Haruna ya zo tare da dukan dattawan Isra’ila, suka ci abinci tare da surukin Musa a gaban Allah.
Jéthro donc, parent de Moïse, offrit des holocaustes et des hosties à Dieu, et Aaron et tous les anciens d’Israël vinrent pour manger du pain avec lui devant Dieu.
13 Kashegari, Musa ya zauna domin yă yi wa mutane shari’a, sai suka tsaya kewaye da shi daga safe har yamma.
Or, le jour suivant Moïse s’assit pour juger le peuple, qui se présentait devant Moïse depuis le matin jusqu’au soir.
14 Sa’ad da surukinsa ya lura da duk abin da Musa yake yi saboda mutane, sai ya ce, “Mene ne wannan da kake yi wa mutane? Don me kai kaɗai kake zama kana yin shari’a wa mutane, yayinda mutanen nan suke tsaya kewaye da kai daga safe har yamma?”
Ce qu’ayant vu le parent de Moïse, c’est-à-dire, tout ce qu’il faisait avec le peuple, il dit: Qu’est-ce que tu fais avec le peuple? pourquoi es-tu seul assis, et le peuple attend-il depuis le matin jusqu’au soir?
15 Musa ya amsa ya ce, “Saboda mutanen suna zuwa wurina, don su nemi nufin Allah.
Moïse lui répondit: Le peuple vient à moi demandant le jugement de Dieu;
16 Duk lokacin da suke da gardama, akan kawo su a wurina, ni kuma sai in raba tsakaninsu, in kuma koya musu dokokin Allah da farillansa.”
Car lorsqu’il leur arrive quelque différend, ils viennent à moi, afin que je juge entre eux et que je leur montre les préceptes de Dieu et ses lois.
17 Surukin Musa ya amsa ya ce, “Abin da kake yi ba daidai ba ne.
Mais celui-ci: Tu ne fais pas, dit-il, une bonne chose:
18 Kai da dukan mutanen da suke zuwa wurinka za ku gajiyar da kanku. Aikin ya fi ƙarfinka; ba za ka iya yinsa kai kaɗai ba.
Par cet imprudent labeur tu te consumes, toi et tout ce peuple qui est avec toi: l’affaire surpasse tes forces; seul, tu ne pourras pas la soutenir.
19 Ka kasa kunne gare ni yanzu, zan ba ka shawara, Allah kuma yă kasance tare da kai. Kai za ka zama wakilin mutane a gaban Allah, ka kuma kawo gardamansu gare shi.
Mais écoute mes paroles et mes conseils, et Dieu sera avec toi. Sois toi-même au peuple dans les choses qui regardent Dieu, pour rapporter les paroles qui lui sont adressées;
20 Ka koya musu dokokinsa da farillarsa, ka kuma nuna musu hanyar rayuwa da ayyukan da za su yi.
Et pour montrer au peuple les cérémonies et la manière de l’honorer, et la voie dans laquelle ils doivent entrer et l’œuvre qu’ils doivent accomplir.
21 Amma ka zaɓi mutane masu iyawa daga dukan mutane, maza masu tsoron Allah, amintattu, masu ƙin rashawa, ka sanya su shugabanni na dubbai, ɗari-ɗari, hamsin-hamsin da goma-goma.
Mais choisis d’entre tout le peuple des hommes valeureux, et craignant Dieu, en qui soit la vérité, et qui haïssent l’avarice, et fais-en des tribuns, des chefs de cent, de cinquante et de dix hommes;
22 Bari waɗannan mutane su sassanta mutane a kan ƙananan matsaloli, amma kowace babban matsala, ko bukata ta musamman, sai su kawo wurinka, ƙananan matsaloli kuma sai su yanke hukuncin da kansu. Ta haka ne za su taimaka wajen ɗaukan nauyin jama’a, don su sa aikin yă zama maka da sauƙi.
Qu’ils jugent le peuple en tout temps: qu’ils te rapportent tout ce qui sera plus important, et qu’eux-mêmes jugent seulement les affaires moins considérables; alors la charge sera plus légère pour toi, le fardeau étant partagé avec d’autres.
23 In ka yi haka, Allah ya umarta za ka iya jimre gajiyar, kuma dukan mutanen nan za su koma gida da murna.”
Si tu fais cela, tu rempliras l’ordre de Dieu, et tu pourras exécuter ses préceptes: et tout ce peuple retournera dans ses demeures en paix.
24 Musa ya kasa kunne ga surukinsa, ya kuma aikata duk abin da ya faɗa.
Ces conseils entendus, Moïse fit tout ce que Jéthro lui avait suggéré.
25 Ya zaɓi mutane masu iyawa daga cikin dukan Isra’ila, ya naɗa su shugabannin mutane, shugabanni a kan dubbai, ɗari-ɗari, hamsin-hamsin da goma-goma.
Et ayant choisi des hommes vaillants de tout Israël, il les établit princes du peuple, tribuns, chefs de cent, de cinquante et de dix hommes.
26 Suka yi hidimar alƙalanci na mutane a dukan lokaci. Gardandamin da suke da wuya, suka kawo wurin Musa, amma ƙananan batuttuwa, suka shari’anta a tsakaninsu.
Ils jugeaient le peuple en tout temps: mais ils rapportaient à Moïse tout ce qui était plus grave, jugeant seulement les affaires les plus faciles.
27 Sa’an nan Musa ya sallame surukinsa Yetro, ya kuwa koma ƙasarsa.
Et Moïse laissa aller son parent, qui s’en retournant alla en son pays.

< Fitowa 18 >