< Fitowa 18 >
1 Ana nan sai Yetro firist na Midiyan, kuma surukin Musa, ya ji duk abin da Allah ya yi wa Musa da mutanensa Isra’ila, da kuma yadda Ubangiji ya fitar da Isra’ila daga Masar.
And he heard Jethro [the] priest of Midian [the] father-in-law of Moses all that he had done God for Moses and for Israel people his that he had brought out Yahweh Israel from Egypt.
2 Bayan da Musa ya tura matarsa Ziffora gida, sai surukinsa Yetro ya karɓe ta
And he had taken Jethro [the] father-in-law of Moses Zipporah [the] wife of Moses after dismissal her.
3 da’ya’yanta biyu maza. Ana kira ɗaya Gershom, domin Musa ya ce, “Na zama baƙo a baƙuwar ƙasa”;
And [the] two sons her who [the] name of the one [was] Gershom for he had said a sojourner I have become in a land foreign.
4 ɗayan kuma Eliyezer, domin ya ce, “Allah mahaifina ya taimake ni ya cece ni daga takobin Fir’auna.”
And [the] name of the one [was] Eliezer for [the] God of father my [has been] help my and he has delivered me from [the] sword of Pharaoh.
5 Yetro surukin Musa tare da’ya’yan Musa da matarsa suka zo wurin Musa a hamada, inda suka kafa sansani kusa da dutsen Allah
And he came Jethro [the] father-in-law of Moses and sons his and wife his to Moses into the wilderness where he [was] encamped there [the] mountain of God.
6 Yetro ya riga ya aika wa Musa cewa, “Ni surukinka Yetro, ina zuwa wurinka tare da matarka da’ya’yanka maza biyu.”
And he said to Moses I father-in-law your Jethro [am] coming to you and wife your and [the] two sons her with her.
7 Sai Musa ya tafi yă taryi surukinsa, ya sunkuya ya yi masa sumba. Suka gai da juna, sa’an nan suka shiga tenti.
And he went out Moses to meet father-in-law his and he bowed down and he kissed him and they asked each of neighbor his to welfare and they went the tent towards.
8 Musa kuwa ya faɗa wa surukinsa duk abubuwan da Ubangiji ya yi wa Fir’auna da Masarawa domin Isra’ila, da batun wahalolin da suka sha a hanya, da yadda Ubangiji ya cece su.
And he recounted Moses to father-in-law his all that he had done Yahweh to Pharaoh and to Egypt on [the] causes of Israel all the hardship which it had come upon them on the journey and he had delivered them Yahweh.
9 Yetro ya yi murna da jin duk abubuwa masu kyau da Ubangiji ya yi wa Isra’ila, wajen cetonsu daga hannun Masarawa.
And he rejoiced Jethro on all the good which he had done Yahweh to Israel whom he had delivered it from [the] hand of Egypt.
10 “Yabo ga Ubangiji wanda ya cece ku daga hannun Masarawa da na Fir’auna, wanda kuma ya cece mutanensa daga hannun Masarawa.
And he said Jethro [be] blessed Yahweh who he has delivered you from [the] hand of Egypt and from [the] hand of Pharaoh who he has delivered the people from under [the] hand of Egypt.
11 Yanzu na san cewa Ubangiji ya fi kowane allah, gama ya yi wannan ga masu girman kai da kuma waɗanda suka wulaƙanta Isra’ila.”
Now I know that [is] great Yahweh more than all the gods for in the matter which they have acted presumptuously on them.
12 Sa’an nan Yetro surukin Musa, ya kawo hadaya ta ƙonawa da waɗansu hadayu wa Allah, Haruna ya zo tare da dukan dattawan Isra’ila, suka ci abinci tare da surukin Musa a gaban Allah.
And he took Jethro [the] father-in-law of Moses a burnt offering and sacrifices to God and he came Aaron and all - [the] elders of Israel to eat food with [the] father-in-law of Moses before God.
13 Kashegari, Musa ya zauna domin yă yi wa mutane shari’a, sai suka tsaya kewaye da shi daga safe har yamma.
And it was from [the] next day and he sat Moses to judge the people and it stood the people at Moses from the morning until the evening.
14 Sa’ad da surukinsa ya lura da duk abin da Musa yake yi saboda mutane, sai ya ce, “Mene ne wannan da kake yi wa mutane? Don me kai kaɗai kake zama kana yin shari’a wa mutane, yayinda mutanen nan suke tsaya kewaye da kai daga safe har yamma?”
And he saw [the] father-in-law of Moses all that he [was] doing for the people and he said what? [is] the thing this which you [are] doing for the people why? [are] you sitting to alone you and all the people [is] standing at you from morning until evening.
15 Musa ya amsa ya ce, “Saboda mutanen suna zuwa wurina, don su nemi nufin Allah.
And he said Moses to father-in-law his thatr it comes to me the people to consult God.
16 Duk lokacin da suke da gardama, akan kawo su a wurina, ni kuma sai in raba tsakaninsu, in kuma koya musu dokokin Allah da farillansa.”
For it will be[long] to them a matter [it is] coming to me and I judge between each and between neighbor his and I make known [the] statutes of God and laws his.
17 Surukin Musa ya amsa ya ce, “Abin da kake yi ba daidai ba ne.
And he said [the] father-in-law of Moses to him not [is] good the thing which you [are] doing.
18 Kai da dukan mutanen da suke zuwa wurinka za ku gajiyar da kanku. Aikin ya fi ƙarfinka; ba za ka iya yinsa kai kaɗai ba.
Certainly you will wear yourself out both you as well as the people this which [is] with you for [is too] heavy for you the thing not you are able to do it to alone you.
19 Ka kasa kunne gare ni yanzu, zan ba ka shawara, Allah kuma yă kasance tare da kai. Kai za ka zama wakilin mutane a gaban Allah, ka kuma kawo gardamansu gare shi.
Now listen to voice my let me advise you and may he be God with you be you for the people in front of God and you will bring you the matters to God.
20 Ka koya musu dokokinsa da farillarsa, ka kuma nuna musu hanyar rayuwa da ayyukan da za su yi.
And you will warn them the statutes and the laws and you will make known to them the way [which] they will walk in it and the work which they will do!
21 Amma ka zaɓi mutane masu iyawa daga dukan mutane, maza masu tsoron Allah, amintattu, masu ƙin rashawa, ka sanya su shugabanni na dubbai, ɗari-ɗari, hamsin-hamsin da goma-goma.
And you you will provide from all the people men of ability [those] fearing God men of faithfulness [who] hate unjust gain and you will appoint over them officials of thousands officials of hundreds officials of fifties and officials of tens.
22 Bari waɗannan mutane su sassanta mutane a kan ƙananan matsaloli, amma kowace babban matsala, ko bukata ta musamman, sai su kawo wurinka, ƙananan matsaloli kuma sai su yanke hukuncin da kansu. Ta haka ne za su taimaka wajen ɗaukan nauyin jama’a, don su sa aikin yă zama maka da sauƙi.
And they will judge the people at every time and it will be every matter great they will bring to you and every matter small they will judge they and lighten from on yourself and they will bear with you.
23 In ka yi haka, Allah ya umarta za ka iya jimre gajiyar, kuma dukan mutanen nan za su koma gida da murna.”
If the thing this you will do and he will command you God and you will be able to endure and also all the people this to place its it will go in peace.
24 Musa ya kasa kunne ga surukinsa, ya kuma aikata duk abin da ya faɗa.
And he listened Moses to [the] voice father-in-law his and he did all that he had said.
25 Ya zaɓi mutane masu iyawa daga cikin dukan Isra’ila, ya naɗa su shugabannin mutane, shugabanni a kan dubbai, ɗari-ɗari, hamsin-hamsin da goma-goma.
And he chose Moses men of ability from all Israel and he appointed them chiefs over the people of icials of thousands officials of hundreds officials of fifties and officials of tens.
26 Suka yi hidimar alƙalanci na mutane a dukan lokaci. Gardandamin da suke da wuya, suka kawo wurin Musa, amma ƙananan batuttuwa, suka shari’anta a tsakaninsu.
And they judged the people at every time the matter difficult they brought! to Moses and every matter small they judged they.
27 Sa’an nan Musa ya sallame surukinsa Yetro, ya kuwa koma ƙasarsa.
And he sent off Moses father-in-law his and he went himself to land his.