< Fitowa 18 >
1 Ana nan sai Yetro firist na Midiyan, kuma surukin Musa, ya ji duk abin da Allah ya yi wa Musa da mutanensa Isra’ila, da kuma yadda Ubangiji ya fitar da Isra’ila daga Masar.
Moses' father-in-law Jethro, the priest of Midian, heard about everything God had done for Moses and his people the Israelites, and how the Lord had led them out of Egypt.
2 Bayan da Musa ya tura matarsa Ziffora gida, sai surukinsa Yetro ya karɓe ta
When Moses had sent home his wife Zipporah, his father-in-law Jethro had welcomed her,
3 da’ya’yanta biyu maza. Ana kira ɗaya Gershom, domin Musa ya ce, “Na zama baƙo a baƙuwar ƙasa”;
together with her two sons. One son was named Gershom, for Moses had said, “I have been a foreigner in a foreign land.”
4 ɗayan kuma Eliyezer, domin ya ce, “Allah mahaifina ya taimake ni ya cece ni daga takobin Fir’auna.”
The other son was named Eliezer, because Moses had said, “The God of my father was my helper, and saved me from death at Pharaoh's hand.”
5 Yetro surukin Musa tare da’ya’yan Musa da matarsa suka zo wurin Musa a hamada, inda suka kafa sansani kusa da dutsen Allah
Moses' father-in-law Jethro, together with Moses' wife and sons, came to see him in the desert at the camp near the mountain of God.
6 Yetro ya riga ya aika wa Musa cewa, “Ni surukinka Yetro, ina zuwa wurinka tare da matarka da’ya’yanka maza biyu.”
Moses was told beforehand, “I, your father-in-law Jethro, am coming to see you together with your wife and her two sons.”
7 Sai Musa ya tafi yă taryi surukinsa, ya sunkuya ya yi masa sumba. Suka gai da juna, sa’an nan suka shiga tenti.
Moses went out to meet his father-in-law and bowed down and kissed him. They asked each other how they were and then went into the tent.
8 Musa kuwa ya faɗa wa surukinsa duk abubuwan da Ubangiji ya yi wa Fir’auna da Masarawa domin Isra’ila, da batun wahalolin da suka sha a hanya, da yadda Ubangiji ya cece su.
Moses told his father-in-law about everything the Lord had done to Pharaoh and the Egyptians on behalf of the Israelites, about all the troubles they had experienced on the way, and about how the Lord had saved them.
9 Yetro ya yi murna da jin duk abubuwa masu kyau da Ubangiji ya yi wa Isra’ila, wajen cetonsu daga hannun Masarawa.
Jethro was delighted to hear about all the good things the Lord had done for Israel when he'd saved them from the Egyptians.
10 “Yabo ga Ubangiji wanda ya cece ku daga hannun Masarawa da na Fir’auna, wanda kuma ya cece mutanensa daga hannun Masarawa.
Jethro announced, “May the Lord be blessed, who saved you from the Egyptians and from Pharaoh.
11 Yanzu na san cewa Ubangiji ya fi kowane allah, gama ya yi wannan ga masu girman kai da kuma waɗanda suka wulaƙanta Isra’ila.”
This is so convincing to me that the Lord is greater than all other gods, for he saved the people from the Egyptians when they acted so arrogantly towards the Israelites.”
12 Sa’an nan Yetro surukin Musa, ya kawo hadaya ta ƙonawa da waɗansu hadayu wa Allah, Haruna ya zo tare da dukan dattawan Isra’ila, suka ci abinci tare da surukin Musa a gaban Allah.
Then Jethro presented a burnt offering and sacrifices to God, and Aaron came with all the elders of Israel to eat a meal with him in God's presence.
13 Kashegari, Musa ya zauna domin yă yi wa mutane shari’a, sai suka tsaya kewaye da shi daga safe har yamma.
The following day Moses sat as a judge for the people, and they presented their cases to him from morning to evening.
14 Sa’ad da surukinsa ya lura da duk abin da Musa yake yi saboda mutane, sai ya ce, “Mene ne wannan da kake yi wa mutane? Don me kai kaɗai kake zama kana yin shari’a wa mutane, yayinda mutanen nan suke tsaya kewaye da kai daga safe har yamma?”
When his father-in-law saw everything that Moses was doing for the people, he asked, “What's all this you're doing for the people? Why are you sitting alone as judge, with everyone presenting their cases to you from morning to evening?”
15 Musa ya amsa ya ce, “Saboda mutanen suna zuwa wurina, don su nemi nufin Allah.
“Because the people come to me to ask God for his decision,” Moses replied.
16 Duk lokacin da suke da gardama, akan kawo su a wurina, ni kuma sai in raba tsakaninsu, in kuma koya musu dokokin Allah da farillansa.”
“When they argue over something, the case is brought before me to decide between one them, and I explain to them the God's laws and regulations.”
17 Surukin Musa ya amsa ya ce, “Abin da kake yi ba daidai ba ne.
Jethro told him, “What you're doing is not the best.
18 Kai da dukan mutanen da suke zuwa wurinka za ku gajiyar da kanku. Aikin ya fi ƙarfinka; ba za ka iya yinsa kai kaɗai ba.
You, and these people who come to you, are all going to wear yourselves out, because the workload is far too heavy. You can't handle it alone.
19 Ka kasa kunne gare ni yanzu, zan ba ka shawara, Allah kuma yă kasance tare da kai. Kai za ka zama wakilin mutane a gaban Allah, ka kuma kawo gardamansu gare shi.
So please listen to me. I'm going to give you some advice, and God will be with you. Yes, you must continue to be the people's representative before God, and take their cases to him.
20 Ka koya musu dokokinsa da farillarsa, ka kuma nuna musu hanyar rayuwa da ayyukan da za su yi.
Go on teaching them the laws and regulations. Show them how to live and the work they are to do.
21 Amma ka zaɓi mutane masu iyawa daga dukan mutane, maza masu tsoron Allah, amintattu, masu ƙin rashawa, ka sanya su shugabanni na dubbai, ɗari-ɗari, hamsin-hamsin da goma-goma.
But now you should choose men who are competent from among the people, men who respect God and who are trustworthy and not corrupt. Put them in charge of the people as leaders of thousands, hundreds, fifties, and tens.
22 Bari waɗannan mutane su sassanta mutane a kan ƙananan matsaloli, amma kowace babban matsala, ko bukata ta musamman, sai su kawo wurinka, ƙananan matsaloli kuma sai su yanke hukuncin da kansu. Ta haka ne za su taimaka wajen ɗaukan nauyin jama’a, don su sa aikin yă zama maka da sauƙi.
These men are to judge the people on a continuing basis. Major issues they can bring to you, but they can decide all the small matters themselves. In this way your burden will be made lighter as they share it with you.
23 In ka yi haka, Allah ya umarta za ka iya jimre gajiyar, kuma dukan mutanen nan za su koma gida da murna.”
If you follow my advice, and if it's what God tells you to do, then you will be able to survive, and all these people can go home satisfied that their cases have been heard.”
24 Musa ya kasa kunne ga surukinsa, ya kuma aikata duk abin da ya faɗa.
Moses listened to what his father-in-law said and followed all his advice.
25 Ya zaɓi mutane masu iyawa daga cikin dukan Isra’ila, ya naɗa su shugabannin mutane, shugabanni a kan dubbai, ɗari-ɗari, hamsin-hamsin da goma-goma.
So Moses chose competent men from all of Israel and put them in charge of the people as leaders of thousands, hundreds, fifties, and tens.
26 Suka yi hidimar alƙalanci na mutane a dukan lokaci. Gardandamin da suke da wuya, suka kawo wurin Musa, amma ƙananan batuttuwa, suka shari’anta a tsakaninsu.
They acted as judges for the people on a continuing basis. They brought the difficult cases to Moses, but they would judge the small matters themselves.
27 Sa’an nan Musa ya sallame surukinsa Yetro, ya kuwa koma ƙasarsa.
Then Moses sent Jethro on his way, and he went back to his own country.