< Fitowa 17 >
1 Dukan taron Isra’ilawa suka kama tafiya daga Hamadar Sin, suka yi ta tafiya suna sauka a wurare dabam-dabam bisa ga umarnin Ubangiji. A ƙarshe suka sauka a Refidim, suka zauna a can, amma ba ruwan da jama’a za su sha.
And all the congregation of the sons of Israel journey from the wilderness of Sin, on their journeys, by the command of YHWH, and encamp in Rephidim, and there is no water for the people to drink;
2 Saboda haka suka yi wa Musa maganganun banza suka ce, “Ba mu ruwa mu sha.” Musa ya amsa ya ce, “Don me kuke mini maganganun banza? Don me kuke gwada Ubangiji?”
and the people strive with Moses, and say, “Give us water, and we drink.” And Moses says to them, “Why do you strive with me? Why do you try YHWH?”
3 Amma mutanen suka yi fama da ƙishirwa a can, suka yi gunaguni a kan Musa. Suka ce, “Don me ka fitar da mu daga Masar, ka sa mu da’ya’yanmu da dabbobinmu, mu mutu da ƙishirwa?”
And the people thirst for water there, and the people murmur against Moses, and say, “Why [is] this [that] you have brought us up out of Egypt to put us to death, also our sons and our livestock, with thirst?”
4 Sai Musa ya yi kuka ga Ubangiji ya ce, “Me zan yi da wannan jama’a? Suna shiri su jajjefe ni da duwatsu.”
And Moses cries to YHWH, saying, “What do I do to this people? Yet a little, and they have stoned me.”
5 Ubangiji amsa wa Musa, “Ka ɗauki sandan da ka bugi ruwan Nilu da shi. Ka kira waɗansu shugabannin Isra’ila, ku wuce a gaban jama’ar.
And YHWH says to Moses, “Pass over before the people, and take with you from [the] elderly of Israel, and take your rod in your hand, with which you have struck the River, and you have gone.
6 Zan tsaya a can a gabanka, kusa da dutsen Horeb. Ka bugi dutsen, ruwa kuwa zai fito daga gare shi domin mutane su sha.” Sai Musa ya yi haka a idon dattawan Isra’ila.
Behold, I am standing before you there on the rock in Horeb, and you have struck on the rock, and waters have come out from it, and the people have drunk.” And Moses does so before the eyes of [the] elderly of Israel,
7 Sai suka ba wa wurin suna, Massa da Meriba, saboda Isra’ilawa sun yi jayayya, suka kuma gwada Ubangiji cewa, “Ubangiji yana tsakaninmu ko babu?”
and he calls the name of the place Massah, and Meribah, because of the strife of the sons of Israel, and because of their trying YHWH, saying, “Is YHWH in our midst or not?”
8 Amalekawa suka zo, suka yaƙi Isra’ilawa a Refidim.
And Amalek comes, and fights with Israel in Rephidim,
9 Musa ya ce wa Yoshuwa, “Zaɓi waɗansu mazanmu, ka je ka yaƙi Amalekawa. Gobe zan tsaya a bisa tudu, da sandan Allah a hannuwana.”
and Moses says to Joshua, “Choose men for us, and go out, fight with Amalek: tomorrow I am standing on the top of the hill, and the rod of God in my hand.”
10 Sai Yoshuwa ya yaƙi Amalekawa kamar yadda Musa ya umarta, Musa, Haruna da Hur kuwa suka tafi bisa tudu.
And Joshua does as Moses has said to him, to fight with Amalek, and Moses, Aaron, and Hur have gone up [to] the top of the height;
11 Muddin hannun Musa yana a miƙe, sai Isra’ilawa su yi ta cin nasara, amma da zarar hannunsa ya sauka, sai Amalekawa su yi ta cin nasara.
and it has come to pass, when Moses lifts up his hand, that Israel has been mighty, and when he lets his hands rest, that Amalek has been mighty.
12 Sa’ad da hannuwan Musa suka gaji, sai Haruna da Hur suka ɗauki dutse suka sa ya zauna a kai. Sa’an nan su kuma suka tsaya gefe da gefe, suna riƙe da hannuwansa har fāɗuwar rana.
And the hands of Moses [are] heavy, and they take a stone and set [it] under him, and he sits on it, and Aaron and Hur have taken hold on his hands, one on this [side] and one on that [side]; and his hands are steadfast until the going in of the sun;
13 Sai Yoshuwa kuwa ya ci nasara a kan Amalekawa da takobi.
and Joshua weakens Amalek and his people by the mouth of the sword.
14 Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka rubuta wannan a cikin littafi, yă zama abin tuni, ka kuma faɗa wa Yoshuwa zan hallaka Amalekawa ƙaƙaf daga duniya.”
And YHWH says to Moses, “Write this, a memorial in a Scroll, and set [it] in the ears of Joshua, that I utterly wipe away the remembrance of Amalek from under the heavens”;
15 Musa ya gina bagade, sai ya kira shi Ubangiji shi ne Tutata.
and Moses builds an altar, and calls its name YHWH-Nissi,
16 Ya ce, “Gama an ɗaga hannuwa sama zuwa kursiyin Ubangiji, Ubangiji zai yaƙi Amalekawa daga tsara zuwa tsara.”
and says, “Because a hand [is] on the throne of YAH, war [is] to YHWH with Amalek from generation [to] generation.”