< Fitowa 17 >
1 Dukan taron Isra’ilawa suka kama tafiya daga Hamadar Sin, suka yi ta tafiya suna sauka a wurare dabam-dabam bisa ga umarnin Ubangiji. A ƙarshe suka sauka a Refidim, suka zauna a can, amma ba ruwan da jama’a za su sha.
And all the congregation of the children of Israel journeyed from the wilderness of Sin, after their journeyings, by the order of the Lord; and they encamped in Rephidim, and there was no water for the people to drink.
2 Saboda haka suka yi wa Musa maganganun banza suka ce, “Ba mu ruwa mu sha.” Musa ya amsa ya ce, “Don me kuke mini maganganun banza? Don me kuke gwada Ubangiji?”
And the people quarrelled with Moses, and said, Give us water that we may drink; and Moses said unto them, Why will ye quarrel with me? why will ye tempt the Lord?
3 Amma mutanen suka yi fama da ƙishirwa a can, suka yi gunaguni a kan Musa. Suka ce, “Don me ka fitar da mu daga Masar, ka sa mu da’ya’yanmu da dabbobinmu, mu mutu da ƙishirwa?”
And the people thirsted there for water; and the people murmured against Moses, and said, For what purpose is it that thou hast brought us up out of Egypt, to kill me and my children and my cattle with thirst?
4 Sai Musa ya yi kuka ga Ubangiji ya ce, “Me zan yi da wannan jama’a? Suna shiri su jajjefe ni da duwatsu.”
And Moses cried unto the Lord, saying, What shall I do unto this people? but little is wanting and they will stone me.
5 Ubangiji amsa wa Musa, “Ka ɗauki sandan da ka bugi ruwan Nilu da shi. Ka kira waɗansu shugabannin Isra’ila, ku wuce a gaban jama’ar.
And the Lord said unto Moses, Pass on before the people, and take with thee some of the elders of Israel; and thy staff, wherewith thou smotest the river, take in thy hand, and go.
6 Zan tsaya a can a gabanka, kusa da dutsen Horeb. Ka bugi dutsen, ruwa kuwa zai fito daga gare shi domin mutane su sha.” Sai Musa ya yi haka a idon dattawan Isra’ila.
Behold, I will be standing before thee there upon the rock at Horeb; and thou shalt smite the rock, and there shall come out from it water, and the people shall drink; and Moses did so before the eyes of the elders of Israel.
7 Sai suka ba wa wurin suna, Massa da Meriba, saboda Isra’ilawa sun yi jayayya, suka kuma gwada Ubangiji cewa, “Ubangiji yana tsakaninmu ko babu?”
And he called the name of the place Massah and Meribah; because of the quarrelling of the children of Israel, and because they tempted the Lord, saying, Is then the Lord among us, or not?
8 Amalekawa suka zo, suka yaƙi Isra’ilawa a Refidim.
Then came Amalek, and fought with Israel in Rephidim.
9 Musa ya ce wa Yoshuwa, “Zaɓi waɗansu mazanmu, ka je ka yaƙi Amalekawa. Gobe zan tsaya a bisa tudu, da sandan Allah a hannuwana.”
And Moses said unto Joshua, Choose for us men, and go out, fight with Amalek; tomorrow I will stand on the top of the hill with the staff of God in my hand.
10 Sai Yoshuwa ya yaƙi Amalekawa kamar yadda Musa ya umarta, Musa, Haruna da Hur kuwa suka tafi bisa tudu.
And Joshua did as Moses had said to him, to fight with Amalek; and Moses, Aaron, and Chur went up to the top of the hill.
11 Muddin hannun Musa yana a miƙe, sai Isra’ilawa su yi ta cin nasara, amma da zarar hannunsa ya sauka, sai Amalekawa su yi ta cin nasara.
And it came to pass, when Moses held up his hand, that Israel prevailed: and when he let down his hand, that Amalek prevailed.
12 Sa’ad da hannuwan Musa suka gaji, sai Haruna da Hur suka ɗauki dutse suka sa ya zauna a kai. Sa’an nan su kuma suka tsaya gefe da gefe, suna riƙe da hannuwansa har fāɗuwar rana.
But when the hands of Moses became heavy, they took a stone, and put it under him, and he sat thereon; and Aaron and Chur supported his hands, one on one side, and the other on the other side; and his hands were steady until the going down of the sun.
13 Sai Yoshuwa kuwa ya ci nasara a kan Amalekawa da takobi.
And Joshua discomfited Amalek and his people with the edge of the sword.
14 Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka rubuta wannan a cikin littafi, yă zama abin tuni, ka kuma faɗa wa Yoshuwa zan hallaka Amalekawa ƙaƙaf daga duniya.”
And the Lord said unto Moses, Write this for a memorial in the book, and rehearse it in the ears of Joshua; for I will utterly blot out the remembrance of Amalek from under the heavens.
15 Musa ya gina bagade, sai ya kira shi Ubangiji shi ne Tutata.
And Moses built an altar, and called its name Adonay Nissy [[The Lord is my Banner]].
16 Ya ce, “Gama an ɗaga hannuwa sama zuwa kursiyin Ubangiji, Ubangiji zai yaƙi Amalekawa daga tsara zuwa tsara.”
And he said, Because the Lord hath sworn on his throne, that the Lord will have war with Amalek from generation to generation.