< Fitowa 17 >
1 Dukan taron Isra’ilawa suka kama tafiya daga Hamadar Sin, suka yi ta tafiya suna sauka a wurare dabam-dabam bisa ga umarnin Ubangiji. A ƙarshe suka sauka a Refidim, suka zauna a can, amma ba ruwan da jama’a za su sha.
Then all the Israelites left the Desert of Sin, going from place to place as they followed the Lord's commands. They camped at Rephidim, but there wasn't any water for the people to drink.
2 Saboda haka suka yi wa Musa maganganun banza suka ce, “Ba mu ruwa mu sha.” Musa ya amsa ya ce, “Don me kuke mini maganganun banza? Don me kuke gwada Ubangiji?”
Some of them came and complained to Moses, saying, “Give us water to drink!” Moses replied, “Why are you complaining to me?” Moses asked. “Why are you trying to challenge the Lord?”
3 Amma mutanen suka yi fama da ƙishirwa a can, suka yi gunaguni a kan Musa. Suka ce, “Don me ka fitar da mu daga Masar, ka sa mu da’ya’yanmu da dabbobinmu, mu mutu da ƙishirwa?”
But the people were so thirsty for water there that they went on complaining to Moses, saying, “Why did you have to bring us out of Egypt? Are you trying to kill us and our children and livestock by thirst?”
4 Sai Musa ya yi kuka ga Ubangiji ya ce, “Me zan yi da wannan jama’a? Suna shiri su jajjefe ni da duwatsu.”
Moses cried out to the Lord, “What am I going to do with these people? A bit more of this and they're going to stone me!”
5 Ubangiji amsa wa Musa, “Ka ɗauki sandan da ka bugi ruwan Nilu da shi. Ka kira waɗansu shugabannin Isra’ila, ku wuce a gaban jama’ar.
The Lord told Moses, “Go ahead of the people, and take some of the elders of Israel with you. Take with you the walking stick you used to hit the Nile, and just go on ahead.
6 Zan tsaya a can a gabanka, kusa da dutsen Horeb. Ka bugi dutsen, ruwa kuwa zai fito daga gare shi domin mutane su sha.” Sai Musa ya yi haka a idon dattawan Isra’ila.
Look, I will stand there beside you by the rock at Horeb. When you hit the rock water will pour out for the people to drink.” So Moses did this as the elders of Israel watched.
7 Sai suka ba wa wurin suna, Massa da Meriba, saboda Isra’ilawa sun yi jayayya, suka kuma gwada Ubangiji cewa, “Ubangiji yana tsakaninmu ko babu?”
He called the place Massah and Meribah because the Israelites argued there, and because they challenged the Lord, saying, “Is the Lord with us, or not?”
8 Amalekawa suka zo, suka yaƙi Isra’ilawa a Refidim.
Then some Amalekites came and attacked the Israelites at Rephidim.
9 Musa ya ce wa Yoshuwa, “Zaɓi waɗansu mazanmu, ka je ka yaƙi Amalekawa. Gobe zan tsaya a bisa tudu, da sandan Allah a hannuwana.”
Moses told Joshua, “Choose some of men and go out and fight the Amalekites. Tomorrow I'll stand on the top of this hill holding the walking stick of God.”
10 Sai Yoshuwa ya yaƙi Amalekawa kamar yadda Musa ya umarta, Musa, Haruna da Hur kuwa suka tafi bisa tudu.
Joshua did what Moses told him and fought the Amalekites, while Moses, Aaron, and Hur climbed to the top of the hill.
11 Muddin hannun Musa yana a miƙe, sai Isra’ilawa su yi ta cin nasara, amma da zarar hannunsa ya sauka, sai Amalekawa su yi ta cin nasara.
As long as Moses held up the walking stick his hands, the Israelites were the ones winning, but when he lowered them, it was the Amalekites.
12 Sa’ad da hannuwan Musa suka gaji, sai Haruna da Hur suka ɗauki dutse suka sa ya zauna a kai. Sa’an nan su kuma suka tsaya gefe da gefe, suna riƙe da hannuwansa har fāɗuwar rana.
So when Moses' hands became heavy, the others took a stone and put it under him for him to sit on. Aaron and Hur stood on each side of Moses and held his hands up. In this way his hands were kept firmly up until the sun went down.
13 Sai Yoshuwa kuwa ya ci nasara a kan Amalekawa da takobi.
As a result Joshua defeated the Amalekite army.
14 Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka rubuta wannan a cikin littafi, yă zama abin tuni, ka kuma faɗa wa Yoshuwa zan hallaka Amalekawa ƙaƙaf daga duniya.”
The Lord told Moses, “Write all this down on a scroll as a reminder and read it out loud to Joshua, because I'm going to completely wipe out the Amalekites so nobody on earth will remember them.”
15 Musa ya gina bagade, sai ya kira shi Ubangiji shi ne Tutata.
Moses built an altar and called it “the Lord is my banner of victory.”
16 Ya ce, “Gama an ɗaga hannuwa sama zuwa kursiyin Ubangiji, Ubangiji zai yaƙi Amalekawa daga tsara zuwa tsara.”
“Hold up the victory banner of the Lord!” Moses declared. “The Lord will go on fighting the Amalekites for all generations!”