< Fitowa 16 >

1 Dukan taron Isra’ila suka tashi daga Elim suka zo hamadar Sin, wadda take tsakanin Elim da Sinai, a rana ta goma sha biyar ga wata biyu, bayan sun fito daga Masar.
Et ils partirent d’Élim, toute l’assemblée des fils d’Israël, et vinrent au désert de Sin, qui est entre Élim et Sinaï, le quinzième jour du second mois après leur sortie du pays d’Égypte.
2 A hamadan, dukan taro suka yi gunaguni a kan Musa da Haruna.
Et toute l’assemblée des fils d’Israël murmura contre Moïse et contre Aaron, dans le désert.
3 Isra’ilawa suka ce musu, “Da ma a hannun Ubangiji ne muka mutu a Masar, inda muka zauna kewaye da tukwanen nama, muna cin duk abincin da muke so, amma kun kawo mu cikin wannan hamada don ku kashe dukan wannan taro da yunwa.”
Et les fils d’Israël leur dirent: Ah! que ne sommes-nous morts par la main de l’Éternel dans le pays d’Égypte, quand nous étions assis auprès des pots de chair, quand nous mangions du pain à satiété! Car vous nous avez fait sortir dans ce désert pour faire mourir de faim toute cette congrégation.
4 Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Zan zubo muku burodi kamar ruwa daga sama. Mutanen za su fita kowace rana su tattara abin da zai ishe su na ranan. Ta haka zan gwada su in ga ko za su bi umarnaina.
Et l’Éternel dit à Moïse: Voici, je vais vous faire pleuvoir des cieux du pain, et le peuple sortira, et en recueillera chaque jour la portion d’un jour, afin que je l’éprouve, [pour voir] s’il marchera dans ma loi, ou non.
5 A rana ta shida za su shirya abin da suka kwaso, wannan kuwa zai zama ninki biyu na abin da sukan tattara na sauran ranaku.”
Et il arrivera que, le sixième jour, ils prépareront ce qu’ils auront rapporté, et ce sera le double de ce qu’ils recueilleront chaque jour.
6 Saboda haka Musa da Haruna suka ce wa dukan Isra’ila, “Da yamma za ku sani Ubangiji ne ya fitar da ku daga Masar.
Et Moïse et Aaron dirent à tous les fils d’Israël: Au soir vous saurez que l’Éternel vous a fait sortir du pays d’Égypte;
7 Da safe za ku ga ɗaukakar Ubangiji, saboda ya ji gunaguninku a kansa. Wane mu, da za ku yi gunaguni a kanmu?”
et, au matin, vous verrez la gloire de l’Éternel, parce qu’il a entendu vos murmures contre l’Éternel; car que sommes-nous, que vous murmuriez contre nous?
8 Musa ya kuma ce, “Za ku san cewa shi ne Ubangiji, sa’ad da ya ba ku nama ku ci da yamma, da kuma duk burodin da kuke so da safe, saboda ya ji gunagunin da kuka yi a kansa. Namu a wane? Ai, gunaguninku ba a kanmu ba, amma a kan Ubangiji ne.”
Et Moïse dit: [Ce sera] en ce que l’Éternel vous donnera le soir de la chair à manger, et au matin du pain à satiété; parce que l’Éternel a entendu vos murmures que vous avez proférés contre lui; car que sommes-nous? Vos murmures ne sont pas contre nous, mais contre l’Éternel.
9 Sai Musa ya ce wa Haruna, “Ka faɗa wa dukan taron Isra’ila, ‘Ku zo gaban Ubangiji, gama ya ji gunaguninku.’”
Et Moïse dit à Aaron: Dis à toute l’assemblée des fils d’Israël: Approchez-vous devant l’Éternel; car il a entendu vos murmures.
10 Yayinda Haruna yake magana da dukan taron Isra’ila, sai suka duba wajen hamada, sai ga ɗaukakar Ubangiji tana bayyana a girgije.
Et il arriva, comme Aaron parlait à toute l’assemblée des fils d’Israël, qu’ils se tournèrent vers le désert; et voici, la gloire de l’Éternel parut dans la nuée.
11 Ubangiji ya ce wa Musa,
Et l’Éternel parla à Moïse, disant:
12 “Na ji gunagunin Isra’ilawa. Ka faɗa musu, ‘A tsakanin fāɗuwar rana da almuru, za ku ci nama, da safe kuma za ku ƙoshi da burodi. Sa’an nan za ku sani ni ne Ubangiji Allahnku.’”
J’ai entendu les murmures des fils d’Israël. Parle-leur, disant: Entre les deux soirs vous mangerez de la chair, et au matin vous serez rassasiés de pain; et vous saurez que je suis l’Éternel, votre Dieu.
13 Da yamman wannan rana, sai makware suka rufe dukan sansani, da safe kuma sai ga raɓa ta kewaye sansani.
Et il arriva, le soir, que des cailles montèrent et couvrirent le camp; et, au matin, il y eut une couche de rosée autour du camp;
14 Lokacin da raɓar ta watse, sai ga wani abu kamar tsaki, falle-falle kuma da laushi, fari, kamar hazo, a ƙasa.
et la couche de rosée se leva, et voici sur la surface du désert quelque chose de menu, de grenu, quelque chose de menu comme la gelée blanche sur la terre.
15 Sa’ad da Isra’ilawa suka ga wannan, sai suka ce wa junansu, “Mene ne wannan?” Gama ba su san ko mene ne ba. Musa ya ce musu, “Wannan shi ne burodin da Ubangiji ya ba ku ku ci.
Et les fils d’Israël le virent, et se dirent l’un à l’autre: Qu’est-ce que cela? Car ils ne savaient ce que c’était. Et Moïse leur dit: C’est le pain que l’Éternel vous a donné à manger.
16 Wannan shi ne abin da Ubangiji ya umarta, ‘Kowane mutum zai tattara bisa ga bukatarsa. Ku tara rabin gallon don mutum guda da yake cikin tentinku.’”
Voici la parole que l’Éternel a commandée: Recueillez-en, chacun en proportion de ce qu’il peut manger, un omer par tête, selon le nombre de vos personnes; vous en prendrez chacun pour ceux qui sont dans sa tente.
17 Isra’ilawa suka yi kamar yadda aka faɗa musu, waɗansu suka tattara da yawa, waɗansu kuma kaɗan.
Et les fils d’Israël firent ainsi, et ils recueillirent, l’un beaucoup, l’autre peu.
18 Da suka gwada a mudu, wanda ya tattara da yawa bai sami mafi yawa ba, wanda kuma ya tattara kaɗan bai sami ƙanƙani ba. Kowane mutum ya tattara daidai bukatarsa.
Et ils mesurèrent à l’omer: et celui qui avait beaucoup, n’eut pas trop; et celui qui avait peu, n’en manqua pas; ils avaient recueilli, chacun en proportion de ce qu’il mangeait.
19 Sa’an nan Musa ya ce musu, “Kada wani yă bar saura har safe.”
Et Moïse leur dit: Que personne n’en laisse de reste jusqu’au matin.
20 Duk da haka waɗansu ba su kula da umarnin Musa ba, suka bar saura har safe, kashegari kuwa ta yi tsutsotsi, ta ruɓe, sai Musa ya yi fushi da su.
Mais ils n’écoutèrent pas Moïse, et quelques-uns [d’entre eux] en laissèrent de reste jusqu’au matin; et il s’y engendra des vers, et cela puait: et Moïse se mit en colère contre eux.
21 Kowace safiya, kowanne mutum yakan tattara daidai bukatarsa, lokacin da rana ta yi zafi, sai ta narke.
Et ils en recueillaient chaque matin, chacun en proportion de ce qu’il mangeait; et à la chaleur du soleil cela fondait.
22 A rana ta shida, suka tattara ninki biyu, mudu biyu ga mutum guda, sai shugabannin taron suka zo suka kawo ƙara wurin Musa.
Et il arriva que, le sixième jour, ils recueillirent du pain au double, deux omers pour chacun; et tous les principaux de l’assemblée vinrent et le rapportèrent à Moïse.
23 Shi kuma ya ce musu, “Wannan shi ne umarnin Ubangiji, ‘Gobe za tă zama ranar hutu, Asabbaci mai tsarki ga Ubangiji. Domin haka sai ku toya abin da kuke so ku toya, ku kuma dafa abin da kuke so ku dafa. Abin da ya rage ku ajiye har safe.’”
Et il leur dit: C’est ici ce que l’Éternel a dit: Demain est le repos, le sabbat consacré à l’Éternel; faites cuire ce que vous avez à cuire, et faites bouillir ce que vous avez à faire bouillir, et tout le surplus serrez-le pour vous, pour le garder jusqu’au matin.
24 Sai suka bar saura har safe, kamar yadda Musa ya umarta, bai kuwa yi wari ko yă yi tsutsa ba.
Et ils le serrèrent jusqu’au matin, comme Moïse l’avait commandé; et cela ne pua point, et il n’y eut point de vers dedans.
25 Musa ya ce, “Ku ci shi yau, saboda yau Asabbaci ne na Ubangiji. Ba za ku same shi a ƙasa a yau ba.
Et Moïse dit: Mangez-le aujourd’hui, car aujourd’hui est le sabbat [consacré] à l’Éternel; aujourd’hui vous n’en trouverez point aux champs.
26 Kwana shida za ku tattara shi, amma a rana ta bakwai, Asabbaci, ba za a same shi ba.”
Six jours vous en recueillerez, mais au septième jour est le sabbat; il n’y en aura point en ce [jour-là].
27 Duk da haka waɗansu mutane suka fita a ranar Asabbaci don su tattara, amma ba su sami kome ba.
Et il arriva, le septième jour, que quelques-uns du peuple sortirent pour en recueillir, et ils n’en trouvèrent point.
28 Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Har yaushe za ku ƙi bin dokokina da umarnaina?
Et l’Éternel dit à Moïse: Jusques à quand refuserez-vous de garder mes commandements et mes lois?
29 Ku lura fa, ai, Ubangiji ne ya ba ku Asabbaci; shi ya sa a kan ba ku burodi na kwana biyu, a rana ta shida. Kowa ya kamata yă kasance inda yake a rana ta bakwai; kada kowa yă fita.”
Voyez que l’Éternel vous a donné le sabbat; c’est pourquoi il vous donne au sixième jour du pain pour deux jours. Que chacun reste chez lui; que personne ne sorte du lieu où il est, le septième jour.
30 Sai mutanen suka huta a rana ta bakwai.
Et le peuple se reposa le septième jour.
31 Mutanen Isra’ila suka kira burodin Manna. Manna yana nan fari kamar farin riɗi, ɗanɗanonsa kuma yana kama da masa da aka yi da zuma.
Et la maison d’Israël appela le nom de cela manne. Et elle était comme de la semence de coriandre, blanche, et avait le goût d’un gâteau au miel.
32 Musa ya ce, “Wannan shi ne abin da Ubangiji ya umarta, ‘Ku auna mudu guda na Manna, a adana ta dukan zamananku, domin kowane zamani yă ga irin abincin da na ba ku ku ci a hamada, yayinda na fitar da ku daga Masar.’”
Et Moïse dit: Voici la parole que l’Éternel a commandée: Qu’on en remplisse un omer pour le garder pour vos générations, afin qu’elles voient le pain que je vous ai fait manger dans le désert, lorsque je vous ai fait sortir du pays d’Égypte.
33 Saboda haka Musa ya ce wa Haruna, “Ka ɗauki tulu, ka sa mudu guda na Manna a ciki. Sa’an nan ka sa shi a gaban Ubangiji, don a adana don tsararraki masu zuwa.”
Et Moïse dit à Aaron: Prends une cruche, et mets-y plein un omer de manne, et pose-la devant l’Éternel, pour la garder pour vos générations.
34 Sai Haruna ya ajiye Mannar a gaban Akwatin Alkawari, don a adana ta kamar yadda Ubangiji ya umarci Musa.
Comme l’Éternel l’avait commandé à Moïse, Aaron la posa devant le témoignage pour être gardée.
35 Isra’ilawa suka yi shekaru arba’in suna cin Manna, har sai da suka shiga cikin ƙasar da take da mutane, suka ci Manna har zuwa kan iyakar ƙasar Kan’ana.
Et les fils d’Israël mangèrent la manne 40 ans, jusqu’à ce qu’ils entrèrent dans un pays habité; ils mangèrent la manne jusqu’à leur arrivée à la frontière du pays de Canaan.
36 (Omer guda, daidai ne da kashi ɗaya bisa goma na Efa.)
Or l’omer est la dixième partie de l’épha.

< Fitowa 16 >