< Fitowa 16 >
1 Dukan taron Isra’ila suka tashi daga Elim suka zo hamadar Sin, wadda take tsakanin Elim da Sinai, a rana ta goma sha biyar ga wata biyu, bayan sun fito daga Masar.
And they took their journey from Elim. And all the congregation of the sons of Israel came to the wilderness of Sin, which is between Elim and Sinai, on the fifteenth day of the second month after their departing out of the land of Egypt.
2 A hamadan, dukan taro suka yi gunaguni a kan Musa da Haruna.
And the whole congregation of the sons of Israel murmured against Moses and against Aaron in the wilderness.
3 Isra’ilawa suka ce musu, “Da ma a hannun Ubangiji ne muka mutu a Masar, inda muka zauna kewaye da tukwanen nama, muna cin duk abincin da muke so, amma kun kawo mu cikin wannan hamada don ku kashe dukan wannan taro da yunwa.”
And the sons of Israel said to them, Would that we had died by the hand of Jehovah in the land of Egypt, when we sat by the flesh-pots, when we ate bread to the full, for ye have brought us forth into this wilderness, to kill this whole assembly with hunger.
4 Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Zan zubo muku burodi kamar ruwa daga sama. Mutanen za su fita kowace rana su tattara abin da zai ishe su na ranan. Ta haka zan gwada su in ga ko za su bi umarnaina.
Then Jehovah said to Moses, Behold, I will rain bread from heaven for you, and the people shall go out and gather a day's portion every day, that I may prove them, whether they will walk in my law, or not.
5 A rana ta shida za su shirya abin da suka kwaso, wannan kuwa zai zama ninki biyu na abin da sukan tattara na sauran ranaku.”
And it shall come to pass on the sixth day, that they shall prepare that which they bring in, and it shall be twice as much as they gather daily.
6 Saboda haka Musa da Haruna suka ce wa dukan Isra’ila, “Da yamma za ku sani Ubangiji ne ya fitar da ku daga Masar.
And Moses and Aaron said to all the sons of Israel, At evening, then ye shall know that Jehovah has brought you out from the land of Egypt,
7 Da safe za ku ga ɗaukakar Ubangiji, saboda ya ji gunaguninku a kansa. Wane mu, da za ku yi gunaguni a kanmu?”
and in the morning, then ye shall see the glory of Jehovah, for he hears your murmurings against Jehovah. And what are we, that ye murmur against us?
8 Musa ya kuma ce, “Za ku san cewa shi ne Ubangiji, sa’ad da ya ba ku nama ku ci da yamma, da kuma duk burodin da kuke so da safe, saboda ya ji gunagunin da kuka yi a kansa. Namu a wane? Ai, gunaguninku ba a kanmu ba, amma a kan Ubangiji ne.”
And Moses said, This shall be when Jehovah shall give you flesh to eat in the evening, and bread to the full in the morning, for that Jehovah hears your murmurings which ye murmur against him. And what are we? Your murmurings are not against us, but against Jehovah.
9 Sai Musa ya ce wa Haruna, “Ka faɗa wa dukan taron Isra’ila, ‘Ku zo gaban Ubangiji, gama ya ji gunaguninku.’”
And Moses said to Aaron, Say to all the congregation of the sons of Israel, Come near before Jehovah, for he has heard your murmurings.
10 Yayinda Haruna yake magana da dukan taron Isra’ila, sai suka duba wajen hamada, sai ga ɗaukakar Ubangiji tana bayyana a girgije.
And it came to pass, as Aaron spoke to the whole congregation of the sons of Israel, that they looked toward the wilderness, and, behold, the glory of Jehovah appeared in the cloud.
11 Ubangiji ya ce wa Musa,
And Jehovah spoke to Moses, saying,
12 “Na ji gunagunin Isra’ilawa. Ka faɗa musu, ‘A tsakanin fāɗuwar rana da almuru, za ku ci nama, da safe kuma za ku ƙoshi da burodi. Sa’an nan za ku sani ni ne Ubangiji Allahnku.’”
I have heard the murmurings of the sons of Israel. Speak to them, saying, At evening ye shall eat flesh, and in the morning ye shall be filled with bread. And ye shall know that I am Jehovah your God.
13 Da yamman wannan rana, sai makware suka rufe dukan sansani, da safe kuma sai ga raɓa ta kewaye sansani.
And it came to pass at evening, that the quails came up, and covered the camp. And in the morning the dew lay round about the camp,
14 Lokacin da raɓar ta watse, sai ga wani abu kamar tsaki, falle-falle kuma da laushi, fari, kamar hazo, a ƙasa.
and when the dew that lay was gone up, behold, upon the face of the wilderness a small round thing, small as the hoarfrost on the ground.
15 Sa’ad da Isra’ilawa suka ga wannan, sai suka ce wa junansu, “Mene ne wannan?” Gama ba su san ko mene ne ba. Musa ya ce musu, “Wannan shi ne burodin da Ubangiji ya ba ku ku ci.
And when the sons of Israel saw it, they said one to another, What is it? For they knew not what it was. And Moses said to them, It is the bread which Jehovah has given you to eat.
16 Wannan shi ne abin da Ubangiji ya umarta, ‘Kowane mutum zai tattara bisa ga bukatarsa. Ku tara rabin gallon don mutum guda da yake cikin tentinku.’”
This is the thing which Jehovah has commanded, Gather ye of it every man according to his eating, an omer a head. According to the number of your persons, ye shall take it, every man for those who are in his tent.
17 Isra’ilawa suka yi kamar yadda aka faɗa musu, waɗansu suka tattara da yawa, waɗansu kuma kaɗan.
And the sons of Israel did so, and gathered, some more, some less.
18 Da suka gwada a mudu, wanda ya tattara da yawa bai sami mafi yawa ba, wanda kuma ya tattara kaɗan bai sami ƙanƙani ba. Kowane mutum ya tattara daidai bukatarsa.
And when they measured it with an omer, he who gathered much had nothing over, and he who gathered little had no lack; they gathered every man according to his eating.
19 Sa’an nan Musa ya ce musu, “Kada wani yă bar saura har safe.”
And Moses said to them, Let no man leave of it till the morning.
20 Duk da haka waɗansu ba su kula da umarnin Musa ba, suka bar saura har safe, kashegari kuwa ta yi tsutsotsi, ta ruɓe, sai Musa ya yi fushi da su.
Notwithstanding they did not hearken to Moses, but some of them left of it until the morning, and it bred worms, and became foul, and Moses was angry with them.
21 Kowace safiya, kowanne mutum yakan tattara daidai bukatarsa, lokacin da rana ta yi zafi, sai ta narke.
And they gathered it morning by morning, every man according to his eating. And when the sun grew hot, it melted.
22 A rana ta shida, suka tattara ninki biyu, mudu biyu ga mutum guda, sai shugabannin taron suka zo suka kawo ƙara wurin Musa.
And it came to pass, that on the sixth day they gathered twice as much bread, two omers for each one. And all the rulers of the congregation came and told Moses.
23 Shi kuma ya ce musu, “Wannan shi ne umarnin Ubangiji, ‘Gobe za tă zama ranar hutu, Asabbaci mai tsarki ga Ubangiji. Domin haka sai ku toya abin da kuke so ku toya, ku kuma dafa abin da kuke so ku dafa. Abin da ya rage ku ajiye har safe.’”
And he said to them, This is that which Jehovah has spoken, Tomorrow is a solemn rest, a holy sabbath to Jehovah. Bake that which ye will bake, and boil that which ye will boil, and all that remains over lay up for you to be kept until the morning.
24 Sai suka bar saura har safe, kamar yadda Musa ya umarta, bai kuwa yi wari ko yă yi tsutsa ba.
And they laid it up till the morning, as Moses bade, and it did not become foul, neither was there any worm in it.
25 Musa ya ce, “Ku ci shi yau, saboda yau Asabbaci ne na Ubangiji. Ba za ku same shi a ƙasa a yau ba.
And Moses said, Eat that today, for today is a sabbath to Jehovah. Today ye shall not find it in the field.
26 Kwana shida za ku tattara shi, amma a rana ta bakwai, Asabbaci, ba za a same shi ba.”
Six days ye shall gather it, but on the seventh day is the sabbath, there shall be none in it.
27 Duk da haka waɗansu mutane suka fita a ranar Asabbaci don su tattara, amma ba su sami kome ba.
And it came to pass on the seventh day, that some of the people went out to gather, and they found none.
28 Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Har yaushe za ku ƙi bin dokokina da umarnaina?
And Jehovah said to Moses, How long do ye refuse to keep my commandments and my laws?
29 Ku lura fa, ai, Ubangiji ne ya ba ku Asabbaci; shi ya sa a kan ba ku burodi na kwana biyu, a rana ta shida. Kowa ya kamata yă kasance inda yake a rana ta bakwai; kada kowa yă fita.”
See, because Jehovah has given you the sabbath, therefore he gives you on the sixth day the bread of two days. Abide ye every man in his place. Let no man go out of his place on the seventh day.
30 Sai mutanen suka huta a rana ta bakwai.
So the people rested on the seventh day.
31 Mutanen Isra’ila suka kira burodin Manna. Manna yana nan fari kamar farin riɗi, ɗanɗanonsa kuma yana kama da masa da aka yi da zuma.
And the house of Israel called the name of it Manna. And it was like coriander seed, white, and the taste of it was like wafers with honey.
32 Musa ya ce, “Wannan shi ne abin da Ubangiji ya umarta, ‘Ku auna mudu guda na Manna, a adana ta dukan zamananku, domin kowane zamani yă ga irin abincin da na ba ku ku ci a hamada, yayinda na fitar da ku daga Masar.’”
And Moses said, This is the thing which Jehovah has commanded. Let an omerful of it be kept throughout your generations, that they may see the bread with which I fed you in the wilderness, when I brought you forth from the land of Egypt.
33 Saboda haka Musa ya ce wa Haruna, “Ka ɗauki tulu, ka sa mudu guda na Manna a ciki. Sa’an nan ka sa shi a gaban Ubangiji, don a adana don tsararraki masu zuwa.”
And Moses said to Aaron, Take a pot, and put an omerful of manna in it, and lay it up before Jehovah, to be kept throughout your generations.
34 Sai Haruna ya ajiye Mannar a gaban Akwatin Alkawari, don a adana ta kamar yadda Ubangiji ya umarci Musa.
As Jehovah commanded Moses, so Aaron laid it up before the Testimony, to be kept.
35 Isra’ilawa suka yi shekaru arba’in suna cin Manna, har sai da suka shiga cikin ƙasar da take da mutane, suka ci Manna har zuwa kan iyakar ƙasar Kan’ana.
And the sons of Israel ate the manna forty years, until they came to a land inhabited. They ate the manna until they came to the borders of the land of Canaan.
36 (Omer guda, daidai ne da kashi ɗaya bisa goma na Efa.)
Now an omer is the tenth part of an ephah.