< Fitowa 16 >

1 Dukan taron Isra’ila suka tashi daga Elim suka zo hamadar Sin, wadda take tsakanin Elim da Sinai, a rana ta goma sha biyar ga wata biyu, bayan sun fito daga Masar.
Så brød de op fra Elim, og hele Israeliternes Menighed kom til Sins Ørken, der ligger mellem Elim og Sinaj, på den femtende Dag i den anden Måned efter deres Udvandring af Ægypten.
2 A hamadan, dukan taro suka yi gunaguni a kan Musa da Haruna.
Men hele Israeliternes Menighed knurrede mod Moses og Aron i Ørkenen,
3 Isra’ilawa suka ce musu, “Da ma a hannun Ubangiji ne muka mutu a Masar, inda muka zauna kewaye da tukwanen nama, muna cin duk abincin da muke so, amma kun kawo mu cikin wannan hamada don ku kashe dukan wannan taro da yunwa.”
og Israeliterne sagde til dem: "Var vi dog blot døde for HERRENs Hånd i Ægypten, hvor vi sad ved Kødgryderne og kunde spise os mætte i Brød! Thi I har ført os ud i denne Ørken for at lade hele denne Forsamling dø af Sult."
4 Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Zan zubo muku burodi kamar ruwa daga sama. Mutanen za su fita kowace rana su tattara abin da zai ishe su na ranan. Ta haka zan gwada su in ga ko za su bi umarnaina.
Da sagde HERREN til Moses: "Se, jeg vil lade Brød regne ned fra Himmelen til eder, og Folket skal gå ud og hver Dag samle så meget, som de daglig behøver, for at jeg kan prøve dem, om de vil følge min Lov eller ej.
5 A rana ta shida za su shirya abin da suka kwaso, wannan kuwa zai zama ninki biyu na abin da sukan tattara na sauran ranaku.”
Og når de på den sjette Ugedag tilbereder, hvad de har bragt hjem, så skal det være dobbelt så meget, som de samler de andre Dage."
6 Saboda haka Musa da Haruna suka ce wa dukan Isra’ila, “Da yamma za ku sani Ubangiji ne ya fitar da ku daga Masar.
Og Moses og Aron sagde til alle Israeliterne: "I Aften skal I kende, at det er HERREN, som har ført eder ud af Ægypten,
7 Da safe za ku ga ɗaukakar Ubangiji, saboda ya ji gunaguninku a kansa. Wane mu, da za ku yi gunaguni a kanmu?”
og i Morgen skal I skue HERRENs Herlighed, thi han har hørt eders Knurren mod HERREN; thi hvad er vel vi, at I knurrer mod os!"
8 Musa ya kuma ce, “Za ku san cewa shi ne Ubangiji, sa’ad da ya ba ku nama ku ci da yamma, da kuma duk burodin da kuke so da safe, saboda ya ji gunagunin da kuka yi a kansa. Namu a wane? Ai, gunaguninku ba a kanmu ba, amma a kan Ubangiji ne.”
Og Moses tilføjede: "Det skal ske, når HERREN i Aften giver eder Kød at spise og i Morgen Brød at mætte eder med; thi HERREN har hørt, hvorledes I knurrer mod ham; thi hvad er vi? Thi det er ikke os, I knurrer imod, men HERREN."
9 Sai Musa ya ce wa Haruna, “Ka faɗa wa dukan taron Isra’ila, ‘Ku zo gaban Ubangiji, gama ya ji gunaguninku.’”
Derpå sagde Moses til Aron: "Sig til hele Israeliternes Menighed: Træd frem for HERRENs Åsyn, thi han har hørt eders Knurren!"
10 Yayinda Haruna yake magana da dukan taron Isra’ila, sai suka duba wajen hamada, sai ga ɗaukakar Ubangiji tana bayyana a girgije.
Og da Aron sagde det til hele Israeliternes Menighed, vendte de sig mod Ørkenen, og se, HERRENs Herlighed viste sig i Skyen.
11 Ubangiji ya ce wa Musa,
Da talede HERREN til Moses og sagde:
12 “Na ji gunagunin Isra’ilawa. Ka faɗa musu, ‘A tsakanin fāɗuwar rana da almuru, za ku ci nama, da safe kuma za ku ƙoshi da burodi. Sa’an nan za ku sani ni ne Ubangiji Allahnku.’”
"Jeg har hørt Israeliternes Knurren; sig til dem: Ved Aftenstid skal I få Kød at spise, og i Morgen tidlig skal I få Brød at mætte eder med, og I skal kende, at jeg er HERREN eders Gud."
13 Da yamman wannan rana, sai makware suka rufe dukan sansani, da safe kuma sai ga raɓa ta kewaye sansani.
Da det nu blev Aften, kom en Sværm Vagtler flyvende og faldt i et tykt Lag over Lejren; og næste Morgen lå Duggen tæt rundt om Lejren,
14 Lokacin da raɓar ta watse, sai ga wani abu kamar tsaki, falle-falle kuma da laushi, fari, kamar hazo, a ƙasa.
og da Duggen svandt, var Ørkenen dækket med noget fint, skælagtigt noget, noget fint der lignede Rim på Jorden.
15 Sa’ad da Isra’ilawa suka ga wannan, sai suka ce wa junansu, “Mene ne wannan?” Gama ba su san ko mene ne ba. Musa ya ce musu, “Wannan shi ne burodin da Ubangiji ya ba ku ku ci.
Da Israeliterne så det, spurgte de hverandre: "Hvad er det?" Thi de vidste ikke, hvad det var; men Moses sagde til dem: "Det er det Brød, HERREN har givet eder til Føde!
16 Wannan shi ne abin da Ubangiji ya umarta, ‘Kowane mutum zai tattara bisa ga bukatarsa. Ku tara rabin gallon don mutum guda da yake cikin tentinku.’”
Og således har HERREN påbudt: I skal samle deraf, enhver så meget som han har behov, en Omer for hvert Hoved; I skal tage deraf i Forhold til Antallet af eders Husfolk, enhver skal tage deraf til dem, der er i hans Telt!"
17 Isra’ilawa suka yi kamar yadda aka faɗa musu, waɗansu suka tattara da yawa, waɗansu kuma kaɗan.
Israeliterne gjorde nu således, og de samlede, nogle mere og andre mindre;
18 Da suka gwada a mudu, wanda ya tattara da yawa bai sami mafi yawa ba, wanda kuma ya tattara kaɗan bai sami ƙanƙani ba. Kowane mutum ya tattara daidai bukatarsa.
og da de målte det med Omeren, havde den, der havde meget, ikke for meget, og den, der havde lidt, ikke for lidt, enhver havde samlet, hvad han behøvede til Føde.
19 Sa’an nan Musa ya ce musu, “Kada wani yă bar saura har safe.”
Derpå sagde Moses til dem: "Ingen må gemme noget deraf til næste Morgen!"
20 Duk da haka waɗansu ba su kula da umarnin Musa ba, suka bar saura har safe, kashegari kuwa ta yi tsutsotsi, ta ruɓe, sai Musa ya yi fushi da su.
Dog adlød de ikke Moses, og nogle af dem gemte noget deraf til næste Morgen; men da var det fuldt af Orme og lugtede. Da blev Moses vred på dem.
21 Kowace safiya, kowanne mutum yakan tattara daidai bukatarsa, lokacin da rana ta yi zafi, sai ta narke.
Således samlede de nu hver Morgen, enhver så meget som han havde behov. Men når Solen begyndte at brænde, smeltede det.
22 A rana ta shida, suka tattara ninki biyu, mudu biyu ga mutum guda, sai shugabannin taron suka zo suka kawo ƙara wurin Musa.
På den sjette Ugedag havde de samlet dobbelt så meget Brød, to Omer for hver Person. Og alle Menighedens Øverster kom og sagde det til Moses;
23 Shi kuma ya ce musu, “Wannan shi ne umarnin Ubangiji, ‘Gobe za tă zama ranar hutu, Asabbaci mai tsarki ga Ubangiji. Domin haka sai ku toya abin da kuke so ku toya, ku kuma dafa abin da kuke so ku dafa. Abin da ya rage ku ajiye har safe.’”
men han sagde til dem: "Det er netop, som HERREN har sagt. I Morgen er det Hviledag, en hellig Sabbat for HERREN. Bag, hvad I vil bage, og kog, hvad I vil koge, men læg det tiloversblevne til Side for at gemme det til i Morgen!"
24 Sai suka bar saura har safe, kamar yadda Musa ya umarta, bai kuwa yi wari ko yă yi tsutsa ba.
De lagde det da til Side til næste Dag, som Moses havde befalet, og det kom ikke til at lugte, og der gik ikke Orm deri.
25 Musa ya ce, “Ku ci shi yau, saboda yau Asabbaci ne na Ubangiji. Ba za ku same shi a ƙasa a yau ba.
Derpå sagde Moses: "Det skal I spise i Dag, thi i Dag er det Sabbat for HERREN; i Dag finder I intet ude på Marken.
26 Kwana shida za ku tattara shi, amma a rana ta bakwai, Asabbaci, ba za a same shi ba.”
I seks bage skal I samle det, men på den syvende Dag, på Sabbaten, er der intet at finde."
27 Duk da haka waɗansu mutane suka fita a ranar Asabbaci don su tattara, amma ba su sami kome ba.
Alligevel var der nogle blandt Folket, der gik ud på den syvende Dag for at samle; men de fandt intet.
28 Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Har yaushe za ku ƙi bin dokokina da umarnaina?
Da sagde HERREN til Moses: "Hvor længe vil I vægre eder ved at holde mine Bud og Love?
29 Ku lura fa, ai, Ubangiji ne ya ba ku Asabbaci; shi ya sa a kan ba ku burodi na kwana biyu, a rana ta shida. Kowa ya kamata yă kasance inda yake a rana ta bakwai; kada kowa yă fita.”
Betænk dog, at HERREN har givet eder Sabbaten! Derfor giver han eder på den sjette Dag Brød til to Dage. Enhver af eder skal blive, hvor han er, og ingen må forlade sin Bolig på den syvende Dag!"
30 Sai mutanen suka huta a rana ta bakwai.
Da hvilede Folket på den syvende Dag.
31 Mutanen Isra’ila suka kira burodin Manna. Manna yana nan fari kamar farin riɗi, ɗanɗanonsa kuma yana kama da masa da aka yi da zuma.
Men Israeliterne kaldte det Manna; det lignede hvide Korianderfrø og smagte som Honningkager.
32 Musa ya ce, “Wannan shi ne abin da Ubangiji ya umarta, ‘Ku auna mudu guda na Manna, a adana ta dukan zamananku, domin kowane zamani yă ga irin abincin da na ba ku ku ci a hamada, yayinda na fitar da ku daga Masar.’”
Moses sagde fremdeles: "Således har HERREN påbudt: En Omer fuld deraf skal gemmes til eders Efterkommere, for at de kan se det Brød, jeg gav eder at spise i Ørkenen, da jeg førte eder ud af Ægypten!"
33 Saboda haka Musa ya ce wa Haruna, “Ka ɗauki tulu, ka sa mudu guda na Manna a ciki. Sa’an nan ka sa shi a gaban Ubangiji, don a adana don tsararraki masu zuwa.”
Og Moses sagde til Aron: "Tag en Krukke, kom en Omer Manna deri og stil den foran HERRENs Åsyn for at gemmes til eders Efterkommere!"
34 Sai Haruna ya ajiye Mannar a gaban Akwatin Alkawari, don a adana ta kamar yadda Ubangiji ya umarci Musa.
Og Aron gjorde, som HERREN havde pålagt Moses, og han stillede den foran Vidnesbyrdet for at gemmes.
35 Isra’ilawa suka yi shekaru arba’in suna cin Manna, har sai da suka shiga cikin ƙasar da take da mutane, suka ci Manna har zuwa kan iyakar ƙasar Kan’ana.
Og Israeliterne spiste Manna i fyrretyve År, indtil de kom til beboede Egne; de spiste Manna, indtil de kom til Grænsen af Kana'ans Land.
36 (Omer guda, daidai ne da kashi ɗaya bisa goma na Efa.)
En Omer er Tiendedelen af en Efa.

< Fitowa 16 >