< Fitowa 15 >

1 Sa’an nan Musa da Isra’ilawa suka rera wannan waƙa ga Ubangiji suka ce, “Zan rera waƙa ga Ubangiji gama an ɗaukaka shi ƙwarai. Doki da mahayinsa ya jefa su cikin teku.
آنگاه موسی و بنی‌اسرائیل در ستایش خداوند این سرود را خواندند: «خداوند را می‌سراییم که شکوهمندانه پیروز شده است، او اسبها و سوارانشان را به دریا افکنده است.
2 “Ubangiji ne ƙarfina da mafakata, ya zama cetona. Shi Allahna ne, zan yabe shi. Allah na kakana, zan ɗaukaka shi.
خداوند قوت و سرود من است، و نجات من گردیده. او خدای من است، پس او را سپاس خواهم گفت. او خدای نیاکان من است، پس او را برمی‌افرازم.
3 Ubangiji mai yaƙi ne Ubangiji ne sunansa.
او جنگاور است و نامش خداوند می‌باشد.
4 Karusan Fir’auna da sojojinsa ya jefa cikin teku. Zaɓaɓɓun jarumawansa ya nutsar da su cikin Bahar Maliya.
خداوند، لشکر و ارابه‌های فرعون را به دریا سرنگون کرد. مبارزان برگزیدهٔ مصر در دریای سرخ غرق شدند.
5 Zurfafan ruwaye sun rufe su; suka nutse cikin zurfi kamar dutse.
آبهای دریا آنها را پوشاندند، و آنها مانند سنگ به اعماق آب فرو رفتند.
6 Hannun damanka, ya Ubangiji, Mai kwarjini ne da iko, hannun damanka, ya Ubangiji, ya farfashe magabci.
«دست راست تو ای خداوند، قدرت عظیمی دارد. به نیروی دستت، دشمنانت را در هم کوبیدی.
7 “A cikin girman kwarjininka ka kā da waɗanda sun yi gāba da kai. Ka aiki fushinka mai zafi ya cinye su kamar tattaka.
با عظمت شکوهت دشمنان را نابود ساختی، آتش خشم تو، ایشان را همچون کاه سوزانید.
8 Da hucin numfashin hancinka ruwaye suka tattaru. Ruwaye masu kwararowa, suka tsaya kamar bango; ruwaye na zurfafa suka daskare a tsakiyar teku.
تو بر دریا دمیدی و آن را شکافتی، آبها مانند دیوار ایستادند و عمق دریا خشک گردید.
9 Magabci ya yi fahariya, cewa ‘Zan fafare su, in ci musu. Zan raba ganima; abin da na so ya samu. Zan ja takobina hannuna kuwa zai hallaka su.’
«دشمن گفت:”آنها را تعقیب کرده، می‌گیرم و با شمشیرم هلاک می‌کنم، ثروتشان را تقسیم کرده، هر چه بخواهم برای خود برمی‌دارم.“
10 Amma ka hura numfashinka sai teku ya rufe su. Suka nutse kamar darma cikin manyan ruwaye.
اما تو ای خداوند، چون بر دریا دمیدی موجها یکباره آنها را پوشانید، همگی مثل سرب در دریای خروشان غرق شدند.
11 Wane ne cikin alloli, ya yi kamar ka, ya Ubangiji? Wane ne kamar ka, mai ɗaukaka cikin tsarki, mai banrazana cikin ɗaukaka, mai aikata al’ajabai?
«کیست مانند تو ای خداوند در میان خدایان؟ کیست مثل تو عظیم در قدوسیت؟ کیست که مانند تو بتواند کارهای مهیب و عجیب انجام دهد؟
12 “Ka miƙa hannunka na dama, ƙasa ta haɗiye abokan gābanka.
چون دست راست خود را دراز کردی، زمین، دشمنان ما را بلعید.
13 A cikin ƙaunarka marar iyaka, za ka bishe mutanen da ka fansa. A cikin ƙarfinka, za ka bishe su zuwa mazauninka mai tsarki.
«قوم خود را که بازخرید نموده‌ای با رحمت خود رهبری خواهی فرمود. تو آنها را با قدرت خود به سرزمین مقدّست هدایت خواهی کرد.
14 Al’ummai za su ji, su yi rawar jiki tsoro zai kama mutanen Filistiya.
قومها وقتی این را بشنوند مضطرب خواهند شد، ساکنان فلسطین از ترس خواهند لرزید،
15 Sarakunan Edom za su tsorata, shugabannin Mowab za su yi rawar jiki, mutanen Kan’ana za su narke.
امیران ادوم وحشت خواهند کرد، بزرگان موآب خواهند لرزید. وحشت، مردم کنعان را فرو خواهد گرفت.
16 Razana da tsoro za su fāɗo a kansu. Da ikon hannunka za su tsaya cik kamar dutse, har sai mutanen da ka kawo sun wuce, ya Ubangiji.
ترس و دلهره بر ایشان غلبه خواهد کرد. ای خداوند از قدرت تو، آنها چون سنگ، خاموش خواهند ایستاد، تا قوم تو که آنها را خریده‌ای از کنار ایشان بگذرند.
17 Za ka kawo su, ka dasa su a kan dutsen nan naka inda, ya Ubangiji, ka shirya domin mazauninka, wuri mai tsarkin da hannuwanka suka kafa, ya Ubangiji.
ای خداوند، تو ایشان را به کوه مقدّس خود بیاور و در همان جایی که برای سکونت خود انتخاب کرده‌ای و خانهٔ خود را در آن ساخته‌ای، ساکن ساز.
18 “Ubangiji zai yi mulki har abada abadin.”
خداوندا، تو تا ابد سلطنت خواهی کرد.»
19 Sa’ad da dawakai, kekunan yaƙi da mahayan dawakan Fir’auna suka shiga cikin teku, Ubangiji ya mayar da ruwan teku a kansu, amma Isra’ilawa suka wuce a cikin teku a busasshiyar ƙasa.
وقتی اسبهای فرعون با ارابه‌ها و سوارانش به دنبال اسرائیلی‌ها وارد دریا شدند، خداوند آب دریا را به سمت ایشان برگردانید، اما اسرائیلی‌ها از میان دریا به خشکی رسیدند.
20 Sa’an nan Miriyam annabiya,’yar’uwar Haruna ta ɗauki ganga a hannunta, dukan mata kuwa suka bi ta, da ganguna suna rawa.
پس از خواندن این سرود، مریم نبیه، خواهر هارون دف به دست گرفت و به رقصیدن پرداخت و زنان دیگر نیز به دنبال وی چنین کردند،
21 Miriyam ta yi musu waƙa. “Ku rera ga Ubangiji gama ya ci gawurtacciyar nasara. Doki da mahayi, ya jefa cikin teku.”
و مریم این سرود را خطاب به ایشان خواند: «خداوند را بسرایید که شکوهمندانه پیروز شده است، او اسبها و سوارانشان را به دریا افکنده است.»
22 Sai Musa ya jagoranci Isra’ila daga jan teku zuwa hamadar Shur. Kwana uku suka yi tafiya cikin hamada ba su sami ruwa ba.
موسی قوم اسرائیل را از دریای سرخ حرکت داد و به طرف صحرای شور هدایت کرد. ولی در آن صحرا پس از سه روز راهپیمایی، قطره‌ای آب نیافتند.
23 Da suka zo Mara, ba su iya shan ruwan ba saboda yana da ɗaci (shi ya sa ake kira wurin Mara).
سپس آنها به ماره رسیدند، ولی از آب آنجا نیز نتوانستند بنوشند، چون تلخ بود. (از این جهت آن مکان را ماره یعنی «تلخ» نامیدند.)
24 Sai mutanen suka yi gunaguni a kan Musa, suna cewa, “Me za mu sha?”
پس مردم غرغرکنان به موسی گفتند: «ما تشنه‌ایم؛ چه بنوشیم؟»
25 Sai Musa ya yi kuka ga Ubangiji, Ubangiji kuwa ya nuna masa wani itace. Sai ya jefa shi cikin ruwan, sai ruwan ya zama mai daɗi. A can Ubangiji ya yi musu doka da farilla, a can kuma ya gwada su.
موسی نزد خداوند دعا کرد و خداوند چوبی به او نشان داد و فرمود: «این چوب را در آب ماره بینداز تا آن را شیرین کند.» موسی چنین کرد و آب، شیرین شد. در ماره، خداوند دستورهایی به قوم اسرائیل داد تا اطاعت آنها را آزمایش کرده باشد.
26 Ya ce, “In kun kasa kunne ga muryar Ubangiji Allahnku kuka yi abin da yake daidai a idanunsa, in kun mai da hankali ga umarnansa, kuka kiyaye dukan farillansa, ba zan kawo muku wani ciwon da na kawo a kan Masarawa ba, gama ni ne Ubangiji da nake warkar da ku.”
او فرمود: «اگر دستورها و احکام مرا که خداوند، خدای شما هستم اطاعت کنید و آنچه را که در نظر من پسندیده است بجا آورید، از تمام بیماریهایی که مصری‌ها را بدان دچار ساختم در امان خواهید ماند، زیرا من، خداوند، شفا دهندهٔ شما هستم.»
27 Sai suka zo Elim inda akwai maɓulɓulan ruwa goma sha biyu da itatuwan dabino saba’in, suka sauka a can, kusa da ruwa.
سپس بنی‌اسرائیل به ایلیم آمدند. در آنجا دوازده چشمه و هفتاد درخت خرما بود؛ پس در کنار چشمه‌ها اردو زدند.

< Fitowa 15 >