< Fitowa 15 >

1 Sa’an nan Musa da Isra’ilawa suka rera wannan waƙa ga Ubangiji suka ce, “Zan rera waƙa ga Ubangiji gama an ɗaukaka shi ƙwarai. Doki da mahayinsa ya jefa su cikin teku.
Alors, Moïse chanta, avec les fils d'Israël, ce cantique au Seigneur; ils dirent: Chantons au Seigneur, car il s'est glorifié avec éclat, et il a précipité dans la mer le cheval et le cavalier.
2 “Ubangiji ne ƙarfina da mafakata, ya zama cetona. Shi Allahna ne, zan yabe shi. Allah na kakana, zan ɗaukaka shi.
Il m'a sauvé, il a été mon secours et mon protecteur; c'est mon Dieu, et je le glorifierai; c'est le Dieu de mon père, et je l'exalterai;
3 Ubangiji mai yaƙi ne Ubangiji ne sunansa.
C'est le Seigneur qui broie les armées, le Seigneur est son nom.
4 Karusan Fir’auna da sojojinsa ya jefa cikin teku. Zaɓaɓɓun jarumawansa ya nutsar da su cikin Bahar Maliya.
Il a précipité dans la mer les chars du Pharaon et son armée, et les grands de son royaume montés sur des chars; la mer Rouge les a engloutis.
5 Zurfafan ruwaye sun rufe su; suka nutse cikin zurfi kamar dutse.
Il les a cachés sous les flots; ils se sont enfoncés dans l'abîme comme une pierre.
6 Hannun damanka, ya Ubangiji, Mai kwarjini ne da iko, hannun damanka, ya Ubangiji, ya farfashe magabci.
Votre droite, Seigneur, a été glorifiée en sa force; votre main droite, Seigneur, a brisé les ennemis.
7 “A cikin girman kwarjininka ka kā da waɗanda sun yi gāba da kai. Ka aiki fushinka mai zafi ya cinye su kamar tattaka.
À la plénitude de votre gloire, vous avez exterminé nos persécuteurs, vous avez déchaîné votre colère; elle les a dévorés comme de la paille.
8 Da hucin numfashin hancinka ruwaye suka tattaru. Ruwaye masu kwararowa, suka tsaya kamar bango; ruwaye na zurfafa suka daskare a tsakiyar teku.
Au souffle de votre colère, l'eau s'est séparée, les eaux se sont dressées comme une tour; les flots se sont affermis au milieu de la mer.
9 Magabci ya yi fahariya, cewa ‘Zan fafare su, in ci musu. Zan raba ganima; abin da na so ya samu. Zan ja takobina hannuna kuwa zai hallaka su.’
L'ennemi a dit: Je poursuivrai, je saisirai, je partagerai les dépouilles; je rassasierai mon âme, je tuerai à coups de glaive; ma main prévaudra.
10 Amma ka hura numfashinka sai teku ya rufe su. Suka nutse kamar darma cikin manyan ruwaye.
Vous avez envoyé votre souffle: la mer les a cachés; ils ont été submergés, comme du plomb, sous les ondes impétueuses.
11 Wane ne cikin alloli, ya yi kamar ka, ya Ubangiji? Wane ne kamar ka, mai ɗaukaka cikin tsarki, mai banrazana cikin ɗaukaka, mai aikata al’ajabai?
Qui donc est semblable à vous parmi les dieux, ô Seigneur? Qui donc est semblable à vous, Dieu, glorifié au milieu des saints, admirable en gloire, fécond en prodiges?
12 “Ka miƙa hannunka na dama, ƙasa ta haɗiye abokan gābanka.
Vous avez étendu votre droite, la terre les a engloutis.
13 A cikin ƙaunarka marar iyaka, za ka bishe mutanen da ka fansa. A cikin ƙarfinka, za ka bishe su zuwa mazauninka mai tsarki.
Dans votre justice vous avez guidé votre peuple que vous avez racheté, vous l'avez consolé par votre force, pour le conduire au séjour saint de votre repos.
14 Al’ummai za su ji, su yi rawar jiki tsoro zai kama mutanen Filistiya.
Les nations ont entendu et se sont irritées; les douleurs de la femme qui enfante ont saisi le peuple Philistin.
15 Sarakunan Edom za su tsorata, shugabannin Mowab za su yi rawar jiki, mutanen Kan’ana za su narke.
Les chefs d'Edom et les princes des Moabites se sont hâtés, la crainte les a frappés; tous ceux de Chanaan se sont consumés.
16 Razana da tsoro za su fāɗo a kansu. Da ikon hannunka za su tsaya cik kamar dutse, har sai mutanen da ka kawo sun wuce, ya Ubangiji.
Que la terreur et l'épouvantement les assaillent; qu'ils soient pétrifiés par la grandeur de votre bras, jusqu'à ce que soit passé votre peuple, ô Seigneur, jusqu'à ce que soit passé ce peuple que vous avez acquis.
17 Za ka kawo su, ka dasa su a kan dutsen nan naka inda, ya Ubangiji, ka shirya domin mazauninka, wuri mai tsarkin da hannuwanka suka kafa, ya Ubangiji.
Conduisez ce peuple, établissez-le en la montagne de votre héritage, en la demeure digne de vous que vous vous êtes préparée, Seigneur, en ce lieu consacré qu'ont préparé vos mains.
18 “Ubangiji zai yi mulki har abada abadin.”
Le Seigneur règne sur les siècles, sur les siècles et au delà.
19 Sa’ad da dawakai, kekunan yaƙi da mahayan dawakan Fir’auna suka shiga cikin teku, Ubangiji ya mayar da ruwan teku a kansu, amma Isra’ilawa suka wuce a cikin teku a busasshiyar ƙasa.
Les chevaux du Pharaon, ses chars et leurs écuyers, sont entrés dans la mer; et le Seigneur a ramené sur eux les flots, et les fils d'Israël ont marché à pied sec au fond de la mer.
20 Sa’an nan Miriyam annabiya,’yar’uwar Haruna ta ɗauki ganga a hannunta, dukan mata kuwa suka bi ta, da ganguna suna rawa.
Alors, Marie, la prophétesse, sœur d'Aaron, prit en ses mains un tambour, et toutes les femmes sortirent à sa suite, en dansant et en frappant leurs tambours.
21 Miriyam ta yi musu waƙa. “Ku rera ga Ubangiji gama ya ci gawurtacciyar nasara. Doki da mahayi, ya jefa cikin teku.”
Et Marie entonna le chœur, disant: Chantons au Seigneur, car il s'est glorifié avec éclat; il a précipité dans la mer le cheval et le cavalier.
22 Sai Musa ya jagoranci Isra’ila daga jan teku zuwa hamadar Shur. Kwana uku suka yi tafiya cikin hamada ba su sami ruwa ba.
Après cela, Moïse fit quitter aux fils d'Israël les bords de la mer Rouge, et il les conduisit dans le désert de Sur. Ils firent trois journées de marche dans le désert, et ils ne trouvèrent point d'eau à boire.
23 Da suka zo Mara, ba su iya shan ruwan ba saboda yana da ɗaci (shi ya sa ake kira wurin Mara).
Arrivés à Mara, ils ne purent boire l'eau qui s'y trouvait, parce qu'elle était amère; c'est pourquoi ils appelèrent ce lieu Amertume (Mara).
24 Sai mutanen suka yi gunaguni a kan Musa, suna cewa, “Me za mu sha?”
Et le peuple murmura contre Moïse, disant: Que boirons-nous?
25 Sai Musa ya yi kuka ga Ubangiji, Ubangiji kuwa ya nuna masa wani itace. Sai ya jefa shi cikin ruwan, sai ruwan ya zama mai daɗi. A can Ubangiji ya yi musu doka da farilla, a can kuma ya gwada su.
Moïse aussitôt cria au Seigneur, et le Seigneur lui montra un arbre dont il jeta le bois dans l'eau; et l'eau devint douce. Là, Dieu lui proposa sa loi et sa justice, après l'avoir éprouvé.
26 Ya ce, “In kun kasa kunne ga muryar Ubangiji Allahnku kuka yi abin da yake daidai a idanunsa, in kun mai da hankali ga umarnansa, kuka kiyaye dukan farillansa, ba zan kawo muku wani ciwon da na kawo a kan Masarawa ba, gama ni ne Ubangiji da nake warkar da ku.”
Et le Seigneur lui dit: Si tu écoutes la voix du Seigneur ton Dieu et fais ce qui lui est agréable, si tu observes ses commandements et restes docile à sa justice, je ne te frapperai d'aucune des plaies dont j'ai frappé l'Égypte, car je suis le Seigneur ton Dieu, ton Dieu qui te guéris.
27 Sai suka zo Elim inda akwai maɓulɓulan ruwa goma sha biyu da itatuwan dabino saba’in, suka sauka a can, kusa da ruwa.
De là, ils vinrent à Elim, où il y avait douze sources d'eau vive et soixante-dix palmiers; et ils campèrent au bord des eaux.

< Fitowa 15 >