< Fitowa 15 >
1 Sa’an nan Musa da Isra’ilawa suka rera wannan waƙa ga Ubangiji suka ce, “Zan rera waƙa ga Ubangiji gama an ɗaukaka shi ƙwarai. Doki da mahayinsa ya jefa su cikin teku.
Then Moses and the people of Israel sang this song to Yahweh. They sang, “I will sing to Yahweh, for he has triumphed gloriously; the horse and its rider he has thrown into the sea.
2 “Ubangiji ne ƙarfina da mafakata, ya zama cetona. Shi Allahna ne, zan yabe shi. Allah na kakana, zan ɗaukaka shi.
Yahweh is my strength and song, and he has become my salvation. This is my God, and I will praise him, my father's God, and I will exalt him.
3 Ubangiji mai yaƙi ne Ubangiji ne sunansa.
Yahweh is a warrior; Yahweh is his name.
4 Karusan Fir’auna da sojojinsa ya jefa cikin teku. Zaɓaɓɓun jarumawansa ya nutsar da su cikin Bahar Maliya.
He has thrown Pharaoh's chariots and army into the sea. Pharaoh's chosen officers were drowned in the Sea of Reeds.
5 Zurfafan ruwaye sun rufe su; suka nutse cikin zurfi kamar dutse.
The depths covered them; they went down into the depths like a stone.
6 Hannun damanka, ya Ubangiji, Mai kwarjini ne da iko, hannun damanka, ya Ubangiji, ya farfashe magabci.
Your right hand, Yahweh, is glorious in power; your right hand, Yahweh, has shattered the enemy.
7 “A cikin girman kwarjininka ka kā da waɗanda sun yi gāba da kai. Ka aiki fushinka mai zafi ya cinye su kamar tattaka.
In great majesty you overthrew those who rose up against you. You sent out your wrath; it consumed them like stubble.
8 Da hucin numfashin hancinka ruwaye suka tattaru. Ruwaye masu kwararowa, suka tsaya kamar bango; ruwaye na zurfafa suka daskare a tsakiyar teku.
By the blast of your nostrils the waters were piled up; the flowing waters stood upright in a heap; the deep water was congealed in the heart of the sea.
9 Magabci ya yi fahariya, cewa ‘Zan fafare su, in ci musu. Zan raba ganima; abin da na so ya samu. Zan ja takobina hannuna kuwa zai hallaka su.’
The enemy said, 'I will pursue, I will overtake, I will share out the plunder; my desire will be satisfied on them; I will draw my sword; my hand will destroy them.'
10 Amma ka hura numfashinka sai teku ya rufe su. Suka nutse kamar darma cikin manyan ruwaye.
But you blew with your wind, and the sea covered them; they sank like lead in the mighty waters.
11 Wane ne cikin alloli, ya yi kamar ka, ya Ubangiji? Wane ne kamar ka, mai ɗaukaka cikin tsarki, mai banrazana cikin ɗaukaka, mai aikata al’ajabai?
Who is like you, Yahweh, among the gods? Who is like you, majestic in holiness, honored in praises, doing miracles?
12 “Ka miƙa hannunka na dama, ƙasa ta haɗiye abokan gābanka.
You reached out with your right hand, and the earth swallowed them.
13 A cikin ƙaunarka marar iyaka, za ka bishe mutanen da ka fansa. A cikin ƙarfinka, za ka bishe su zuwa mazauninka mai tsarki.
In your covenant loyalty you have led the people you have rescued. In your strength you have led them to the holy place where you live.
14 Al’ummai za su ji, su yi rawar jiki tsoro zai kama mutanen Filistiya.
The peoples will hear, and they will tremble; terror will seize the inhabitants of Philistia.
15 Sarakunan Edom za su tsorata, shugabannin Mowab za su yi rawar jiki, mutanen Kan’ana za su narke.
Then the chiefs of Edom will fear; the soldiers of Moab will shake; all the inhabitants of Canaan will melt away.
16 Razana da tsoro za su fāɗo a kansu. Da ikon hannunka za su tsaya cik kamar dutse, har sai mutanen da ka kawo sun wuce, ya Ubangiji.
Terror and dread will fall on them. Because of your arm's power, they will become as still as a stone until your people pass by, Yahweh— until the people you have rescued pass by.
17 Za ka kawo su, ka dasa su a kan dutsen nan naka inda, ya Ubangiji, ka shirya domin mazauninka, wuri mai tsarkin da hannuwanka suka kafa, ya Ubangiji.
You will bring them and plant them on the mountain of your inheritance, the place, Yahweh, that you have made to live in, the sanctuary, our Lord, that your hands have built.
18 “Ubangiji zai yi mulki har abada abadin.”
Yahweh will reign forever and ever.”
19 Sa’ad da dawakai, kekunan yaƙi da mahayan dawakan Fir’auna suka shiga cikin teku, Ubangiji ya mayar da ruwan teku a kansu, amma Isra’ilawa suka wuce a cikin teku a busasshiyar ƙasa.
For Pharaoh's horses went with his chariots and horsemen into the sea. Yahweh brought back the waters of the sea on them. But the Israelites walked on dry land in the middle of the sea.
20 Sa’an nan Miriyam annabiya,’yar’uwar Haruna ta ɗauki ganga a hannunta, dukan mata kuwa suka bi ta, da ganguna suna rawa.
Miriam the prophetess, sister of Aaron, picked up a tambourine, and all the women went out with tambourines, dancing along with her.
21 Miriyam ta yi musu waƙa. “Ku rera ga Ubangiji gama ya ci gawurtacciyar nasara. Doki da mahayi, ya jefa cikin teku.”
Miriam sang to them: “Sing to Yahweh, for he has triumphed gloriously. The horse and his rider he has thrown into the sea.”
22 Sai Musa ya jagoranci Isra’ila daga jan teku zuwa hamadar Shur. Kwana uku suka yi tafiya cikin hamada ba su sami ruwa ba.
Then Moses led Israel onward from the Sea of Reeds. They went out into the wilderness of Shur. They traveled for three days into the wilderness and found no water.
23 Da suka zo Mara, ba su iya shan ruwan ba saboda yana da ɗaci (shi ya sa ake kira wurin Mara).
Then they came to Marah, but they could not drink the water there because it was bitter. So they called that place Marah.
24 Sai mutanen suka yi gunaguni a kan Musa, suna cewa, “Me za mu sha?”
So the people complained to Moses and said, “What can we drink?”
25 Sai Musa ya yi kuka ga Ubangiji, Ubangiji kuwa ya nuna masa wani itace. Sai ya jefa shi cikin ruwan, sai ruwan ya zama mai daɗi. A can Ubangiji ya yi musu doka da farilla, a can kuma ya gwada su.
Moses cried out to Yahweh, and Yahweh showed him a tree. Moses threw it into the water, and the water became sweet to drink. It was there that Yahweh gave them a strict law, and it was there that he tested them.
26 Ya ce, “In kun kasa kunne ga muryar Ubangiji Allahnku kuka yi abin da yake daidai a idanunsa, in kun mai da hankali ga umarnansa, kuka kiyaye dukan farillansa, ba zan kawo muku wani ciwon da na kawo a kan Masarawa ba, gama ni ne Ubangiji da nake warkar da ku.”
He said, “If you carefully listen to the voice of Yahweh your God, and do what is right in his eyes, and if you give ear to his commands and obey all his laws—I will put on you none of the diseases that I put on the Egyptians, for I am Yahweh who heals you.”
27 Sai suka zo Elim inda akwai maɓulɓulan ruwa goma sha biyu da itatuwan dabino saba’in, suka sauka a can, kusa da ruwa.
Then the people came to Elim, where there were twelve springs of water and seventy palm trees. They camped there by the water.