< Fitowa 15 >

1 Sa’an nan Musa da Isra’ilawa suka rera wannan waƙa ga Ubangiji suka ce, “Zan rera waƙa ga Ubangiji gama an ɗaukaka shi ƙwarai. Doki da mahayinsa ya jefa su cikin teku.
then to sing Moses and son: descendant/people Israel [obj] [the] song [the] this to/for LORD and to say to/for to say to sing to/for LORD for to rise up to rise up horse and to ride his to shoot in/on/with sea
2 “Ubangiji ne ƙarfina da mafakata, ya zama cetona. Shi Allahna ne, zan yabe shi. Allah na kakana, zan ɗaukaka shi.
strength my and song LORD and to be to/for me to/for salvation this God my and to beautify him God father my and to exalt him
3 Ubangiji mai yaƙi ne Ubangiji ne sunansa.
LORD man battle LORD name his
4 Karusan Fir’auna da sojojinsa ya jefa cikin teku. Zaɓaɓɓun jarumawansa ya nutsar da su cikin Bahar Maliya.
chariot Pharaoh and strength: soldiers his to shoot in/on/with sea and best officer his to sink in/on/with sea Red (Sea)
5 Zurfafan ruwaye sun rufe su; suka nutse cikin zurfi kamar dutse.
abyss to cover them to go down in/on/with depth like stone
6 Hannun damanka, ya Ubangiji, Mai kwarjini ne da iko, hannun damanka, ya Ubangiji, ya farfashe magabci.
right your LORD be glorious in/on/with strength right your LORD to shatter enemy
7 “A cikin girman kwarjininka ka kā da waɗanda sun yi gāba da kai. Ka aiki fushinka mai zafi ya cinye su kamar tattaka.
and in/on/with abundance pride your to overthrow to arise: attack you to send: depart burning anger your to eat them like/as stubble
8 Da hucin numfashin hancinka ruwaye suka tattaru. Ruwaye masu kwararowa, suka tsaya kamar bango; ruwaye na zurfafa suka daskare a tsakiyar teku.
and in/on/with spirit: breath face: nose your to pile up water to stand like heap to flow to congeal abyss in/on/with heart sea
9 Magabci ya yi fahariya, cewa ‘Zan fafare su, in ci musu. Zan raba ganima; abin da na so ya samu. Zan ja takobina hannuna kuwa zai hallaka su.’
to say enemy to pursue to overtake to divide spoil to fill them soul: appetite my to empty sword my to possess: take them hand: power my
10 Amma ka hura numfashinka sai teku ya rufe su. Suka nutse kamar darma cikin manyan ruwaye.
to blow in/on/with spirit: breath your to cover them sea to sink like/as lead in/on/with water great
11 Wane ne cikin alloli, ya yi kamar ka, ya Ubangiji? Wane ne kamar ka, mai ɗaukaka cikin tsarki, mai banrazana cikin ɗaukaka, mai aikata al’ajabai?
who? like you in/on/with god LORD who? like you be glorious in/on/with holiness to fear: revere praise to make: do wonder
12 “Ka miƙa hannunka na dama, ƙasa ta haɗiye abokan gābanka.
to stretch right your to swallow up them land: soil
13 A cikin ƙaunarka marar iyaka, za ka bishe mutanen da ka fansa. A cikin ƙarfinka, za ka bishe su zuwa mazauninka mai tsarki.
to lead in/on/with kindness your people this to redeem: redeem to guide in/on/with strength your to(wards) pasture holiness your
14 Al’ummai za su ji, su yi rawar jiki tsoro zai kama mutanen Filistiya.
to hear: hear people to tremble [emph?] agony to grasp to dwell Philistia
15 Sarakunan Edom za su tsorata, shugabannin Mowab za su yi rawar jiki, mutanen Kan’ana za su narke.
then to dismay chief Edom leader Moab to grasp them trembling to melt all to dwell Canaan
16 Razana da tsoro za su fāɗo a kansu. Da ikon hannunka za su tsaya cik kamar dutse, har sai mutanen da ka kawo sun wuce, ya Ubangiji.
to fall: fall upon them terror and dread in/on/with great: large arm your to silence: stationary like/as stone till to pass people your LORD till to pass people this to buy
17 Za ka kawo su, ka dasa su a kan dutsen nan naka inda, ya Ubangiji, ka shirya domin mazauninka, wuri mai tsarkin da hannuwanka suka kafa, ya Ubangiji.
to come (in): bring them and to plant them in/on/with mountain: mount inheritance your foundation to/for to dwell you to work LORD sanctuary Lord to establish: establish hand your
18 “Ubangiji zai yi mulki har abada abadin.”
LORD to reign to/for forever: enduring and perpetuity
19 Sa’ad da dawakai, kekunan yaƙi da mahayan dawakan Fir’auna suka shiga cikin teku, Ubangiji ya mayar da ruwan teku a kansu, amma Isra’ilawa suka wuce a cikin teku a busasshiyar ƙasa.
for to come (in): come horse Pharaoh in/on/with chariot his and in/on/with horseman his in/on/with sea and to return: return LORD upon them [obj] water [the] sea and son: descendant/people Israel to go: walk in/on/with dry land in/on/with midst [the] sea
20 Sa’an nan Miriyam annabiya,’yar’uwar Haruna ta ɗauki ganga a hannunta, dukan mata kuwa suka bi ta, da ganguna suna rawa.
and to take: take Miriam [the] prophetess sister Aaron [obj] [the] tambourine in/on/with hand her and to come out: come all [the] woman after her in/on/with tambourine and in/on/with dance
21 Miriyam ta yi musu waƙa. “Ku rera ga Ubangiji gama ya ci gawurtacciyar nasara. Doki da mahayi, ya jefa cikin teku.”
and to sing to/for them Miriam to sing to/for LORD for to rise up to rise up horse and to ride his to shoot in/on/with sea
22 Sai Musa ya jagoranci Isra’ila daga jan teku zuwa hamadar Shur. Kwana uku suka yi tafiya cikin hamada ba su sami ruwa ba.
and to set out Moses [obj] Israel from sea Red (Sea) and to come out: come to(wards) wilderness Shur and to go: went three day in/on/with wilderness and not to find water
23 Da suka zo Mara, ba su iya shan ruwan ba saboda yana da ɗaci (shi ya sa ake kira wurin Mara).
and to come (in): come Marah [to] and not be able to/for to drink water from Marah for bitter they(masc.) upon so to call: call by name her Marah
24 Sai mutanen suka yi gunaguni a kan Musa, suna cewa, “Me za mu sha?”
and to grumble [the] people upon Moses to/for to say what? to drink
25 Sai Musa ya yi kuka ga Ubangiji, Ubangiji kuwa ya nuna masa wani itace. Sai ya jefa shi cikin ruwan, sai ruwan ya zama mai daɗi. A can Ubangiji ya yi musu doka da farilla, a can kuma ya gwada su.
and to cry to(wards) LORD and to show him LORD tree: stick and to throw to(wards) [the] water and be sweet [the] water there to set: make to/for him statute: decree and justice: judgement and there to test him
26 Ya ce, “In kun kasa kunne ga muryar Ubangiji Allahnku kuka yi abin da yake daidai a idanunsa, in kun mai da hankali ga umarnansa, kuka kiyaye dukan farillansa, ba zan kawo muku wani ciwon da na kawo a kan Masarawa ba, gama ni ne Ubangiji da nake warkar da ku.”
and to say if to hear: hear to hear: hear to/for voice LORD God your and [the] upright in/on/with eye: appearance his to make: do and to listen to/for commandment his and to keep: obey all statute: decree his all [the] sickness which to set: put in/on/with Egypt not to set: put upon you for I LORD to heal you
27 Sai suka zo Elim inda akwai maɓulɓulan ruwa goma sha biyu da itatuwan dabino saba’in, suka sauka a can, kusa da ruwa.
and to come (in): come Elim [to] and there two ten spring water and seventy palm and to camp there upon [the] water

< Fitowa 15 >