< Fitowa 15 >

1 Sa’an nan Musa da Isra’ilawa suka rera wannan waƙa ga Ubangiji suka ce, “Zan rera waƙa ga Ubangiji gama an ɗaukaka shi ƙwarai. Doki da mahayinsa ya jefa su cikin teku.
Then Moses and the Israelites sang this song to the Lord: “I will sing to the Lord, for he is supreme! He has thrown the horses and their riders into the sea.
2 “Ubangiji ne ƙarfina da mafakata, ya zama cetona. Shi Allahna ne, zan yabe shi. Allah na kakana, zan ɗaukaka shi.
The Lord gives me strength. He is the theme of my song. He saves me. He is my God, and I will praise him. He is my father's God, and I will honor him.
3 Ubangiji mai yaƙi ne Ubangiji ne sunansa.
The Lord is like a warrior. His name is the Lord.
4 Karusan Fir’auna da sojojinsa ya jefa cikin teku. Zaɓaɓɓun jarumawansa ya nutsar da su cikin Bahar Maliya.
He threw Pharaoh's chariots and his army into the sea. Pharaoh's best officers were drowned in the Red Sea.
5 Zurfafan ruwaye sun rufe su; suka nutse cikin zurfi kamar dutse.
The flooding water covered them. They dropped down into the depths like a stone.
6 Hannun damanka, ya Ubangiji, Mai kwarjini ne da iko, hannun damanka, ya Ubangiji, ya farfashe magabci.
Your power, Lord, is truly amazing! Your power, Lord, crushed the enemy.
7 “A cikin girman kwarjininka ka kā da waɗanda sun yi gāba da kai. Ka aiki fushinka mai zafi ya cinye su kamar tattaka.
By your majestic power you destroyed those who opposed you. Your anger blazed out and burned them up like stubble.
8 Da hucin numfashin hancinka ruwaye suka tattaru. Ruwaye masu kwararowa, suka tsaya kamar bango; ruwaye na zurfafa suka daskare a tsakiyar teku.
You blew and the sea piled up. The waves stood straight like a wall. The depths of the ocean turned solid.
9 Magabci ya yi fahariya, cewa ‘Zan fafare su, in ci musu. Zan raba ganima; abin da na so ya samu. Zan ja takobina hannuna kuwa zai hallaka su.’
The enemy bragged, ‘I will chase them and catch up with them. I will divide the plunder. I will eat them alive. I will swing my sword. By my hand I will destroy them.’
10 Amma ka hura numfashinka sai teku ya rufe su. Suka nutse kamar darma cikin manyan ruwaye.
But you blew with your breath and the sea swept over them. They sank down like lead in the swirling waters.
11 Wane ne cikin alloli, ya yi kamar ka, ya Ubangiji? Wane ne kamar ka, mai ɗaukaka cikin tsarki, mai banrazana cikin ɗaukaka, mai aikata al’ajabai?
Who is like you among the gods, Lord? Who is like you, glorious in holiness, awesome in wonder, doing miracles?
12 “Ka miƙa hannunka na dama, ƙasa ta haɗiye abokan gābanka.
You acted, and the earth swallowed the Egyptians.
13 A cikin ƙaunarka marar iyaka, za ka bishe mutanen da ka fansa. A cikin ƙarfinka, za ka bishe su zuwa mazauninka mai tsarki.
You led the people you saved with your trustworthy love. You will guide them in your strength to your holy home.
14 Al’ummai za su ji, su yi rawar jiki tsoro zai kama mutanen Filistiya.
The nations will hear what has happened and will shake with fear. The people who live in Philistia will experience agonizing distress.
15 Sarakunan Edom za su tsorata, shugabannin Mowab za su yi rawar jiki, mutanen Kan’ana za su narke.
The Edomite chiefs will be terrified. The Moabite leaders will tremble. The people living in Canaan will melt away in panic.
16 Razana da tsoro za su fāɗo a kansu. Da ikon hannunka za su tsaya cik kamar dutse, har sai mutanen da ka kawo sun wuce, ya Ubangiji.
Terror and fright will fall on them. Lord, because of your great power, they will be as still as stone until your people pass by, until the people you bought pass by.
17 Za ka kawo su, ka dasa su a kan dutsen nan naka inda, ya Ubangiji, ka shirya domin mazauninka, wuri mai tsarkin da hannuwanka suka kafa, ya Ubangiji.
You will take your people and plant them on the mountain that you own, the place that you, Lord, have prepared as your home, the sanctuary that your hands have built, Lord.
18 “Ubangiji zai yi mulki har abada abadin.”
The Lord will reign forever and ever!”
19 Sa’ad da dawakai, kekunan yaƙi da mahayan dawakan Fir’auna suka shiga cikin teku, Ubangiji ya mayar da ruwan teku a kansu, amma Isra’ilawa suka wuce a cikin teku a busasshiyar ƙasa.
When Pharaoh's horses, chariots, and horsemen went into the sea, the Lord brought the water rushing back over them. But the Israelites walked through the sea on dry ground.
20 Sa’an nan Miriyam annabiya,’yar’uwar Haruna ta ɗauki ganga a hannunta, dukan mata kuwa suka bi ta, da ganguna suna rawa.
Miriam the prophet, Aaron's sister, picked up a tambourine, and all the women followed her dancing and playing tambourines.
21 Miriyam ta yi musu waƙa. “Ku rera ga Ubangiji gama ya ci gawurtacciyar nasara. Doki da mahayi, ya jefa cikin teku.”
Miriam sang to them: “Sing to the Lord, for he is supreme! He has thrown the horses and their riders into the sea.”
22 Sai Musa ya jagoranci Isra’ila daga jan teku zuwa hamadar Shur. Kwana uku suka yi tafiya cikin hamada ba su sami ruwa ba.
Then Moses led Israel away from the Red Sea and into the Desert of Shur. For three days they walked in the desert but couldn't find any water.
23 Da suka zo Mara, ba su iya shan ruwan ba saboda yana da ɗaci (shi ya sa ake kira wurin Mara).
When they arrived at Marah, the water there was too bitter to drink. (That's why the place is called Marah.)
24 Sai mutanen suka yi gunaguni a kan Musa, suna cewa, “Me za mu sha?”
So the people complained to Moses, asking, “What are we going to drink?”
25 Sai Musa ya yi kuka ga Ubangiji, Ubangiji kuwa ya nuna masa wani itace. Sai ya jefa shi cikin ruwan, sai ruwan ya zama mai daɗi. A can Ubangiji ya yi musu doka da farilla, a can kuma ya gwada su.
Moses called out to the Lord for help, and the Lord showed him a piece of wood. When he threw it into the water, it became sweet. There the Lord gave them rules and instructions and also tested their loyalty to him.
26 Ya ce, “In kun kasa kunne ga muryar Ubangiji Allahnku kuka yi abin da yake daidai a idanunsa, in kun mai da hankali ga umarnansa, kuka kiyaye dukan farillansa, ba zan kawo muku wani ciwon da na kawo a kan Masarawa ba, gama ni ne Ubangiji da nake warkar da ku.”
He told them, “If you pay attention to what the Lord your God says, do what is right in his sight, obey his commands, and keep all his regulations, then I will not make you suffer from any of the diseases I gave the Egyptians because I am the Lord who heals you.”
27 Sai suka zo Elim inda akwai maɓulɓulan ruwa goma sha biyu da itatuwan dabino saba’in, suka sauka a can, kusa da ruwa.
Then they traveled on to Elim, which had twelve springs of water and seventy palm trees. They set up camp there beside the water.

< Fitowa 15 >