< Fitowa 14 >

1 Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa,
Gospod je spregovoril Mojzesu, rekoč:
2 “Ka faɗa wa Isra’ilawa, su juya su kafa sansani a Fi Hahirot, a tsakanin Migdol da teku. Za su kafa sansanin kai tsaye kusa da teku, wanda ya fuskanci Ba’al-Zafon.
»Govori Izraelovim otrokom, da se obrnejo in se utaborijo pred Pi Hahirótom, med Migdólom in morjem, nasproti Báal Cefónu. Pred njim se boste utaborili ob morju.
3 Fir’auna zai yi tsammani, ‘Aha, Isra’ilawa sun rikice cikin ƙasar, hamada kuwa ta yimƙe su.’
Kajti faraon bo o Izraelovih otrocih rekel: ›Zapletli so se v deželi, divjina jih je zaprla noter.‹
4 Zan kuma taurare zuciyar Fir’auna, zai kuwa bi su. Na shirya wannan domin in nuna ɗaukakata a bisa Fir’auna da ƙungiyar sojansa. Bayan wannan, mutanen Masar za su sani ni ne Ubangiji.” Sai Isra’ilawa suka yi haka.
Jaz pa bom zakrknil faraonovo srce, da bo sledil za njimi in počaščen bom na faraonu in na vsej njegovi vojski, da bodo Egipčani lahko spoznali, da jaz sem Gospod.« In tako so storili.
5 Sa’ad da aka faɗa wa Fir’auna cewa Isra’ilawa sun gudu, sai Fir’auna da bayinsa suka canja ra’ayinsu game da su, suka ce, “Me muka yi? Mun bar Isra’ilawa suka tafi, mun kuwa rasa hidimarsu!”
Egiptovskemu kralju je bilo povedano, da je ljudstvo zbežalo. In srce faraona in njegovih služabnikov je bilo obrnjeno zoper ljudstvo in rekli so: »Zakaj smo storili to, da smo pustili Izraela oditi od služenja nam?«
6 Sai shi da keken yaƙinsa suka shirya, ya kuma ɗauki sojojinsa tare da shi.
In pripravil je svoj bojni voz in s seboj vzel svoje ljudstvo.
7 Ya ɗauki kekunan yaƙi ɗari shida mafi kyau duka, tare da duk sauran keken yaƙin Masar, da shugabanni kuma a kan dukansu.
Vzel je šeststo izbranih bojnih voz in vse egiptovske bojne vozove in častnike nad vsakim izmed njih.
8 Ubangiji ya taurare zuciyar Fir’auna sarkin Masar, domin yă bi Isra’ilawa waɗanda suke tafiya ba tsoro.
Gospod je zakrknil srce faraonu, egiptovskemu kralju in ta je zasledoval Izraelove otroke. Izraelovi otroci pa so izšli z vzdignjeno roko.
9 Masarawa, dukan dawakan Fir’auna da kekunan yaƙi da mahaya da sojoji, suka bi Isra’ilawa suka cin musu yayinda suke a sansani kusa da teku kurkusa da Fi Hahirot, wanda ya fuskanci Ba’al-Zafon.
Toda Egipčani so jih zasledovali, vsi faraonovi konji in bojni vozovi in njegovi konjeniki in njegova vojska in jih dohiteli ob morju, utaborjene poleg Pi Hahiróta, pred Báal Cefónom.
10 Da Fir’auna ya yi kusa, Isra’ilawa suka ɗaga idanu sai suka hange Masarawa daga nesa suna tā da ƙura suna zuwa. Sai suka tsorata ƙwarai, suka kuwa yi kuka ga Ubangiji.
Ko se je faraon približal, so Izraelovi otroci povzdignili svoje oči in glej, Egipčani so korakali za njimi in bili so boleče prestrašeni in Izraelovi otroci so zavpili h Gospodu.
11 Suka ce wa Musa, “Don babu makabarta a Masar ne, ka kawo mu a hamada mu mutu? Me ka yi mana ke nan da ka fitar da mu daga Masar?
Mojzesu so rekli: »Ali si nas odpeljal proč, da umremo v divjini, ker ni bilo grobov v Egiptu? Zakaj si tako ravnal z nami, da si nas odvedel iz Egipta?
12 Ba mu faɗa maka a Masar ba, cewa ‘Ka bar mu mu bauta wa Masarawa’? Ai, da ya fi mana mu bauta wa Masarawa, da a ce mu mutu a hamada!”
Mar ni to beseda, ki smo ti jo povedali v Egiptu, rekoč: ›Pusti nas pri miru, da lahko služimo Egipčanom?‹ Kajti za nas bi bilo bolje, da služimo Egipčanom, kakor pa, da bi umrli v divjini.«
13 Musa ya amsa wa mutane ya ce, “Kada ku ji tsoro. Ku tsaya dai ku ga ceton da Ubangiji zai kawo muku yau. Masarawan da kuke gani yau, ba za ku ƙara ganinsu ba.
Mojzes je ljudstvu rekel: »Ne bojte se, mirno stojte in glejte Gospodovo rešitev duš, ki vam jo bo danes pokazal, kajti Egipčane, ki ste jih videli danes, jih na veke ne boste več videli.
14 Ubangiji zai yi yaƙi dominku, ku dai tsaya kurum.”
Gospod se bo boril za vas in vi boste ohranili svoj mir.«
15 Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa, “Don me kake mini kuka? Ka faɗa wa Isra’ilawa su ci gaba da tafiya.
Gospod je rekel Mojzesu: »Zakaj vpiješ k meni? Govori Izraelovim otrokom, da gredo naprej.
16 Ka ɗaga sandanka, ka miƙa shi bisa teku don ruwa yă rabu domin Isra’ilawa su wuce cikin teku a kan busasshiyar ƙasa.
Toda ti vzdigni svojo palico in iztegni svojo roko nad morje in ga razdeli in Izraelovi otroci bodo šli po suhih tleh skozi sredo morja.
17 Zan taurare zukatan Masarawa su shiga don su bi su. Ta haka zan ci nasara bisa Fir’auna da rundunansa, da keken yaƙinsa, da mahayan dawakansa.
Glej, zakrknil bom srca Egipčanom in oni jim bodo sledili in jaz si bom pridobil čast nad faraonom in nad vso njegovo vojsko, nad njegovimi bojnimi vozovi in nad njegovimi konjeniki.
18 Masarawa za su sani ni ne Ubangiji sa’ad da na sami nasara bisa kan Fir’auna, da keken yaƙinsa, da mahayan dawakansa.”
Egipčani bodo vedeli, da jaz sem Gospod, ko sem si pridobil čast nad faraonom, nad njegovimi bojnimi vozovi in nad njegovimi konjeniki.«
19 Sai mala’ikan Allah wanda yake tafiya a gaban sojojin Isra’ila, ya janye, ya koma bayansu. Al’amudin girgije shi ma ya koma, ya tsaya a bayansu,
Božji angel, ki je šel pred Izraelovim taborom, se je odstranil in odšel za njimi, in oblačni steber je odšel izpred njihovih obrazov in stal za njimi.
20 ya dawo tsakanin sojojin Masar da na Isra’ila. Duk dare, girgijen ya jawo duhu ga gefe ɗaya, haske kuma ga ɗaya gefen; saboda haka ba wanda ya kusaci wani duk dare.
Prišel je med tabor Egipčanov in tabor Izraela. Njim je bil oblak in tema, toda le-tem je dajal svetlobo ponoči, tako da vso noč eni niso prišli blizu k drugim.
21 Da Musa ya miƙa hannunsa a bisa teku, sai Ubangiji ya tura teku baya da iskar gabas mai ƙarfi duk dare, ya maishe shi busasshiyar ƙasa. Ruwa ya rabu,
Mojzes je svojo roko iztegnil nad morje in Gospod je storil, da je morje vso tisto noč šlo nazaj z močnim vzhodnikom in naredilo morje kopno zemljo in vode so bile razdeljene.
22 sai Isra’ilawa suka wuce cikin teku a kan busasshiyar ƙasa, ruwan ya zama musu katanga dama da hagu.
In Izraelovi otroci so šli v sredo morja po suhih tleh in vode so jim bile zid na njihovi desnici in na njihovi levici.
23 Masarawa suka bi su da dukan dawakan Fir’auna, da kekunan yaƙi, da mahayan, suka bi su cikin teku.
Egipčani pa so jih zasledovali in šli noter za njimi v sredo morja, celo vsi faraonovi konji, njegovi bojni vozovi in njegovi konjeniki.
24 Da asubahin fāri, sai Ubangiji ya dubi ƙasa a kan sojojin Masarawa daga al’amudin wuta da kuma girgije, sai ya sa suka ruɗe.
Pripetilo se je, da je ob jutranji straži Gospod skozi ognjen in oblačen steber pogledal na vojsko Egipčanov in prizadel vojsko Egipčanov.
25 Ya sa ƙafafun keken yaƙinsu suka fita don su kāsa tuƙi. Sai Masarawa suka ce, “Bari mu gudu daga Isra’ilawa gama Ubangiji yana yaƙi dominsu gāba da Masar.”
Snemal je kolesa njihovim bojnim vozovom, da so jih težko vozili. Tako da so Egipčani rekli: »Zbežimo pred obličjem Izraela, kajti Gospod se bori zanje zoper Egipčane.«
26 Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa, “Miƙa hannunka bisa teku don ruwa yă koma kan Masarawa, da keken yaƙinsu, da kuma mahayansu.”
Gospod je rekel Mojzesu: »Svojo roko iztegni nad morje, da lahko vode ponovno pridejo nad Egipčane, nad njihove bojne vozove in nad njihove konjenike.«
27 Musa ya miƙa hannunsa a bisa tekun, da wayewar gari kuwa teku ya koma wurinsa na dā. Masarawa suka yi ƙoƙari su gudu, sai Ubangiji ya tura su cikin teku.
Mojzes je svojo roko iztegnil nad morje in ko se je prikazalo jutro, se je morje vrnilo k svoji moči in Egipčani so bežali proti le-temu; in Gospod je Egipčane porazil v sredi morja.
28 Ruwan ya komo ya rufe keken yaƙin da mahayan, dukan sojojin Fir’aunan da suka bi bayan Isra’ilawa cikin teku, ba ko ɗaya da ya tsira.
Vode so se vrnile in pokrile bojne vozove, konjenike in vso faraonovo vojsko, ki je za njimi prišla v morje. Tam ni ostal niti eden izmed njih.
29 Amma Isra’ilawa suka wuce cikin teku a busasshiyar ƙasa, ruwa kuwa ya yi musu katanga dama da hagu.
Toda Izraelovi otroci so hodili po suhi zemlji v sredi morja. Vode so jim bile zid na njihovi desnici in na njihovi levici.
30 A rana nan Ubangiji ya cece Isra’ila daga hannuwan Masarawa, Isra’ilawa kuwa suka ga gawawwakin Masarawa a bakin teku.
Tako je Gospod tega dne rešil Izraela iz roke Egipčanov, in Izrael je videl Egipčane mrtve na morski obali.
31 Sa’ad da Isra’ilawa suka ga iko mai girma da Ubangiji ya yi gāba da Masarawa, sai mutanen suka ji tsoron Ubangiji, suka amince da shi, da kuma bawansa Musa.
Izrael je videl to veliko delo, ki ga je Gospod storil na Egipčanih, in ljudstvo se je balo Gospoda in verjelo Gospodu in njegovemu služabniku Mojzesu.

< Fitowa 14 >