< Fitowa 14 >

1 Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa,
Or le Seigneur parla à Moïse, disant:
2 “Ka faɗa wa Isra’ilawa, su juya su kafa sansani a Fi Hahirot, a tsakanin Migdol da teku. Za su kafa sansanin kai tsaye kusa da teku, wanda ya fuskanci Ba’al-Zafon.
Dis aux enfants d’Israël qu’ils retournent, et qu’ils campent vis-à-vis de Phihahiroth, qui est entre Magdalum et la mer, contre Béelséphon: c’est la vue de ce lieu que vous poserez votre camp, près de la mer.
3 Fir’auna zai yi tsammani, ‘Aha, Isra’ilawa sun rikice cikin ƙasar, hamada kuwa ta yimƙe su.’
Car Pharaon va dire des enfants d’Israël: Ils sont resserrés dans la terre, le désert les tient enfermés.
4 Zan kuma taurare zuciyar Fir’auna, zai kuwa bi su. Na shirya wannan domin in nuna ɗaukakata a bisa Fir’auna da ƙungiyar sojansa. Bayan wannan, mutanen Masar za su sani ni ne Ubangiji.” Sai Isra’ilawa suka yi haka.
Et j’endurcirai son cœur, et il les poursuivra; et je serai glorifié en Pharaon et en toute son armée; et les Egyptiens sauront que je suis le Seigneur. Et les enfants d’Israël firent ainsi.
5 Sa’ad da aka faɗa wa Fir’auna cewa Isra’ilawa sun gudu, sai Fir’auna da bayinsa suka canja ra’ayinsu game da su, suka ce, “Me muka yi? Mun bar Isra’ilawa suka tafi, mun kuwa rasa hidimarsu!”
Cependant on annonça au roi des Egyptiens que le peuple s’était enfui, et le cœur de Pharaon et de ses serviteurs fut changé à l’égard du peuple; et ils dirent: Qu’avons-nous voulu faire en laissant aller Israël, pour qu’il ne nous servît plus?
6 Sai shi da keken yaƙinsa suka shirya, ya kuma ɗauki sojojinsa tare da shi.
Il attela donc son char, et prit tout son peuple avec lui.
7 Ya ɗauki kekunan yaƙi ɗari shida mafi kyau duka, tare da duk sauran keken yaƙin Masar, da shugabanni kuma a kan dukansu.
Il emmena aussi, outre six cents chars d’élite, tout ce qu’il y eut de chars dans l’Egypte, et les chefs de toute l’armée.
8 Ubangiji ya taurare zuciyar Fir’auna sarkin Masar, domin yă bi Isra’ilawa waɗanda suke tafiya ba tsoro.
Et le Seigneur endurcit le cœur de Pharaon, roi d’Egypte, et il poursuivit les enfants d’Israël; mais eux étaient sortis par une main élevée.
9 Masarawa, dukan dawakan Fir’auna da kekunan yaƙi da mahaya da sojoji, suka bi Isra’ilawa suka cin musu yayinda suke a sansani kusa da teku kurkusa da Fi Hahirot, wanda ya fuskanci Ba’al-Zafon.
Et comme les Egyptiens suivaient leurs traces de près, ils les trouvèrent dans leur camp près de la mer: toute la cavalerie et les chars de Pharaon et l’armée entière étaient à Phihahiroth contre Béelséphon.
10 Da Fir’auna ya yi kusa, Isra’ilawa suka ɗaga idanu sai suka hange Masarawa daga nesa suna tā da ƙura suna zuwa. Sai suka tsorata ƙwarai, suka kuwa yi kuka ga Ubangiji.
Et quand Pharaon se fut approché, les enfants d’Israël, levant les yeux, virent les Egyptiens derrière eux, et ils furent saisis d’une grande crainte, et ils crièrent au Seigneur,
11 Suka ce wa Musa, “Don babu makabarta a Masar ne, ka kawo mu a hamada mu mutu? Me ka yi mana ke nan da ka fitar da mu daga Masar?
Et ils dirent à Moïse: Peut-être qu’il n’y avait pas de sépultures en Egypte; c’est pour cela que tu nous a amenés, afin que nous mourions dans le désert: qu’as-tu voulu faire en nous retirant de la terre d’Egypte?
12 Ba mu faɗa maka a Masar ba, cewa ‘Ka bar mu mu bauta wa Masarawa’? Ai, da ya fi mana mu bauta wa Masarawa, da a ce mu mutu a hamada!”
N’est-ce pas là le langage que nous te tenions en Egypte, disant: Retire-toi de nous, afin que nous servions les Egyptiens? car il valait beaucoup mieux les servir que mourir dans le désert.
13 Musa ya amsa wa mutane ya ce, “Kada ku ji tsoro. Ku tsaya dai ku ga ceton da Ubangiji zai kawo muku yau. Masarawan da kuke gani yau, ba za ku ƙara ganinsu ba.
Or Moïse répondit au peuple: Ne craignez point, demeurez fermes, et voyez les grandes œuvres que le Seigneur va faire aujourd’hui; car les Egyptiens que vous voyez en ce moment, vous ne les verrez plus jamais.
14 Ubangiji zai yi yaƙi dominku, ku dai tsaya kurum.”
Le Seigneur combattra pour vous, et vous serez dans le silence.
15 Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa, “Don me kake mini kuka? Ka faɗa wa Isra’ilawa su ci gaba da tafiya.
Le Seigneur dit ensuite à Moïse: Pourquoi cries-tu vers moi? Dis aux enfants d’Israël qu’ils partent.
16 Ka ɗaga sandanka, ka miƙa shi bisa teku don ruwa yă rabu domin Isra’ilawa su wuce cikin teku a kan busasshiyar ƙasa.
Mais toi, élève ta verge, et étends ta main sur la mer, et divise-la, afin que les enfants d’Israël marchent au milieu de la mer à sec.
17 Zan taurare zukatan Masarawa su shiga don su bi su. Ta haka zan ci nasara bisa Fir’auna da rundunansa, da keken yaƙinsa, da mahayan dawakansa.
Pour moi, j’endurcirai le cœur des Egyptiens, afin qu’ils vous poursuivent, et je serai glorifié en Pharaon, et en toute son armée, et en ses chars et en ses cavaliers
18 Masarawa za su sani ni ne Ubangiji sa’ad da na sami nasara bisa kan Fir’auna, da keken yaƙinsa, da mahayan dawakansa.”
Et les Egyptiens sauront que moi, je suis le Seigneur, quand j’aurai été glorifié en Pharaon, et en ses chars et en ses cavaliers.
19 Sai mala’ikan Allah wanda yake tafiya a gaban sojojin Isra’ila, ya janye, ya koma bayansu. Al’amudin girgije shi ma ya koma, ya tsaya a bayansu,
Alors l’ange de Dieu qui précédait le camp d’Israël, alla derrière eux; et ainsi que lui, la colonne de nuée, passant de devant en arrière,
20 ya dawo tsakanin sojojin Masar da na Isra’ila. Duk dare, girgijen ya jawo duhu ga gefe ɗaya, haske kuma ga ɗaya gefen; saboda haka ba wanda ya kusaci wani duk dare.
Se tint entre le camp des Egyptiens et le camp d’Israël; or la nuée était ténébreuse, et elle éclairait la nuit; en sorte que durant tout le temps de la nuit, ils ne pouvaient s’approcher l’un de l’autre.
21 Da Musa ya miƙa hannunsa a bisa teku, sai Ubangiji ya tura teku baya da iskar gabas mai ƙarfi duk dare, ya maishe shi busasshiyar ƙasa. Ruwa ya rabu,
Lors donc que Moïse eut étendu la main sur la mer, le Seigneur la fit retirer, un vent impétueux et brûlant ayant soufflé toute la nuit, et il la mit à sec, et l’eau fut divisée.
22 sai Isra’ilawa suka wuce cikin teku a kan busasshiyar ƙasa, ruwan ya zama musu katanga dama da hagu.
Ainsi les enfants d’Israël entrèrent au milieu de la mer desséchée; car l’eau était comme un mur à leur droite et à leur gauche.
23 Masarawa suka bi su da dukan dawakan Fir’auna, da kekunan yaƙi, da mahayan, suka bi su cikin teku.
Et les poursuivant, les Egyptiens entrèrent après eux au milieu de la mer, ainsi que toute la cavalerie de Pharaon, ses chars et ses cavaliers.
24 Da asubahin fāri, sai Ubangiji ya dubi ƙasa a kan sojojin Masarawa daga al’amudin wuta da kuma girgije, sai ya sa suka ruɗe.
Et déjà était venue la veille du matin, et voilà que le Seigneur jetant un regard sur le camp des Égyptiens à travers la colonne de feu et de nuée, tua toute leur armée,
25 Ya sa ƙafafun keken yaƙinsu suka fita don su kāsa tuƙi. Sai Masarawa suka ce, “Bari mu gudu daga Isra’ilawa gama Ubangiji yana yaƙi dominsu gāba da Masar.”
Et renversa les roues des chars, ils furent entraînés au profond de la mer. Les Égyptiens dirent donc: Fuyons Israël, car le Seigneur combat pour eux contre nous.
26 Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa, “Miƙa hannunka bisa teku don ruwa yă koma kan Masarawa, da keken yaƙinsu, da kuma mahayansu.”
Et le Seigneur dit à Moïse: Étends ta main sur la mer, afin que les eaux retournent vers les Égyptiens, sur leurs chars et leurs cavaliers.
27 Musa ya miƙa hannunsa a bisa tekun, da wayewar gari kuwa teku ya koma wurinsa na dā. Masarawa suka yi ƙoƙari su gudu, sai Ubangiji ya tura su cikin teku.
Et lorsque Moïse eut étendu sa main contre la mer, elle retourna au premier point du jour en son premier lieu; et les eaux vinrent à la rencontre des Égyptiens qui s’enfuyaient, et le Seigneur les enveloppa au milieu des flots.
28 Ruwan ya komo ya rufe keken yaƙin da mahayan, dukan sojojin Fir’aunan da suka bi bayan Isra’ilawa cikin teku, ba ko ɗaya da ya tsira.
Ainsi les eaux retournèrent et couvrirent les chars et les cavaliers de toute l’armée de Pharaon, qui poursuivant Israël, étaient entrés dans la mer: et il ne resta pas même un seul d’entre eux.
29 Amma Isra’ilawa suka wuce cikin teku a busasshiyar ƙasa, ruwa kuwa ya yi musu katanga dama da hagu.
Mais les enfants d’Israël poursuivirent leur chemin au milieu de la mer desséchée, et les eaux étaient pour eux comme un mur à droite et à gauche:
30 A rana nan Ubangiji ya cece Isra’ila daga hannuwan Masarawa, Isra’ilawa kuwa suka ga gawawwakin Masarawa a bakin teku.
Et le Seigneur délivra en ce jour-là Israël de la main des Egyptiens.
31 Sa’ad da Isra’ilawa suka ga iko mai girma da Ubangiji ya yi gāba da Masarawa, sai mutanen suka ji tsoron Ubangiji, suka amince da shi, da kuma bawansa Musa.
Et ils virent les Égyptiens morts sur le rivage de la mer, et la main puissante qu’avait étendue le Seigneur contre eux: et le peuple craignit le Seigneur, et ils crurent au Seigneur et à Moïse son serviteur.

< Fitowa 14 >