< Fitowa 14 >

1 Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa,
Le Seigneur dit ensuite à Moïse:
2 “Ka faɗa wa Isra’ilawa, su juya su kafa sansani a Fi Hahirot, a tsakanin Migdol da teku. Za su kafa sansanin kai tsaye kusa da teku, wanda ya fuskanci Ba’al-Zafon.
Parle aux fils d'Israël, qu'ils se détournent, qu'ils transportent leurs tentes à l'opposite du campement actuel, entre Magdol et la mer, en face de Béelséphon; tu les feras camper là, près de la mer.
3 Fir’auna zai yi tsammani, ‘Aha, Isra’ilawa sun rikice cikin ƙasar, hamada kuwa ta yimƙe su.’
Et le Pharaon dira à son peuple: Les fils d'Israël sont errants dans la contrée, et pris par le désert.
4 Zan kuma taurare zuciyar Fir’auna, zai kuwa bi su. Na shirya wannan domin in nuna ɗaukakata a bisa Fir’auna da ƙungiyar sojansa. Bayan wannan, mutanen Masar za su sani ni ne Ubangiji.” Sai Isra’ilawa suka yi haka.
Mais, moi j'endurcirai le cœur du Pharaon; il vous poursuivra, et je serai glorifié en lui et en toute son armée; et tous les fils des Égyptiens sauront que je suis le Seigneur. C'est, en effet, ainsi qu'ils firent.
5 Sa’ad da aka faɗa wa Fir’auna cewa Isra’ilawa sun gudu, sai Fir’auna da bayinsa suka canja ra’ayinsu game da su, suka ce, “Me muka yi? Mun bar Isra’ilawa suka tafi, mun kuwa rasa hidimarsu!”
On annonça au roi des Égyptiens que le peuple avait fui; et le cœur du Pharaon et celui de ses serviteurs se tournèrent contre le peuple, et ils dirent: Qu'avons-nous fait? pourquoi avons-nous congédié les fils d'Israël, de sorte qu'ils ne nous serviront plus?
6 Sai shi da keken yaƙinsa suka shirya, ya kuma ɗauki sojojinsa tare da shi.
Le Pharaon attela donc ses chars, et il emmena avec lui tout son peuple.
7 Ya ɗauki kekunan yaƙi ɗari shida mafi kyau duka, tare da duk sauran keken yaƙin Masar, da shugabanni kuma a kan dukansu.
Il prit six cents chars d'élite, avec toute la cavalerie des Égyptiens, et tous les grands du royaume.
8 Ubangiji ya taurare zuciyar Fir’auna sarkin Masar, domin yă bi Isra’ilawa waɗanda suke tafiya ba tsoro.
Et le Seigneur endurcit le cœur du Pharaon, roi d’Égypte, ainsi que celui de ses serviteurs; le Pharaon poursuivit les fils d'Israël; mais, dans leur marche, les fils d'Israël étaient conduits par une puissante main.
9 Masarawa, dukan dawakan Fir’auna da kekunan yaƙi da mahaya da sojoji, suka bi Isra’ilawa suka cin musu yayinda suke a sansani kusa da teku kurkusa da Fi Hahirot, wanda ya fuskanci Ba’al-Zafon.
Les Égyptiens, les ayant poursuivis, les trouvèrent campés près de la mer. Tous les chevaux, tous les chars du Pharaon, sa cavalerie et son armée se déployèrent, contre le camp, en face de Béelséphon.
10 Da Fir’auna ya yi kusa, Isra’ilawa suka ɗaga idanu sai suka hange Masarawa daga nesa suna tā da ƙura suna zuwa. Sai suka tsorata ƙwarai, suka kuwa yi kuka ga Ubangiji.
Le Pharaon s'approcha; et les fils d'Israël, ayant levé les yeux, virent les Égyptiens campés derrière eux, et ils eurent grande crainte. Les fils d'Israël invoquèrent le Seigneur.
11 Suka ce wa Musa, “Don babu makabarta a Masar ne, ka kawo mu a hamada mu mutu? Me ka yi mana ke nan da ka fitar da mu daga Masar?
Et ils dirent à Moïse: C'est parce que nous n'avions pas de tombeaux en Égypte, que tu nous as amenés pour mourir dans le désert. Pourquoi nous as-tu fait cela en nous tirant de l'Égypte?
12 Ba mu faɗa maka a Masar ba, cewa ‘Ka bar mu mu bauta wa Masarawa’? Ai, da ya fi mana mu bauta wa Masarawa, da a ce mu mutu a hamada!”
N'est-ce point là ce que nous te disions en Égypte: Laisse-nous servir les Égyptiens; mieux vaut pour nous les servir que d'aller périr dans le désert.
13 Musa ya amsa wa mutane ya ce, “Kada ku ji tsoro. Ku tsaya dai ku ga ceton da Ubangiji zai kawo muku yau. Masarawan da kuke gani yau, ba za ku ƙara ganinsu ba.
Rassurez-vous, répondit Moïse au peuple, faites halte, et soyez attentifs au salut que le Seigneur va vous envoyer aujourd'hui même. Ces Égyptiens que vous apercevez en ce moment, vous ne les verrez plus à jamais.
14 Ubangiji zai yi yaƙi dominku, ku dai tsaya kurum.”
Le Seigneur combattra pour vous, pendant que vous resterez tranquilles.
15 Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa, “Don me kake mini kuka? Ka faɗa wa Isra’ilawa su ci gaba da tafiya.
Et le Seigneur dit à Moïse: Que cries-tu vers moi? Parle aux fils d'Israël, et qu'ils lèvent leur camp.
16 Ka ɗaga sandanka, ka miƙa shi bisa teku don ruwa yă rabu domin Isra’ilawa su wuce cikin teku a kan busasshiyar ƙasa.
Pour toi, prends ta baguette: étends la main sur la mer, ouvre ses flots; les fils d'Israël entreront au milieu de la mer comme sur un sol affermi.
17 Zan taurare zukatan Masarawa su shiga don su bi su. Ta haka zan ci nasara bisa Fir’auna da rundunansa, da keken yaƙinsa, da mahayan dawakansa.
Et j'endurcirai le cœur du Pharaon et de tous les Égyptiens; ils y entreront après vous, et je serai glorifié en ce Pharaon, en son armée entière, en ses chars et en sa cavalerie.
18 Masarawa za su sani ni ne Ubangiji sa’ad da na sami nasara bisa kan Fir’auna, da keken yaƙinsa, da mahayan dawakansa.”
Et tous les Égyptiens connaîtront que je suis le Seigneur, lorsque je me serai glorifié en ce Pharaon, en ses chars et en ses chevaux.
19 Sai mala’ikan Allah wanda yake tafiya a gaban sojojin Isra’ila, ya janye, ya koma bayansu. Al’amudin girgije shi ma ya koma, ya tsaya a bayansu,
Cependant, l'ange du Seigneur qui précédait les fils d'Israël, changea de place et passa derrière eux; la colonne de nuée, quittant leur front, se posa derrière eux.
20 ya dawo tsakanin sojojin Masar da na Isra’ila. Duk dare, girgijen ya jawo duhu ga gefe ɗaya, haske kuma ga ɗaya gefen; saboda haka ba wanda ya kusaci wani duk dare.
Elle se mit entre le camp des Égyptiens et le camp des fils d'Israël, et s'y tint; il y eut obscurité et ténèbres; les deux camps étaient séparés par la nuit, et, durant toute la nuit, ils ne se rejoignirent point.
21 Da Musa ya miƙa hannunsa a bisa teku, sai Ubangiji ya tura teku baya da iskar gabas mai ƙarfi duk dare, ya maishe shi busasshiyar ƙasa. Ruwa ya rabu,
Alors, Moïse étendit la main sur la mer, et le Seigneur, durant toute la nuit, fit souffler un vent violent sur la mer: les flots s'ouvrirent ' et la mer fut à sec.
22 sai Isra’ilawa suka wuce cikin teku a kan busasshiyar ƙasa, ruwan ya zama musu katanga dama da hagu.
Et les fils d'Israël entrèrent au milieu de la mer comme sur un sol affermi; les eaux formaient un, mur à droite et un mur à gauche.
23 Masarawa suka bi su da dukan dawakan Fir’auna, da kekunan yaƙi, da mahayan, suka bi su cikin teku.
Les Égyptiens les poursuivirent; toute la cavalerie du Pharaon, les chars et les écuyers entrèrent à leur suite au milieu des flots.
24 Da asubahin fāri, sai Ubangiji ya dubi ƙasa a kan sojojin Masarawa daga al’amudin wuta da kuma girgije, sai ya sa suka ruɗe.
La veille du matin arrivée, le Seigneur abaissa ses regards sur l'armée des Égyptiens, du milieu de la colonne de nuée et de feu, et il confondit l'armée des Égyptiens.
25 Ya sa ƙafafun keken yaƙinsu suka fita don su kāsa tuƙi. Sai Masarawa suka ce, “Bari mu gudu daga Isra’ilawa gama Ubangiji yana yaƙi dominsu gāba da Masar.”
Il embarrassa les essieux de leurs chars, il les poussa violemment; et les Égyptiens se dirent: Fuyons loin de la face d'Israël, car le Seigneur combat pour eux contre nous.
26 Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa, “Miƙa hannunka bisa teku don ruwa yă koma kan Masarawa, da keken yaƙinsu, da kuma mahayansu.”
Mais le Seigneur dit à Moïse: Étends la main sur la mer, que l'eau reprenne son cours, qu'elle couvre les Égyptiens, les chars et les écuyers.
27 Musa ya miƙa hannunsa a bisa tekun, da wayewar gari kuwa teku ya koma wurinsa na dā. Masarawa suka yi ƙoƙari su gudu, sai Ubangiji ya tura su cikin teku.
Et Moïse étendit la main sur la mer; comme le jour paraissait, l'eau commença à reprendre sa place, et les Égyptiens s'enfuyaient devant les eaux, et le Seigneur confondit les Égyptiens au milieu de la mer.
28 Ruwan ya komo ya rufe keken yaƙin da mahayan, dukan sojojin Fir’aunan da suka bi bayan Isra’ilawa cikin teku, ba ko ɗaya da ya tsira.
L'eau, qui reprenait sa place, couvrait les chars, et les écuyers, et toute l'armée du Pharaon: de tous ceux qui, derrière Israël, étaient entrés dans la mer, il n'en échappa pas un seul.
29 Amma Isra’ilawa suka wuce cikin teku a busasshiyar ƙasa, ruwa kuwa ya yi musu katanga dama da hagu.
Cependant, les fils d'Israël avaient marché à pied sec au fond de la nier, l'eau fortifiant pour eux un mur à droite et un mur à gauche.
30 A rana nan Ubangiji ya cece Isra’ila daga hannuwan Masarawa, Isra’ilawa kuwa suka ga gawawwakin Masarawa a bakin teku.
En ce jour-là, le Seigneur sauva Israël des mains des Égyptiens; et Israël vit les cadavres des Égyptiens sur les bords de la mer.
31 Sa’ad da Isra’ilawa suka ga iko mai girma da Ubangiji ya yi gāba da Masarawa, sai mutanen suka ji tsoron Ubangiji, suka amince da shi, da kuma bawansa Musa.
Alors, Israël vit la grande main du Seigneur; il vit comme elle avait frappé les Égyptiens; et le peuple eut crainte du Seigneur; il crut en Dieu et en son serviteur Moïse.

< Fitowa 14 >