< Fitowa 14 >
1 Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa,
Yahvé parla à Moïse, et dit:
2 “Ka faɗa wa Isra’ilawa, su juya su kafa sansani a Fi Hahirot, a tsakanin Migdol da teku. Za su kafa sansanin kai tsaye kusa da teku, wanda ya fuskanci Ba’al-Zafon.
Parle aux enfants d'Israël, pour qu'ils fassent demi-tour et campent devant Pihahiroth, entre Migdol et la mer, devant Baal Zephon. Vous camperez en face d'elle, près de la mer.
3 Fir’auna zai yi tsammani, ‘Aha, Isra’ilawa sun rikice cikin ƙasar, hamada kuwa ta yimƙe su.’
Pharaon dira des enfants d'Israël: « Ils sont empêtrés dans le pays. Le désert les a enfermés.
4 Zan kuma taurare zuciyar Fir’auna, zai kuwa bi su. Na shirya wannan domin in nuna ɗaukakata a bisa Fir’auna da ƙungiyar sojansa. Bayan wannan, mutanen Masar za su sani ni ne Ubangiji.” Sai Isra’ilawa suka yi haka.
J'endurcirai le cœur de Pharaon, et il les suivra; je m'assurerai la gloire sur Pharaon et sur toutes ses armées, et les Égyptiens sauront que je suis Yahvé. » C'est ce qu'ils firent.
5 Sa’ad da aka faɗa wa Fir’auna cewa Isra’ilawa sun gudu, sai Fir’auna da bayinsa suka canja ra’ayinsu game da su, suka ce, “Me muka yi? Mun bar Isra’ilawa suka tafi, mun kuwa rasa hidimarsu!”
On apprit au roi d'Égypte que le peuple s'était enfui; le cœur de Pharaon et de ses serviteurs fut changé à l'égard du peuple, et ils dirent: « Qu'avons-nous donc fait, pour laisser Israël s'enfuir loin de nous? »
6 Sai shi da keken yaƙinsa suka shirya, ya kuma ɗauki sojojinsa tare da shi.
Il prépara son char et prit avec lui son armée;
7 Ya ɗauki kekunan yaƙi ɗari shida mafi kyau duka, tare da duk sauran keken yaƙin Masar, da shugabanni kuma a kan dukansu.
il prit six cents chars d'élite et tous les chars d'Égypte, avec des chefs sur chacun d'eux.
8 Ubangiji ya taurare zuciyar Fir’auna sarkin Masar, domin yă bi Isra’ilawa waɗanda suke tafiya ba tsoro.
Yahvé endurcit le cœur de Pharaon, roi d'Égypte, et il poursuivit les enfants d'Israël, car les enfants d'Israël sortaient avec une main levée.
9 Masarawa, dukan dawakan Fir’auna da kekunan yaƙi da mahaya da sojoji, suka bi Isra’ilawa suka cin musu yayinda suke a sansani kusa da teku kurkusa da Fi Hahirot, wanda ya fuskanci Ba’al-Zafon.
Les Égyptiens les poursuivirent. Tous les chevaux et les chars de Pharaon, ses cavaliers et son armée les rattrapèrent en campant près de la mer, à côté de Pihahiroth, devant Baal Zephon.
10 Da Fir’auna ya yi kusa, Isra’ilawa suka ɗaga idanu sai suka hange Masarawa daga nesa suna tā da ƙura suna zuwa. Sai suka tsorata ƙwarai, suka kuwa yi kuka ga Ubangiji.
Lorsque Pharaon s'approcha, les enfants d'Israël levèrent les yeux, et voici que les Égyptiens marchaient à leur poursuite; ils eurent très peur. Les enfants d'Israël crièrent à Yahvé.
11 Suka ce wa Musa, “Don babu makabarta a Masar ne, ka kawo mu a hamada mu mutu? Me ka yi mana ke nan da ka fitar da mu daga Masar?
Ils dirent à Moïse: « Parce qu'il n'y avait pas de tombeaux en Égypte, nous as-tu emmenés mourir dans le désert? Pourquoi nous as-tu traités de la sorte, pour nous faire sortir d'Égypte?
12 Ba mu faɗa maka a Masar ba, cewa ‘Ka bar mu mu bauta wa Masarawa’? Ai, da ya fi mana mu bauta wa Masarawa, da a ce mu mutu a hamada!”
N'est-ce pas là la parole que nous t'avons adressée en Égypte, en te disant: « Laisse-nous tranquilles, pour que nous servions les Égyptiens »? Car il aurait mieux valu pour nous servir les Égyptiens que de mourir dans le désert. »
13 Musa ya amsa wa mutane ya ce, “Kada ku ji tsoro. Ku tsaya dai ku ga ceton da Ubangiji zai kawo muku yau. Masarawan da kuke gani yau, ba za ku ƙara ganinsu ba.
Moïse dit au peuple: « N'ayez pas peur. Restez immobiles et voyez le salut de l'Éternel, qu'il va opérer pour vous aujourd'hui, car vous ne verrez plus jamais les Égyptiens que vous avez vus aujourd'hui.
14 Ubangiji zai yi yaƙi dominku, ku dai tsaya kurum.”
L'Éternel combattra pour vous, et vous resterez tranquilles. »
15 Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa, “Don me kake mini kuka? Ka faɗa wa Isra’ilawa su ci gaba da tafiya.
Yahvé dit à Moïse: « Pourquoi cries-tu vers moi? Parle aux enfants d'Israël, pour qu'ils avancent.
16 Ka ɗaga sandanka, ka miƙa shi bisa teku don ruwa yă rabu domin Isra’ilawa su wuce cikin teku a kan busasshiyar ƙasa.
Lève ta verge, étends ta main sur la mer et divise-la. Les enfants d'Israël entreront à sec au milieu de la mer.
17 Zan taurare zukatan Masarawa su shiga don su bi su. Ta haka zan ci nasara bisa Fir’auna da rundunansa, da keken yaƙinsa, da mahayan dawakansa.
Voici, je vais moi-même endurcir le cœur des Égyptiens, et ils entreront après eux. Je me rendrai maître de Pharaon et de toutes ses armées, de ses chars et de ses cavaliers.
18 Masarawa za su sani ni ne Ubangiji sa’ad da na sami nasara bisa kan Fir’auna, da keken yaƙinsa, da mahayan dawakansa.”
Les Égyptiens sauront que je suis Yahvé, quand je me serai acquis la gloire sur Pharaon, sur ses chars et sur ses cavaliers. »
19 Sai mala’ikan Allah wanda yake tafiya a gaban sojojin Isra’ila, ya janye, ya koma bayansu. Al’amudin girgije shi ma ya koma, ya tsaya a bayansu,
L'ange de Dieu, qui marchait devant le camp d'Israël, se déplaça et alla derrière eux; et la colonne de nuée se déplaça de devant eux, et se tint derrière eux.
20 ya dawo tsakanin sojojin Masar da na Isra’ila. Duk dare, girgijen ya jawo duhu ga gefe ɗaya, haske kuma ga ɗaya gefen; saboda haka ba wanda ya kusaci wani duk dare.
Elle se plaça entre le camp d'Égypte et le camp d'Israël. Il y avait la nuée et les ténèbres, et pourtant elle donnait de la lumière pendant la nuit. L'un ne s'approchait pas de l'autre de toute la nuit.
21 Da Musa ya miƙa hannunsa a bisa teku, sai Ubangiji ya tura teku baya da iskar gabas mai ƙarfi duk dare, ya maishe shi busasshiyar ƙasa. Ruwa ya rabu,
Moïse étendit sa main sur la mer, et Yahvé fit reculer la mer par un fort vent d'est toute la nuit; il mit la mer à sec, et les eaux se partagèrent.
22 sai Isra’ilawa suka wuce cikin teku a kan busasshiyar ƙasa, ruwan ya zama musu katanga dama da hagu.
Les enfants d'Israël entrèrent au milieu de la mer à sec, et les eaux formaient pour eux une muraille à droite et à gauche.
23 Masarawa suka bi su da dukan dawakan Fir’auna, da kekunan yaƙi, da mahayan, suka bi su cikin teku.
Les Égyptiens les poursuivirent et entrèrent après eux au milieu de la mer: tous les chevaux de Pharaon, ses chars et ses cavaliers.
24 Da asubahin fāri, sai Ubangiji ya dubi ƙasa a kan sojojin Masarawa daga al’amudin wuta da kuma girgije, sai ya sa suka ruɗe.
A la veille du matin, Yahvé regarda l'armée égyptienne à travers la colonne de feu et de nuée, et il confondit l'armée égyptienne.
25 Ya sa ƙafafun keken yaƙinsu suka fita don su kāsa tuƙi. Sai Masarawa suka ce, “Bari mu gudu daga Isra’ilawa gama Ubangiji yana yaƙi dominsu gāba da Masar.”
Il enleva les roues de leurs chars et les fit rouler lourdement, si bien que les Égyptiens dirent: « Fuyons devant Israël, car Yahvé combat pour eux contre les Égyptiens! ».
26 Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa, “Miƙa hannunka bisa teku don ruwa yă koma kan Masarawa, da keken yaƙinsu, da kuma mahayansu.”
Yahvé dit à Moïse: « Étends ta main sur la mer, afin que les eaux reviennent sur les Égyptiens, sur leurs chars et sur leurs cavaliers. »
27 Musa ya miƙa hannunsa a bisa tekun, da wayewar gari kuwa teku ya koma wurinsa na dā. Masarawa suka yi ƙoƙari su gudu, sai Ubangiji ya tura su cikin teku.
Moïse étendit sa main sur la mer, et la mer reprit sa force à l'apparition du matin; les Égyptiens s'enfuirent devant elle. Yahvé renversa les Égyptiens au milieu de la mer.
28 Ruwan ya komo ya rufe keken yaƙin da mahayan, dukan sojojin Fir’aunan da suka bi bayan Isra’ilawa cikin teku, ba ko ɗaya da ya tsira.
Les eaux revinrent et couvrirent les chars et les cavaliers, toute l'armée de Pharaon qui entra après eux dans la mer. Il n'en resta pas un seul.
29 Amma Isra’ilawa suka wuce cikin teku a busasshiyar ƙasa, ruwa kuwa ya yi musu katanga dama da hagu.
Mais les enfants d'Israël marchaient à sec au milieu de la mer, et les eaux leur servaient de muraille à droite et à gauche.
30 A rana nan Ubangiji ya cece Isra’ila daga hannuwan Masarawa, Isra’ilawa kuwa suka ga gawawwakin Masarawa a bakin teku.
Ce jour-là, Yahvé sauva Israël de la main des Égyptiens, et Israël vit les Égyptiens morts au bord de la mer.
31 Sa’ad da Isra’ilawa suka ga iko mai girma da Ubangiji ya yi gāba da Masarawa, sai mutanen suka ji tsoron Ubangiji, suka amince da shi, da kuma bawansa Musa.
Israël vit la grande œuvre que Yahvé avait faite aux Égyptiens, et le peuple craignit Yahvé; et ils crurent en Yahvé et en son serviteur Moïse.